28/03/2020, 21:32 - Messages to this group are now secured with end-to-end encryption. Tap for more info. 03/09/2020, 10:52 - Anty saliha: *Asslamu Alaikum Wa Rahmatullah Wa BARAKATUHU.* 💕 *A dalilin yawan kira da neman tsoffin Littafaina da Masoyana keyi yasa na yanke shawarar kokartawa in rubuto muku su online don farin cikinku saboda dominku ake rubutun*💞 *Zamu fara da littafina mai suna RAHIMA saboda yawan tambayarsa da ake in Sha Allah. Littafin *RAHIMA* na *sayarwa ne*, don haka ga masu son karantawa za'ayi adding dinsu a group ne bayan sun biya *300* kacal ta daya daga cikin wadannan bankuna. A- *0598537268* GT Bank B- *6016142358* Keystone. Nagode. ....*RAHIMA*doc by Jami *ONE* Na *Saliha Abubakar Abdullahi Zaria* 1 *Bismillahir Rahmanir Raheem* Gaba daya yau cikin garin Kano an tashi cikin fatsakin rana ne duk da cewan an shiga watannin da ya kamata a rinka samun ruwan sama ko da yaushe. Al'amarin sai addu'a kenan domin wasu jihohin da kauyaku tuni sun sami ruwan sama, banda wannan ma sau da yawa hadari zai hadu a sararin samaniya tamkar ruwa zai sauko kafin kiftawar ido amma cikin hukuncin Allah sannu a hankali hadarin sai ya washe garin yayi haske , abu gwanin ban tsoro. A kalla a kan jera kwanaki ana hakan kafin Jalla sarkin sarauta Yai nasa hikimar a saukar da ruwan kamar da bakin kwarya, wani lokacin har a yini a kwana ana shekawa. Idan anyi dace da wannan baiwa, garin ya kanyi sanyi, duk inda mutum ya taka zai ji taushi da kamshin kasa wanda sansanyar iska ke yadawa ko'ina, alamun an samu ni'imar Allah kenan don zafi zai ragu matuka, daga nan kuma sai manoma su dukufa su koma gona, malamai da sauran jama'a kuwa mu ci gaba da adduar samun damina mai albarka don kasarmu ta Kara samun yalwar abinci da kyakkyawar ci gaba, Allah yasa mu dace, ameen. Duk da cewan ranar tayi yawa wacce ta haddasa zafin dake bugawa ta ko'ina bai hana jama'a bayin Allah zirga-zirga da kaiwa da komowar su wajen sana'oinsu ba, matan aure a gidajensu sun dukufa neman na kansu, halayen Kanawan Dabo dake burgeni kenan. Ba dai kaga suna zaman kashe wando ba mazansu da matansu, babba da yaro sun san hanyar da zasu maida taro sisi, sisi ya zama sule, sulen nan ya koma naira ba tareda girman Kai ko kyashin juna ba. A daya daga cikin wadannan gidajen dake unguwar Yakasai ne Hajiya Kaltume, dattijiya 'yar kimanin shekaru hamsin da biyar ke zaune cikin dakinta tana 'yan kulle-kullen kayan sana'arta, kamarsu kuka, kubewa busashahiya, maggi vedan da mai tauraro, tana sayarda omo, gishiri da suga, ga dakakken yaji da take masa hada-haden kayan kamshi, tafarnuwa dasu magi harda soyayyar gyada,kana ta durasu cikin robobi ko kwalabe tana saidawa. Sha biyu da rabi dai-dai babban danta Dr Haseeb yai sallama ya shigo gidan ya tarad da ita ta baje kayan a gabanta tana ta faman kulli, ganin haka ya kara tamke fuska ya murtuke babu alamun walwala ko kadan. Itama sanin halin likitan yasa ta daure nata fuskar, ko banza Dan fari ne,daman can ba sakin fuskar yake samu ba. Ya gaisheta ta amsa a ciki. Ya gyara zamansa tare da kurawa tafukan hannunsa idanu na 'yan dakikoki ya saki ajiyar zuciya. An ce tsakanin da da mahaifi sai Allah, ajiyar zuciyar da yayi yasa uwar ta dago Kai ta kallesa tace "Kai lafiya, wani abu na damunka ne?" Ya kada kau "Komi lafiya ba abinda ke damuna, sakon da kika bari a gida ne yasa na garzayo inji ko lafiya kike son ganina da hanzari?" Kafin ta bashi amsa Saida ta kulla kullin gishiru uku, hakan ya kara tunzura shi nan take ya kasa daurewa ya bara "Wai Hajiya don Allah me yasa kike son wahalar da kanki ne? Meye naki na zama kina wadannan kulle-kullen?" Ta kallesa ta kau da kai kana ta amsa " Tun shigowarka na lura ranka a bace yake, amma so nawa zan fada maka cewan ni rayuwata ta duniya iyayena basu yi min tarbiyyar zaman banza ba tunda kuruciyata, nasan muhimmancin dogaro da Kai ta hanyar neman na kaina, naga Kuma amfanin sana'a tun duniya na kwance kudin nada daraja ba yanzun da muke muna sana'a ba, muna buga-buga." 03/09/2020, 10:52 - Anty saliha: ....RAHIMA..doc by jami 3 Karfe biyar na wannan ranar yana kwance cikin dakin barcinsa, tunanin al'amarin 'yanuwansa kaf suka addabesa, ya juya can, ya juya nan.... Aka bude kofar dakin a hankali, ta shigo da dauke da cup data doro bisa faranti mai dauke da tatacciyar abarba ta tsaya gefensa ta mika masa, bai karba ba Saida ya tashi zaune, maimakon ya sha ya rinka karkada 'yan kololon kankarar da aka jefa cikin juice din don yai sanyi. Kafadarsa ta dafa tace "In tambayi Daktan wani abu?" Ya dago ya kalleta yana shafar goshinsa da yatsunsa biyu wanda alama ce ta nuni da yana cikin damuwa, ita tasan haka don ba banza kawai take takamar ta fahimci halin wannan murdadden mijin nata da suka kwashe shekaru shidda suna tare ba. Kafin ta bata amsa Saida ya kurbi juice din ya hadiye sannan Y Ya dago ya kalleta yace "Meye?" Ta amsa "Lafiya na ganka cikin wani yanayi tunda ka dawo?" "Ba wani abu ya bata amsa a taikaice kafin ya ci gaba batun auren Rabi'u ne ya taso, Ina ganin karshen watan nan za a daura auren ayi bukin kowa ya huta." Zuwaira ta bugi kirji "Wane Rabi'un, ba dai autan Hjy ba, karatunsa fa?" "Saurara! Ya fadi ba tareda kallonta ba, Hjy na ganin danta ya girma don haka gara ayi auren, idan da halin ci gaba da school to, but for now ayi auren dai... Ta so taji karin bayani daga bakin maigidan nata amma tsawon minti goma sha biyar ta fahimci iyakar abinda zata ji kenan daga bakinsa, taja jiki ta fita ta koma kicin. Karfe shidda kanninsa suka yi sallama gidan babban Yaya, ya fito falonsa suka zauna, Hayatu da Rabi'u suka zamo daga Kan kujeru domin su gaishe shi, ya amsa musu cikin fara'a har suka ji mamaki dalili da a zatonsu bom zai tashi! Ba bata lokaci ya fara magana "Ba wani abu yasa na nemeku ba sai don inji daga bakinka bayan na Hajiya dangane da batun aurenka." Rabi'u ya gyara zama ya fara kare kansa "Wallahi Yaya ban taba tsammanin abu ya zama haka ba, yes nasan mun fara sa mutunta juna tun shigowarta makarantarmu don shekara daya kacal na wuce ta, duk da ba course dinmu guda ba muna fahimtar fannin karatun junanmu da inda muka dosa. Da farko relationship dinmu tamkar yan uwa har a kan kiramu wa da kanwa, cikin ikon Allah myka shaku da juna fuye da zatonku, Kuma wallahi bamu taba furtawa juna batun soyayya ba sai watanni biyu da suka wuce har muke ganin zamu iya zama abokan rayuwa, sai dai ko da muka gasgata muka yanke shawarar bamu kawo batun aure kusa ba don gaskiya na fada mata sai na kare karatu ta amince saboda itama tana shaawar karatun sosai. Ashe muna namu ne Allah na nasa, kwatsam kakanta na wajen uba ya tada kayar baya cewa shi sam bai San da batun wani karatu ba aure ya sani, Kuma dole Rahima ta fidda miji ko yayi mata na dole. Ta taho ta zayyane min batun cikin tashin hankali da rashin sanin madafa, na tausaya mata kwarai, sannan naga ga alkawarin auren juna da muka shine naga ya dace dole inyi wanu abu a kai in taimaka ayi aurenmu in yaso ma ci gaba da karatun later." Hayatu ya daka masa harara "Kaji dan ka iya, watau ma har ka riga ka tsara yadda za'ayi, in hakane meye na neman shawarar ko yardarmu, ba ka shirya ba? Yaro da shegen rigiman tsiya, muna zamanmu lafiya ka tayar Mana zaune tsaye." Rabi'u ya gyada Kai "Kunji Yaya Hayatu da kayi naka wa ya hanaka ko shawara wa ka dauka, gashi nan saboda zara ka kasa zama da mace guda sai biyu duk sun hana maka sakat " Haseeb yai gyaran murya "Ni ban kiraku gardama ba, shawara na taraku muyi, Kai Hayatu hakuri za muyi ayi abinda ya dace, Hjy ma na goyin bayansa. Amma Kai Rabi'u Ina son kasan cewan wallahi ba da son raina za ayi auren nan ba, na amince ne gudun bacin ran mahaifiyarmu Kuma bamu san alkhairin dake ciki ba so karka damu ba zaka ji kunya ba in Allah yaso. Yanzun su waye ne iyayenta, wace unguwa take?" Baki yaki rufuwa saboda murna, Hayatu ya kallesa ya bushe da dariya yace "Ka daina wani murna in har munji bata da usuli batun aure ya tashi ehe, uhhmmm Kai muke saurare: 03/09/2020, 10:52 - Anty saliha: ...RAHIMA..doc by Jami 2 Dr Haseeb yai murmushi bayan jin kalaman tsohuwarsa yace "Tuni na amince da batunki Hajiya shiyasa na sayo miki wadannan kayan masarufin yadda kika bukata bisa yarjejeniyar aunarwa za ki rinka yi ba ki zauna kina irin wahalar nan ba." Itama tayi 'yar dariya " Ina wahala a nan? Ku fa likitoci kuka ce mutum ya rinka motsa jininsa, Kuma idan kace sai tiya ko mudu zan rinka sayarwa kenan sana'ar tawa bata talaka ba ce, in kuwa hakane to ci gabanmu ragagge ne domin talaka shine jigon kowacce irin sana'a, ni don Allah ka bar wannan zancen, Kai kenan kullum kazo gidannan da sabon tsirkun da zaka kirkiro alhali ni din nan ban gaza ba da sauran karfina, to Wai ma Ina wahalar take? Mai aiki fa ka ajiye min musamman babu abinda ni keyi kullum sai dai in wanke goma in tsoma biyar, inci mai kyau, insha mai kyau, in daura zanin da wata yarinyar macen bata daura na, inyi barci na ya isheni, in bautawa Ubangijina gwargwadon karfina, bani da sauran buri a duniya da ya wuce illa inga auren Dan autana, baya ga shi sai rokon cikawa da imani. Haba wace wahala, lokacin da akayi ta can da anyi yanzun kuwa albrkacinku sai godiyar Allah da fatar Allah ya baku masu yi muku fiye da yadda kuke yi mana." Ya amsa "Ameen Hajiya, shikenan ba zan kara magana kan hidimar sana'arki ba Allah ya bada sa'a, amma don Allah ki rinka samun isashshen hutu, bayan haka nace ki tambayeni duk abinda kike so cikin ikon Allah ba zai gagara ba." Hjy. Kaltume ta tattara kayan gabanta ta ture gefe tace "Bari dai in tsaya muyi maganar nan sosai don na fahimci hira kake ji yau, shin me yasa kake son maida hannun agogo baya ne? Na fada maka Kai kadai, na gaya maka tare da 'yanuwanka, yau ma zan Kara fada maka ni ban raina hidimar da kake min ba, iyaka nafi amincewa da in nemi nawa na kaina, ba sai na jiraka ba balle 'yanuwanka da basu da hali. Ranar da Allah ya hore maka kayi inyi murna da farin ciki, ranar da baka dashi sai inyi amfani da nawan da kuke rainawa, kaga na rufawa kaina asiri na rufa muku, banda wannan yau da gobe bata bar komi ba, koda nike mahaifiyarku ba lale Allah ya tara min duk masu jin kaina ba, idan Kuma har na samu hakan nasan irin matan da zaku auro? Wata matar ita ke hana da ya kula da iyayensa yadda ya kamata duk da ni alhamdulillah matanku na kwatanta min da'a. To idan duk muka ture wannan batun, ka duba kaga kaine babba, Allah bai ba 'yanuwanka rufin asiri irin naka ba, kai kake dawainiya dani, kayi dasu da dangina, ka taimaki dangin mahaifinka, Ina tausaya maka kwarai da gaske don ka zama hannu guda ba wani mai tallafa maka, ga iyali ka fara tarawa dole in rinka taimakonka, misali ko haihuwa matarka tayi na baka gudumuwar zanin goyo ban taimaka maka ba?" Dole yayi murmushin da har kyawawan hakoransa suka bayyana yace "Wallahi Hjy kin ban dariya, amma insha Allah ba zan sake shishishigi cikin hidimominki ba, Allah Kuma ya kara taimakawa." "Yauwa yanzun naji batu, to tunda naga ka saki ranka yanzun sai muyi maganar dalilin nemanka." Ya amsa "Ina saurarenki, Allah yasa lafiya." " Lafiya kalau, batun kaninka Rabi'u ne, kasan na fara yi maka bayanin neman auren da ta fara kwanaki ko? To shine jiya ya taho min da maganar cewan wai iyayen yarinyar sunce inda gaske yake ya fito." Haseeb yai kasake na wani lokaci kafin ya furta "Har yanzun yana nan yana shirmen nasa kenan?" Tace "Wane irin shirme Kuma, yaro na neman raya sunnar manzo?" "Hmmmm hjy Rabi'un guda nawa yake ne? Ni fa karatu na turasa makaranta yayi ba soyayya ba, don Allah Ina zai kai mata yanzun?" "Ban gane ina zai kai mata ba, bai isa auren bane ko yaya?" Ko kuwa don ka turashi karatu sai yaki aure, maza da mata nawa ke yin auren su ci gaba da karatun nasu?" Ya kada Kai "Kwarai ana yi amma ga Wanda ya shirya, yana da muhallin da zai aje matar yanada kamu sayar domin ciyar da ita da daukar sauran lalurorin yau da kullum na shi kansa da ita matar da ya aje. Rabi'u karatu yake Hajiya, duka -duka 200 level yake a jami'a, me zai hana ya hakura ya kare sauran shekara dayan, ya samu abinyi kafin muyi wani batun aure?" Ta fara harzuka "Da yawan yajin aikin da ake yi a jami'oi ne zai gama karatun nan da shekara gudan? To naji, yanzun ya kake son ayi da iyayen yarinyar, me zamu ce dasu?" Ya amsa "Ace musu bai shirya ba sai ya gama karatunsa tukunna." Tace "To ita Kuma yarinyar da aka ce za a aurar da ita yanzun ne fa?" Ya bata amsa da "Ta nemi wani ta aura tunda iyayenta sun matsu su aurar da ita, shi Kuma Allah ya bashi wata nan gaba idan lokacin auren nasa yayi." Ta fusata "Na fahimci ka shiryawa kowacce tambaya zanyi maka, kawai ka fito fili kace ba zaka taimakawa danuwanka hidimar aurensa ba fakat." Ya Kara ladabtar da kansa "Ko kusa ba haka bane Ni a ko yaushe shirye nike in yiwa 'yanuwana kowanne irin taimako suka bukata daga gareni. Ba wai baba son Rabi'u yai aure bane, tunanina mene na gaugawa,hanzari ba nasa bane, ya bi a hankali mana har Allah ya bashi daidai shi." Hjy Kaltu ta juya masa baya "Kai kake da lokacin surutu, da kake gaya min wannan zancen wofin kaninka da kuke uba daya nawa suka yi aure? Gaba dayansu babu Wanda ya haura shekaru ashirin a cikinsu, me yasa baka hanasu ba, wane irin gudumuwa ce baka basu ba, sai yanzun yaro ya Kai shekaru da biyar a duniya ya isa aure kace zaka tauye masa hakkinsa?" Yace Yi hakuri ban tari numfashinki ba, wadanda kike magana na amince musu ne saboda kowannansu nada shago a kasuwa, sunada abinyi,tunda sun nuna su kasuwancin suke so fiye da karatun, na tabbatar Kuma zasu iya daukar takalihun matansu, amma Kya hada da wannan ahi ba karatun ba, shi ba aiki ko wata katamammiyar sana'a ba? Idan Kuma kina ganin banyi magana Kan auren su Hamisu ba na Hayatu shima na hana shi ai amma shima don rashin sanin ciwon Kai matar shekararta biyu ya sake auro wata, gasu nan banda tashin hankali me suke yi?" Ta juyo a fusace "Ka rufa min bakinka kaji, ai fa tunda ba Kai ya shafa ba yanzun zaka rinka kawo min kabli da ba'di, to shima da ya auri mata biyun ai ance matar mutum kabarinsa da yaje yana neman na banza a waje ai gara ya tara cikin gidansa. Kai wai ya za ayi daman ra'ayin rikau dinka ya zama irin na kowa? Naji ta bakinka, tashi jeka, kaga kyaun sana'ar da kake mita, ni zan tsaya, Allah kuma zai taimakemu ayi wannan auren da yardar Allah autana ba zai kunyata ba, idan ba zaka jagoranci harkar auren ba ai ba Kai kadai bane, kaninka na Nan, Allah dai na gani na baka hakkinka na kasancewa babba." Da ya tabbatar da al'amarin yai nisa gashi bai son bacin ranta ko kadan har dai in ya tuna can inda aka fito da can dole ya fara lallashi yana bata hakuri yace "Tunda abin ya zama haka ba komi Hajiya, daman ni naso ace ya kara sanin ciwon kansa ne yasan wahalar ya nemi na sa yadda idan yai auren zai fi rike matar da daraja da mutunci amma tunda an matsa insha Allahu ba damuwa za ayi yadda kika ce cikin yardar Allah. Zan nemi Hayatu mu tafi gidan iyayen yarinyar cikin satin nan in yaso duk yadda muka yi dasu Kya ji, anjima ki turo min Rabi'un yai min bayanin unguwar, Allah yasa mana hannu." Dadi ya rufeta cikin murna tace "Insha Allah yau dinnan zaka ganshi yana dawowa gida zan turo maka shi, Allah yai maka albarka." "Ameen nagode, idan babu wani abu Ina son komawa asibiti amma shi Rabi'un ya sameni a gida." Ya ciro kudi cikin aljihunsa ya ajiye a gabanta bisa tabarma, ya mike kana yai mata sallama ya fita tana sanya masa albarka. 03/09/2020, 10:52 - Anty saliha: ...RAHIMA..doc by jami 4 Rabi'u yace "Yaya Haseeb, Rahima da iyayenta 'yan usulin jihar nan ne, gidansu na unguwar rijiyar lemu, muna iya kiranta marainiya don ta rasa mahaifiyata tun lokacin haihuwarta. Bayan Allah ya amshi ran mahaifiyarta ne kanwar uwar dake shayar da nata jaririyar 'yar kimanin watanni uku ta dauketa taci gaba da shayar dasu gaba daya. Kasancewa mahaifinta daman matansa biyu sai abin yazo masa da sauki domin ta samu saukin maraicin diyarsa da aka mutu aka barin masa, ko sa yake ita ce diya kwara daya tilo da mahaifiyarta ta bari su bakwai ne cif wajen mahaifinsu, sunan mahaifiyar nata aka mayar mata don tunawa da marigayiyar. Sunan mahaifinta Aliyu ana kiransa Ali mai goro, data girma ta isa shiga makaranta saita shiga da suna Rahima Mamman Mai yadi, sunanta marikinta kenan, kowa dai ya san Mamman Mai yadi na Yakasai, tsakanin gidansa dana Hajiya bai wuce loko biyar zuwa shidda ba, bayan wannan Rahima yarinya ce mai hankali da zurfin tunani Ya Haseeb. Hayatu ya kallesa "To ai ka bari har mu bincika muji wa kunuwanmu tukunna kana mu zartas da hukunci, Kai daman ya za ayi ka Fadi wasu aibunta tunda kana sonta." Rabi'u yace "Balle ma bata dasu, yarinya ce mai da'a wace ta samu dimbin kyawawan tarbiyya nagari Kuma nagartacce." A nan dole Haseeb yai murmushin da bai shirya ba yace "A nan kan Ina bayan Hayatu Rabi'u, idan har mun bincika mun tabbatar da yarinyar da halayen daka fadi babu shakka kayi sa'ar Mata, idan kuma munji sabanin haka sai dai kayi hakuri. Yanzun sai ku koma gida, idan Allah ya kaimu gobe zanyi abinda ya dace sai kaje kaci gaba da adduar Allah ya tabbatar mana da alkhairi. Duk yadda muka yi goben za kuji insha Allah." Sunyi sallama cikin farin cika da murna. Kamar yadda ya dauki alkawari, ya binciko dukkan abubuwan da suka dace ya sani ya Kuma ji ta gamsu saboda aure tsakanin Rabi'u da Rahima tabbas ba makawa. Baiyi sanya a gwiwa ba nan da Nan ya nemi Baffansu Rabi'u da kanin Hajiyarsul watau kawunsu yai musu bayanin halinda ake ciki. Suma basu bata lokaci ba suka amince, suka hadu su hudu suka nufi gidan Mamman Mai yadi a matsayin mabidan auren wa dansu diyarsa. Ba wai ta fannin saye da sayar da yadiddika kadau yasa sunan Alh. Mamman yayi fice ba, ah ah duk wani Mai hulda dashi ta cinikayya ko harkokin yau da kullum ya shaidi mutym ne Mai son jama'a da mutunta su, ya iya hulda da mutane kwarai da gaske. Ta fannin iyalinsa kuwa matarsa uwar 'ya'yansa Habiba ita kadai ya mallaka, tunda ya aureta suke zaune lafiya, zaman so da kauna da mutunta juna sai bai taba sha'awa ko tunanin karo wata matar ba, gashu sun hayayyafa, Allah ya azurtasu da diya takwas, biyar maza uku mata. A zahiri diyanta bakwai ne amma tunda matarsa ta amshi marainiya Rahima ta shayar da ita yarinyar ta shiga zuciyarsa, yaji yana tsananin sonta, irin son da da mahaifi har bai son yaji wasu su furta bashi ya haifeta ba, itama kanta Rahimar Saida tayi wayo ta fara sanin ciwon kanta ne ta fahimci cewan ba sune mahaifanta ba, ta Kara tabbatar da hakan yanzun da aka ce mahaifinta na wajen Uba ne yai ruwa sa tsaki wajen hanata ci gaba da karatunta. Hausawa kance wani ma yai rawa ballantana dan makadi, su Alh. Mamman kan shiga su fita suyi wakilcin aurarraki da dama har sau sunga an kulla sunnar Manzon Allah SAW suke numfasawa to Ina ga Kuma ana batun auren diyarsu aka zi yi, 'yar lelensa wace yake ji da ita? 'Yanuwan Rabiu da sukayi tattaki zuwa wajen neman auren sunsha mamakin irin karamcin da akayi musu bayan an karbesu hannu bibbiyu. Sun rabu kan cewan an basu yarinya saura batun sa ranar daurin aure sai abinda 'Yanuwa suka tattauna zasu nemi dangin angon. Mutunta su day aka yi ya karawa Hasseb kwarin gwiwar aiwatar da abubuwan da suka kamata dangane da auren. Kudi ya ware masu yawan gaske ya baiwa matarsa ta hado kayan lefe setin akwatuna uku dankare da tufafi, kayan shafa, jakunna, takalma da sauran tarkacen da ake hadawa budurwar data hadu Kuma ta dace da Mai yin. Shi kansa Rabi'u akwati guda ya cika masa da tsadaddun shaddodi na shigar angonci kana ya samar masa Dan madaidaicin gidan da zasu zauna amma mahaifiyarsu taki amincewa da hakan, tace tafi son ta zauna tare dasu tunda daga amaryar har angon yarane suna bukatar zama kusa da manya domin tsawartawa lokaci-lokaci. Dalilin haka yasa Haseeb ya gyarawa kanin nasa dakuna biyu dake saman bene, kicin da toilet a gidan Hajiyar tareda Kara yiwa nata bangaren kwaskwarima duk da ko can ko ina a gyaren yake. Lokacin da Alh Mamman Mai yadi ya tafi gidan aininhin mahaifin Rahima batun auren bayan ya sanar dashi ko su waye maneman, Mal Ali Mai goro ya nuna masa halacci, din kekasa kasa yayi yaki amincewa ayi maganar dashu ya kare da fadin "Wannan yarinya diyarka ce Alh. halak makak, kana da damar aurar da ita ga duk Wanda ka so, mene nawa a cikin wannan zancen? Babu ruwana, Kuma don Allah duk abinda ya taso karka sake tuntubata, kaida uwarta kun isa ku zartas da hukunci." Tunda Rahima ta dawo hannunsa sanin kansa ne mahaifinta bai taba nuna masa ba shine ubanta ba, yana yi masa kawaici fiye da yadda ake zato, Yana jin dadin haka, sai dai halaccin da ya nuna masa yau ya tabbatar da Alh. Ali ya cika dattijon da yasan yakamata yasan ciwon kansa. Dadi ya rufesa, zuciyarsa ta Kara zurfafa da kaunar diyar tasa bai san lokacin da ya fara zuba godiya ba... Alh Ali yace "Ni ke da godiya Alhaji, a yau da zamani ya canza harka sami Mai rike maka d'a tsakani da Allah, ba cuta ba cutarwa, ba wata tsangwama balle banbanci ai sai mutum ya godewa Allah, ya rinka wansa yai masa namijin kokarin nan addua, wallahi ni nakan rasa irun godiyar da zanyi maka ma, Allah dai ya saka da khairan yasa diyan suji kanmu." Alh. Mamman yace "Ameen Nima nagode, zamu je mu Kara tattauna batun sa ranar buki da uwarta tunda naga dangin yaron tuni sun shirya." Mal Aliyu yace "Ba laifi Allah ya sanya alkhairi yasa za ayi damu, insha Allahu Nima goben ko jibi Zan tafi Gumel in shaidawa tsohonmu halinda ake ciki, kasan tun fil azal shi ta tayar da rikicin Nan." Alh Mamman yace "To ya za ayi, duk inda tsoho yake sai lallabawa da lallashi har Allah yasa a rabu lafiya, Ni da nawa tsoffin suka dade da rasuwa har shaawar irinku Nike, yawanci wadanda suka manyanta da iyayensu sai kaga suna musu yadda suka ga dama ko su rinka cewa rigimarsu ta ishesu." Mal Ali ya nisa "Wani abin da muke ganin rigima ce sai kaga sunada dalilin aikatawa, yanzun shi wannan wa yasan dalilin kafewarsa Kan lalle sai a fiddata makaranta ayi Mata aure? Mu dai har kullum albarkarsu muke nema dole mu bi son zuciyarsu don mu gama lafiya." Alh. Mamman tace "Hakkun, maganarka dutse, Nima Zan shirya in bika mu tafi in Kai masa goro da hannuna in shaida masa diyata ta samu miji yaro danye sharaf ba irinsa ba." 'Yan dattijan suka bushe da dariya kana suka yi sallama cike da murna. 03/09/2020, 10:52 - Anty saliha: *Afwaan jama'a ga number da zaku turo shaidar payment ayi adding dinku.* *080 34243456* ....ˆRAHIMA...doc by Jami 5 Habiba ta shiga goda tana rafka sallama tun daga sori amma babu wadda taji har saida ta iso daf da kofar daki. Dukkansu 'yanmatan biyu suka amsa salkamar tare da fadin "Lah Umma yaushe kika shigo?" Rahima tayi saurin amsar jakar dake hannunta tace "Duk laifin Maryam ce, ta kuntuke da surutu ba wakafi ba aya, balle alamun motsin rai." Maryam ta zaburo "Amma da alamar motsin tambayar da baki bani amsa ba ko?" Habiba ta cire hijab tana fadin "Anyi babbar kwabo, ke kenan ki tasa kanwarki gaba kiyi ta tsatstsagarta?" Cikin shagwaba Rahima tace "Tunda kika fita gidan ta bude faifaina dana Rabiu har kaina na ciwo." Habiba ta jayo kujera ta zauna kafin tace "Bata ko jin kunya, wannan yaushe zaice dake wata Yaya?" Rahima tayi mata gwalo ba tareda uwar ta gani ba tace "Nima haka Nike fada mata tuni." Maryam ta Kai Mata bugu cikin wasa "Ni na rasa irin girman da ake son dora min ba gaira ba dalili alhalin watanni uku kacal fa na bata." Habiba tace "Sai girman jikin ba, kowa ya hanku zaiyi zaton shekaru uku kika bata ko Ina Zaki Kai wannan jikin oho." Rahima ta sake fakar idon Ummar tasu tayi mata gwalo kana tace "Aure Umma za ayi mata, yanzun nan take fada min wai Abbas ya matsa mata da zancen aure." Maryam ta kara zaburowa "Allah Rahima ki kiyayeni, Umma karya take min." Habiba tasha mur ta kallesu "Eh ba shakka, tabbas Kun cika yan zamani, kiri-kiri Kun zauna batun aurenku kuke ba kunya ba wani shakka, Allah ya shirya Mana,wannan zamanin sai shiru. To ni ince ko Kun dora min sanwa ko kuna can kuna hirar samari?" "Tun dazun muka Dora Umma." Suka bata amsa tare sannan suka nufi kicin din domin duba girkin, ta bisu da kallo, cikin zuciyarta ta ce inda da gaske shi Abbas din ya shirya ai da an hada bukin ayi rana daya mu huta. Maigidan ya dawo ya shigo dauke da ledojin kayan lashe-lashe da yakan sayowa yara, su Rahima suka fito da hanzari suka durkusa "Sannu da dawowa Baffa." Ya amsa Yana Mai farin cikin ganinsu yace "Ina kannin naku ne banji motsin kowa ba." Maryam ta amsa "Wallahi Baffa suna can sama suna kallo ba suji muryarka bane da tuni sun sauko." "Bari na kirasu." Cewar Rahima. Ta hau a guje ta shiga ta kashe Tv din tace Sarakunan kallo to Bafda ya dawo yana nemanku idan kunga damar sauka.". Har da zasu tsaya korafin an hanasu kallo sai suka jiyo muryarsa, sanin lalle da abin lasawan da yake tahowa gida dasu yasa suka rugo kasa suba fadin "Baffa oyo yyo me ka sayo Mana " Maryam ce ta bude ledan ta shuga rarraba musu youghurt da biscuits, Rahima Kuma ta bude ledan nama ra busde ta rabawa kowa nasa, kafin ta mikawa Maryam tasa hannu cikin na Samunu ta diba yanka biyu ta saka a Baki, yaro ya saka kuka, Rahima ta kalleta "Kash Maryam meye haka?" Umma ta harareta "Zalunci mana, ba Kya tsaya a baki naki ba gandoki?" Ta saki dariya "Wallahi miyauna ne ya tsunke Umma.". Rahima ta ce "Ai nasan maganinta, ta kasa rabin Maryam din biyu ta mikawa kaninsu, Maryam ta taso tace ba zata sabu ba bindiga a ruwa ta juyo zata amshe na Rahimar, ta gudu daki, ta bita Yana dariya. Iyayen suka bisu da kallo cike da sha'awa da tausayin su. Alh Mamman yai ajiyar zuciya ya numfasa bayan yasha ruwan da Umma ta kawo masa tare da abinci, Ya kalleta cike da kauna yace "Kinsan abinda ke damuna?" Ta kada Kai "Sai ka Fadi Alhaji." Ya gyara murya "Ina jimamin yadda yaran nan zasu rabu da juna ne, sauran kwanaki tara kacal fa bukin Rahima, ya 'yaruwata zata ji?" Tace "Hhmmm kace ya za ayi da kewar juna dai, Ni kuwa nafi tausayin Rahima na rasa dalili." Yace "Ai kinsan maraya da shiga zucci dole ki rinka tuno 'yaruwarki yanzun musamman da auren nan ya kawo jiki saukinmu idan Allah ya turowa Maryak nata mijin tayi auren sai hankalunmu yafi kwanciya. Habiba tace " Da fa masoyinta Alhaji ita taki bashi damar ya fito dama ya riga mijin Rahima magana." "Ahaf ai ban sani ba da an tuntubesa aji in ya shirya a hada auren 'yan tagwayen naki mu huta.". "Ka shirya auren 'yan mata biyu lokaci daya a wannan zamanin namu?" Ya amsa "Yo me zai gagara? Nufa duk shigi da ficin kasuwancin da nike yi dominku ne, rufin asiri alhamdulillah don Allah ke yiwa bawansa, idan har batun auren Maryam ya tabbata naji nata masoyin ya shirya to ba shakka tare za a hadasu ayi sha'anin insha Allahu, a shirye nike, Allah zai rufa mana asiri." "Kamar inyi guda Alhaji saboda jin dadin maganarka, Allah ya Kara budi ya karemu daga sharrin makiya.". Ya amsa "Ameen bari in dan kwanta in huta kafin a Kira sallah." 03/09/2020, 10:52 - Anty saliha: *A turo shaidar biyan bank ta wannan Number 08034243456, Nagode* ....RAHIMA..doc by jami 6 A dakin 'yan matan Rahima ce kwance bisa doguwar kujera ita Kuma Maryam na kishingide gefen katifarsu rike da wani littafi mai suna *Tun Ran gini ran zane* Rahimar nata magana Maryam bata kulata har ta gaji ta fisge littafin tace "Wane irin wulakanci ina magana kamar ba dake nike ba?" Ta juyo "Sai hakuri 'Yaruwa na tsunduma, kinsan yadda karatun littafan nan suke, idan kina yi sai mutum ya rinka ganin abin a zahiri, Kinga Sa'adatun nan ji nike inda nice ita ba zan wulakanta Sagir ba tunda Ina sonsa." "Maryam sarakunan soyayya inji Rahima, kinsan nayi kokarin kwatanta irin soyayyan abu yaci tura, wallahi ban san yadda ake yinta ba." Maryam ta tashi zaune tace "Rahima batun naki nayi ne, soyayyar dake tsakaninku da Rabiun fa?" Ta saki 'yar ajiyar zuciya "In gaskiyar kike so, ban taba jin faduwar gaba don na gansa ba balle ma ace na kidime na rasa sukuni sabida rashin ganinsa, that's why nike ganin kamar hauka kawai kuke keda Abbas, infact zakewarku tayi yawa." Maryam ta gyara zama "Babu zakewa a sha'anin soyayyarmu, bari inyi Miki misali donki fahimce Ni, kin karanta littafan Aunty Saliha ai, tun daga kan *Wani jinkiri, Zumuncin Zamani da Son Zuciya da wannan din nan, ko yaushe ina kwatanta soyayyarmu tamkar nasu Faruk da Surayya ne har nike ganin haka rayuwar aurenmu zata kasance domin ni din nan na karantu na dau darussa da dama cikin littafan, yadda nike ji daahi hakan yake ji dani, meye aibun mu?" Rahima tace "Ban ce akwai aibu ba fa ina Miki bayanin duk shakuwar da mukayi da Rabi'u ban taba jin kwatankwacin abubuwan da taurarin littafan Aunty Salihar ke ji ba dangne da mazajen da Allah ya hadasu ba, shine nike tuhumar anya na san so dinma kuwa ko kuwa in tambayeki shin menene so dinnan ne?" Ta tafa hannu "Allah ya kawo mu, Rahima baki san so ba, duk zancen Rabiun da kike kururuwar iblis ne?" Ta bude ido ta lumshe tace "Ba shakka da na dauka kyakkyawar hulda da shakuwa irinta abota da mukayi da Rabi'u shine shine son da ake fadi, Saida na yawaita karantun littafan nan naga yadda kuke tafiyar da al'amarin naku soyayyar dole na fara doubting, anya are we right for each other?" Maryam ta kyalkyace da dariya "Is too late to be having second thought." Ta buga kirji "Ina! Ba abinda zuciyata ke nufi ba kenan ba, na riga na amince da Rabiu dari bisa dari zan Kuma aureshi insha Allah, duk da cewan bashi cikin tsarin mazajen dana yiwa kaina sha'awar aure amma ya na iya da ikon Allah." Taja tsuki "Tun farko na rasa dalilin amince masa." "To da in auri wanda ban sani ba gara wanda muka saba, muka san juna, and with time zan kaunace sa " Maryam tayi shiru kafin tace "Nasan halinki Rahima kusan ince fiye da zatonki, tun tasowarmu Ina lura dake da dabioinki, ke mace ce miskila, hakan ya haifar miki da rashin son kula kowa sai lokacin da kika bushi iska da kanki, sau nawa samaru ke approaching dinki su kyale ki dole saboda rashin samun fuska daga gareki, da yawansu sunyi min complain, suna sonki amma kinki kulasu har muka kare secondary baki da saurayi, da muka shiga B.U.K ma batun gudane baki canza ba. Na dade ina mamakin yadda kuka lakewa juna keda Rabiun naki, don naga ko wanne namiji bai isheki kallo ba. Shin kinsan Umma ta taba tsareni kan batunki har cewa tayi tana tsoron ko kina tareda wani bakin aljani ne mai saki gudun maza? Don in kwantar mata da hankali ba shiri na bata labarin Rabiu duk da nasan babu alakar soyayya cikin zuciyarki game dashi, mind you ban san abinda ke nasa zuciyar ba." Cikin tausayin Ummar tasu Rahima tace "Allah satki Ummana, ni kaina wallahi na fara jin tsoron kaina tun bai dameni ba na fara damuwar tunda mace nike Maryam Kuma inada masoyan nan amma ko kusa har zuwa yau dinnan banji Ina son wani ba, infact sai ji nike na tsani duk namijin da zai bude baki yace yana sona." Maryam ta bude baki "Naso in fahimci hakan amma banyi tsammanin yai nisa haka ba to ko dai gaskiyar Umma ne a fada mata ta tashi tsaye?" Tayi saurin fadin "Ko kusa ba zan tayar mata da hankali ba ai ina addua gashi Kuma Allah ya amsa tunda ya hadani da Rabi'u kuma har cikin zuciyata na amince dashi matsayin mijina, zanci gaba kuma da adduoin, na sani ko nan gaba soyayyar da za muyi a rayuwarmu ta zarce nasu Surayyar, Kausar, Laila da Saadatun da kike magana?" Tayi shewa "Abin nayi ne, Allah ya rayamu inga wannan ranar, ni kuwa dana aikawa Aunty Saliha suga yadda mai gudun maza ta shiga cikin kogin soyayya mai wuyar fitar." Rahima tace "Ni har kin tuna min tambayata baki ban amsa ba, shin meye so?" Ta daga mata hannu "Ina! You're an amateur in love ba zaki fahimci komi ba saboda baki dandani Zaki, daci da sauran abubuwan data kunsa ba, amma nayi miki alkawarin duk ranar da Allah ya dasa miki wannan baiwa a zuciyarki, kika tsunduma ciki sosai, zan baki amsar, ke dai roki Allah idan zai zo ya taho da sauki don irinku ne masu zakewa kuga tamkar kowa bai iya ba sai ku." Rahima ta daga hannayenta sama "Ya Allah ka dasa min so cikin zuciyata." Maryam tace "Ubangiji ya amsa don alkawari yayi babu bawansa da zai daga hannu sama ya rokesa face ya biya masa bukatarsa, sai mu jira lokaci da saukar ijabarsa, kin gani zan shiga wanka, Abbas zai taho anjima." 03/09/2020, 13:41 - Anty saliha: ...ˆRAHIMA..doc by Jami 7 Rabi'u Yakasai ya gama shirinsa tsaf, yau shigar doguwar riga yayi dinkin tazarce ta yadin shadda mai ruwan kasa-kasa, taji guga sai sheki take yi, ya kwafa hula kube kalar kayan, ya feshe jikinsa da sauran turaren da Ya Haseeb ya kawo masa tsaraba wata tafiya da yayi, kamshi ya bude cikin dakinsa dake soron gidansu, ya saka takalmansa cover wadanda tun la'asar ya baiwa shoe shiner kwangilar gugarsu, ya fito ya maida kofarsa ya rufe ya shiga cikin gida wajen Hajiyarsu. Tana ganinsa ta washe baki tace "Dan auta kenan wannan irin shiga hala wajen diyata zaka?" Cikin kunya ya durkusa ya gaisheta da yini kana ya amsa "Eh wajen Rahima zani mu karike shirye-shirye, Ya Haseeb yace in kai masa kiyasin abubuwan da suka rage ya bani yasan ya gama da hidimar." Hajiya tace "Gaskiyane, an gode masa Allah ya Kara budi, kaima ince ko kana yi masa adduar?" Yace "Duk rana ta Lillahi Hjy, tsakaninmu dashi adduar ce kadai abinyu don ko godiya nayi masa sai yaita fada." Tace karka fasa don nasan yana jin dadi, tashi ka tafi Kar dare yayi kace Ina gaisheta." Har ya mike ta tsayar dashi ta bude wata Jakarta ta fiddo sabbin kudi ta mika masa bandur na dubu biyu 'yan naira ishirin tace "Amshi ka Kai mata." Yasa hannu ya karba Yana tambayar "Ina kika sami sabbin kudi haka?". "Sai kaji inda suka fito? To kyautar Yayanku ne ya bani Ni Kuma na ajiye maka." Rabi'u yai tsaye shiru.." Kinga Hajiya ko kusa bai dace ba, ya zai miki alkhairi don ki amfana sai ki bani, gaskiya ba zaiji dadi ba." Ta hararesa "Kai zaka tafi ka fada masa ko wane, to idan ma baka karba ba Hayatu ya taho ya amsa tunda shi kullum cikin neman karin na cefane yake." Ya maidasu a aljihu yace "Ah ah Ina so Hajiya, Allah ya saka miki da aljanna madawamiyya." Ta amsa "Ameen Auta, hanzarta ka gani, sai ka dawo." Ya fito har zai hau babur dinsa sai shaawar takawa a kasa yazo masa, ya fasa ya bi titi yana takawa daidai, irin tafiyar yaro matashi Mai jini a jika. A cikin gidansu Rahima tuni ta dade da kimtsawa tana jiran Rabiun, a yau shigar wando da riga suka yi ita da Maryam 'yan Pakistan tsarabar Umrah ne da Baffansu ya kawo musu, duk kalarsu guda watau ruwan hoda da zanen kalar gwaiduwar kwai a jikinsa, banbancinsu kawai na Maryam yafi nata girma tunda ta fita girman jiki. Ita Rahima yarinyace gajera, baka mai dan jiki, ba kyakkyawa ba ce ba Kuma za a kirata mummuna ba, Maryam ta fita kyaun fuska nesa ba kusa ba, ita kuwa halittar jiki Ubangiji ya kyautatata mata. Tana da kyaun siga kwarai da gaske, kirar jikin matan Nan da ake Kira masu kirat kwalbar coca-cola. Duk da ita ba Mai kiba bace Allah yai mata halittar wasu guraye murde a wuyanta, layi-layi uku. So da dama akan kirata mai karuwar jiki kasancewar kowanne irin sutura ta saka su kanyi mata kyau suyi ras a jikinta tamkar dominta aka yi. Bayan wannan ba kowa ke yarda idan an fada masa shekarunta sun kai ashirin ba saboda jikin da fuskar basu nunawa. Sanin yadda sutura ke amsar jikinta suna fito Mata da shape yasa babu yadda za ayi mutum ya ganta ba tare da after dress ba, ga addini ya ratsata sosai domin Alh. Mamman ba daga baya ba wajen kyautata tarbiyyatr yayansa. Alhamdulillah su Rahima sun gogu da addini sun san hanyayoyin tafiyar da harkokinsu ta yau da kullum musamman tsarin addinin islama, tsakar gidansu kadai mutum zai shiga yaga kalar tufafin da ta saka saboda tsananin bin dokar Ubangiji. Cikin wannan shiga ta kamala ta fito ciiin natsuwa da kamun Kai ta tarbi maigida to be da harkarta yadda suka saba yiwa juna, suka gaisa a mutunce. Rabi'u ya isar Mata da sakon Hjajiya. Rahima ta amsa da "Kasan kuwa da kace Hajiya na gaisheni wani irin dadi kan rufe ni, ni shar kenan don wannan alama ce ta dace da sarakuwar kwarai." Ya gyara hularsa cikon jin dadi "In don Hajiya Kar kiji komi, ta yaba dake fiye da zatona, ke ko matan Ya Hayatu da suke kullum cikin bala'i bata kyamace su ba, ba abinda ke tsakaninsu sai kyautatawa." Rahima tace "Ta hutawa zuciyarta da masifa, daman har addua nike Kar Allah ya hadani da muguwar sarakuwa mai sa ido da kasa kunni a harkar matan danta don in kaji labarin masifar wata tsohuwar sai auren ya fita ran mutum gaba daya." Yayi dariya "Banyi tsammanin Hajiya zata kula matar Ya Hasseb ba balle na Ya Hayatu koda ace gida daya suke zaunre balle Allah ya raba zaman, Ya Hasseb na Galadanci, Ya Hayatu na Gwammaja ita tana Yakasai, bata zuwa gidan kowannansu balle ta gano abinda zai tayar Mata da hankali, sune dai duk sati suke Kai matansu su gaisheta, mu kuwa saboda kaunar da take miki ne yasa tace da ita zamu zauna." Tace "Lalle Dan lelen Hajiya, wai Rabiu daman kana da sauran turaren nan ka daina fesawa na daina jin kamshinsa." Ya kyalkyace da daruys "Kinsan na gaya miki nima fa Ya Haseeb ya bani, da naga ya kusa karewa ne na boye, ban san kina son shi ba dana kawo miki tuni amma zan adana miki sauran in kinzo in baki." Tace iye dan gatan Ya... Haka kawai ta tsinci kanta da jin nauyin Yayan Rabiun ta kasa fadin sunansa duk da bata taba ganinsa ba. . Ya girgiza Kai "Ba zaki ma tabbatar da hakan ba Saida batun aurenmu ya taso, gaskiya Ya Haseeb ya cika danuwa kaunar zumunci da taimakon zumunta kamar yadda Allah yai mana horo muyi. Gaskiya kullum Ina jinjina masa, yana kaunata, yana ji dani matuka, nima bani da kamarsa Rahima." Ta nisa tace "To Allah ya barku tare Rabiu, Allah ya kaika matsayin da zaka kyautata masa kaima.' Ya amsa "Ameen, insha Allahu zanyi struggling, bari harkar bukin nan ya kare mu gama karatunmu ki gani da taimakon Allah zamu ba marada kunya." Tace "Ko shakka babu sai mun ba mutane mamaki.". "Kar ma dai ace 'Yan B.U.K da suke yada surutan banza, kinji maganganun da suke yi dana Kai musu IV, wasu har karyatawa suka yi." Taja tsaki "Kai kake kulasu, ai ni banda lokacinsu balle in saurari surutunsu.". Suna nan tsaye Umma da Maryam suka dawo unguwa, ya durkusa ya gaisheta ta wuce cikin gida, Maryam tana tsokanarsa "Ango kasha Mai, har an fara Shirin angoncine?" Yai dariya "Ban sanki da haka ba Aunty Maryam, Ina kuka fito da dare Nan?" Ta amsa "Gandun albasa, kasan can za a Kai amaryar taka rufi wajen Inna kanwar su Umma, Kuma don Allah ka daina kirana wata Aunty sai kaina ya rinka girma." Rahima tace "Girma ai ya hau kanki Auntyn Rabiu." Ta harareta "Kina korata ne kawai Kar in bata muku hira, Rabi'u Saida safe, ke Kuma zaki shigo ki sameni." Suka yi dariya suna kallon shigewarta gida. Rabi'u ya kurawa Tahima ido tun tana kaucewa har ta gaji tace "Wai lafiya?" Ya jingine da bango ya amsa "Kallon kyakkyawar fuskar amaryar Rabiu nike, wallahi Rahima tunda aka sa ranar aurenmu so da kaunarki dada tofo suke cikin zuciyata, so da yawa ina share awowi ina tunanin zamanmu a school, yanayin shakuwarmu da irin ji da juna da muke ashe soyayya ce ke shigarmu bamu fahimta ba. A kullum godewa Allah nike days kaddaro kasancewar hakan tsakaninmu, da Allah bai rubuto ke mata ta bace Rahima ya zanyi da Raina, Ina zan Kai wannan kololon son da ya cika min Zuciya har ya zamanto babu sauran ko masaka tsinke na kaunar wata, Rahima you're my life, don Allah ki so ni yadda nike sonki.". Ta saki ajiyar zuciya kafin tace "Ina sonka Rabiu, kaunar da nike maka ne ta haifar da na amince ka zama abokin rayuwata.". "Na amince sosai Rahima nagode, bari in koma gida, ba sauran abinda kike bukata?"?. Ta kada Kai "Tsakaninmu ba wannan, lalurarka tawa ce kamar yadda tawa take taka, kasan nima 'gata ce su Umma sunyi min komi, kasan sun so a hada bukin nan dana su Maryam amma Allah bai kaddara ba Abbas ya roki arzikin a bari sai ya dawo daga Dubai, sha'anin Dan kasuwa.". "Lalle naji, Allah yasa shine alkhairi mu dai Allah yasa ba za a daga namu ba." Tayi murmushi kawai ba tareda bashi amsa ba. Ya fiddo kudin da Hjy ta bashi ya mika mata taki karba saida yace sakon Hjy ce ta tara jannu biyu domin karba, maimakon ya saka mata kawai sai taji caraf ya kama hannayen nata ya rike yana kallonta... Tayi saurin kwacewa tana fadin "A'uzu bilahi minal shaidanin rajim, wa iyazu billah." Shima yai saurin juya baya Yana tasa adduar korar shaidan din, kana ya juyo a hankali yace "Rahima ki gafarceni, banyi da niyya ba wallahi." "Hhmmm Allah ya gafarta mana Rabiu nasan ba halinka bane, babu zargi tsakaninmu." Yace "Nagode, gashi. A wannan karon hijabinta ta santa ta rufe tafukan hannunta shi Kuma ya saka Mata, suka yi sallama ya tafi cikin damuwa. Shaidan mugune, la'ananne, masheranci, Allah ka Kara yi Mana katangar karfe da dashi. Adduar da Rahima keyi kenan har ta shiga gida ta iske Umma da 2000 din da ya bata. Nan take ta fara fada "Anya Rahima ba nace karki sake karban ko sisi daga hannun yaron nan ba, yaro dan makaranta da wane hidimar zaiji taki ko nasa?" Ta durkusa "Umma naki karba ya tilastani Wai Hajiyarsa ce tace ya kawo min." Umma ta kyalkyace da dariya "Hjy Kaltume kenan, aikinta yafi da haka, wallahi kasancewar danta ne zaki aura yasa nike farin ciki, domin duk unguwar nan kowa yasan macece mai matukar sanin yakamata, ba a taba jin kanta da surukanta ba balle na tsakaninta da 'ya'yanta. Gashi Allah yasa babban danta ya saya mata wannan babban gidan take zaune da kowa lami lafiya, keni yadda labari yazo min ance ba irin wahalar da bata sha ba da mijinta na fari daga ita har danta, ance yai masa kaskanci kamar bashi ya kawosa duniya ba to ga sakamakon Allah nan tana gani, shi yaron ya zama kwararren likitan kwakwalwa ba unda sunansa bai Kai bba daga Nigeria har kasashen waje, ke naji ance ma har turawa hayarsa suke yaje can yai musu aiki su biyasa.." Tunda ta fara bayaninta ba tace komi ba Saida ta numfasa tace "Umma kema kina sauraren gulmar matan gidan buki ko?" Tace "Ba gulma bace, wafannan batutuwa da kika ji ba karya ba za'ida, Ni nasa aka binciko min don dole insan halayyar mutanen sa zan Kai Diyata cikinsu, ko nayi kuskure. Rahima ta kada Kai "Uhmmm Uhmm Ymma, Ni zani in kwanta.". Ta kalli kudin tace Dauka ki ajiye a jakarki ba zaki rasa amfani dasu ba bai kamata in kashe kyautar sarakuwarki ba ta karike tana dariya. Cikin shagwaba tace "Umma abin ya koma zolaya Kuma, Saida safe. 03/09/2020, 22:19 - Anty saliha: ...RAHIMA...doc by jami 8 Suka ci gaba da shirin buki har zuwa ranar daurin auren, Yayan ango ya biya sadakin Rahima lakadan, an daura aure lafiya an tashi lafiya, shagali ya rage na mata inda suma suka ci gaba da saukar qur'ani mai girma aka dora da wa'azi da nasihohi yayin walimar don taya ma'auratan murna da fatar alkhairi. Iyayen amarya sunyi rawar gani wajen gyarewa diyarsu dakunanta ras, sai wanda ya gani, sun kuma nuna bajinta wajen kawowa ango garan buhunnan abinci da su Mai da sauran tarkace harda kudin cefane a sama, a yayinda dangin angon suja karbi sabuwar 'yaruwar tasu hannu bibbyu. Sati guda suka dauka sua amarci sannan suka koma school don ci gaba da neman ilmi. Kafin nan Saida Rabiu ya zagaya da amarya gidajen 'yanuwansa kaf da abokan arziki don you musu ban gajiya su Kuma san juna, gidan Ya Haseeb ne farkon ziyarta inda suka yi karo dashi zai fita cikin hanzari domin ana nemansa a asibiti, sama-sama suka gaisa don Rahima ma ba zata tantance kalarsa ba, saurin da yake bai bashi damar tsayawa ba balle suyi masa godiya. Washegari Ya Hasseb ya Kira kanin nasa bayan ya bashi hakurin rashin tsayawa su gaisa a jiya ya mika masa key din mota "focus" a matsayin gift dinsa na aurensu tareda taya su murna da adduoi. Murna a wajensu bai faduwa, Hjy Kaltume kuwa harda hawayen dadi Saida ta fitar tana ci gaba da sanyawa Haseeb albarka. Wani weekend Rabi'u da amarya suka shiga kanti suka cikowa yaran Hasseb kayan kwalam suka nufi Galadanci misalin karfe sha daya na safe. Tuni yaran da mahaifiyarsu sun tashi sunata Kara kaina a kicin, Rabi'u ya sallama Rahima na biye dashi a baya dauke da ledan tsaraba. A guje yaran suks rugo suka nufo shi "Uncle oyo-yo. Ya duka ya dauki karamin mai suna Junaid suna kiransa Khalifa sabida sunan mahaifin maigidan kenan, shekarunsa biyu harda rabi, ya rike hannun babban Mai suna Mohammad suna kiransa Abba shima kasancewar sunan shakikin Haseeb ne Wanda ya taimaka masa kwarai a rayuwa kana shine surukinsa mahaifin matarsa Zuwaira, shekarunsa hudu. Zuwaira ta daina abinda take yi ta juyo garesu cikin murna ta rungume Rahima "Maraba lale da amare da ango, Rabiu ba kace min aure kake so daman tuni, kaga kibar da kayi kuwa, ko zan San sirrin?" Yayi wani irin juyi a tsakiyar kicin yace "Wasa Ni da kyau Auntyna amma kash sirrin tsakaninmu ne Rahima ko in Fadi?" Cike da kunya tace "Kyaleshi don Allah Aunty har akwai wani sirrin da ya wuce shagwabamun da kuke kullum." Zuwaira tayi dariya "Laifin Dakta kenan na fada masa ya rage Kar nan da shekara guda muga Rabiu ya aje tozo." Kusan awa biyu suka kwashe suna hira saboda ance Yayan nasu bai tashi daga barci ba. Rahima ta zauna gefe ta zuba tagumi tana kallon yadda Rabi'u ya kwanta su Khalifa nata dumurmusarsa,ya daga wannan ya aje, yaiwa gudan cakulkuli, su fada a jikinsa dukansu suna dariya, gefe guda ga kayan wasansu da suka watsar sunyi kaca-kaca, shaawarsu ya cikata Nan take tayi shaawar samun nasu babyn harta fara imagining yadda babansu zai rinka wasa dashi kamar yanzun, gaskiya Rabi'u mutum ne Mai son Yara.. Bata ankara ba taji yana gaida Ya Hasseb, tayi saurin gyara mayafinta ta zamo daga kujera ta durkusa gwiwa bibbyu ta gaida wan mijin nata cikin ladabi da biyayya. Ya amsa cikin yanayin da bata iya fassarawa don babu sakin fuska a tareda shi sam. Bai zauna ba ya koma falonsa Kaninsa ya bishi can ita kuma suja ci gaba da hira da Zuwaira inda ba a dau dogon lokaci ba ta lakanci halin Antyn tasu tas Zuwaira macece Mai harka,tafi mijinta sakin fuska nesa ba kusa a, tana da son mutane da saurin sabo saidai fa akwaita da surutu don cikin awanni kalilan ta fayyace mata labarinta kaf , na iyayenta da 'yanuwanta da na shi kansa maigidan nata, ta fada mata irin zaman da suke da irin matukar son da take masa. Wani Abu da ta lakanta Aunty Zuwaira irin matan Nan ne masu son rayuwar jin dadi kota halin kaka, masu son kashe kudi da neman kudin kota wacce irin hanya Kuma.. Da alamun ilmin addini bai gama ratsata ba, abinda tafi sani shine ta daura zani komin tsadarsa, ta saka latest takalmi ta rataya jika cike da dimbin naira ba tareda tunanin komi ba, tana da son cin dadi daoilin hakane yasa ko ta dafa nama a tukunyarta ka'ida ne duk daren duniya a sawo mata gasashshiyar kaza, 'yan shila, tsire ko balango taci ta kwanta. Babban abinda ya bata mamaki babu wani kusanci Mai karfi tsakaninta da mijin da take ikrari tana masifar son, kowa harkar gabansa yake..... Saida ta tabu kafadarta ta dawo daga duniyar tunani.. "Duk tunanin angon ya barki ne haka? Tafdijan da kece matar Dakta ya za kiyi?" Rahima ta share maganar tace "Aunty lokacin dora abincin rana yayi ko?" Ta zabura "Tabbas Ni bana manta inada baki cikin gidana ba, taso mu shiga kicin yau muci girkin amare." Suna aikin Zuwaira naci gaba da yi mata bayani nau'in sanaar sa take yi, Dubai take ziwa saro manyan bedsheets harda zinari, a cewarta ba zata iya wahalar karatu ko wani aikin gwamnati ba. "Me kike karantawa ne a school? Ta tambayi Rahima. Ta amsa "Special Education ne, tunda shi accountancy yake yi." Tace "Me ya kaiki karatun wani special education?" Tayi 'yar dariya "Wallahi Aunty Zuwaira Ina matukar tausayin yara makafi, gura gu da bebaye da kurame, da ma wadanda ake haihuwarsu da karamar kwakwalwa, a ganina hanyar da Zan iya taimaka musu kadai kenan." "Kice kawai kina son wahalar da kanki da rai da lafiyarki baki koyar a normal school ba sai makarantar kurame, ah ah wahala dai kike shaawa." Ta girgiza Kai "Banyi tunanin wata wahala ba gaskiya, abinda na sani shine kowanne aiki na zabawa kaina dole in zama Mai dauriya da hakurin jure kowacce irin wahala ke tattare da aikin, na zabi wannan fannin ne don bada tawa gudumuwar." Zuwaira ta gyasa Kai "Daukarwa rai dai Allah ya taimaka ai kin kusa karewa ko?" " Da ikon Allah karshen shekara nan zamu gama Basu tafi ba sai bayan laasar, zuwa lokacin maigidan ya fita tuni kafin ya fita ya ba Zuwaira kudi a baiwa sarakuwarsa. Da kyar ta amsa, a ganinta dawainyyar tayi yawa ta isa yanzun su ya rage su nemi nasu na kansu su ci gaba da kwatanta alkhairin da ake musu don shege kawai ke mance alkhairi Dan halas bai mantawa komin kankantarsa. Watanni takwas kacak suka rage su kare digirinsu na farko, cikin watannin ne Rahima ta Kara shakuwa da mijinta, kaunarsa ta fara zurfi da tasiri cikin zuciyarta har abin na daure mata Kai. Yanuwa da abikan arzikinsu sai shaawar zaman nasu suke musamman yanayin tafiyar da rayuwar auren nasu Tunda akayi auren sai Kara ji da juna suke, suna samun natsuwa da kwanciyar hankali irin wadanda ake samu muddin aka yi katari da dacen abokin zama, ba abinda yafi musu dadi illa Kara fahimtar juna da suke ko yaushe. Rahima bata da damuwar data wuce taga ta kare karatunta lfy, bayan so da kaunar mijinta tayi dace da sarakuwar da take ji tamkar ita ta tsugunna ta haifeta itama, koda wasa Hjy Kaltume Bata son ganin bacin ran Rahima ko na dakika gudane, duk abinda ta samu indai naci ne sai taba Rahima taci kafin takai bakinta, idan kudine ko yaushe tana tattalin ta bata su Wai karta zauna baby na kashewa, dangane da abubuwan hidimomin yau da kullum kuwa kamar su man shafawa sabulu wanka dana wanki duk wata zata kebe kudu a sayo ta kirata ta damkasu a hannunta, kayan lashe-lashe da tande-tande ba a maganarsu, ita dai Kar Rahima ta nemi komi ta rasa. Ita Kuma bata zubar sa tarbiyyar da akai mata tun a gida ba, daraja na gaba ko a Ina ne musamman tsoho, to ta mutunta wadanda bata San inda suka fito ba a titi ballanta uwar mijinta Mai kaunarta tamkar ta lasheta. Sai ya zama cikin surukanta babu kamar Rahima ba don ta kasance matar Dan autanta ba ah ah kima da girmamatan da take yi tun zuwanta gidan ya haifar da hakan. Kafin su fara karatu gadan garan ne suka shirya suka nufi Gumel gano kakanta da sauran dangin mahaifiyarta, duk sati zasu ziyarci gidajen 'yanuwa ba inda ta tsani zuwa sai gidan Hayatu sabida rashin zaman lafiyar da matansa keyi, ta tsani tashin hankali. Ba zata manta ba ranat da suka fara zuwa gidan ta riga Rabi'u shiga ciki tayi sallama aka amsa ta durkusa don gaida matar data gani zaune bakin famfo tana wanke-wanke, ta dago Kai ta Mike tsaye tana fadin "Lalle yau nayi farin gani, amarya Ina angon naki?" Kafin ta amsa Rabiu ya sallama yace "Aunty amarya gamu mun taho me kuka aje mana?" Sai nan Rahima ta gane wannan ce amaryar Yaya Hayatu sunanta Haulatu... Haulatu tayi dariya" Me kuka kawo mana goron amarci dai, ku shiga dafa ciki ka barta a tsakar guda tsaye." Yai musu jagora zuwa dakin uwargidan suka sallama bata amsa ba sai da ya daga labulen dakin suka ganta zaune abinta, Rabiu ya shiga ciki Rahima ta bishi syka zauna suka gaisheta ta amsa a ciki, suka zauna shiru-shiru na mintoci bata Kara ce musu kanzil ba, ya kada Kai ya umurci matarsa ta tashi su tafi, suka sake mara sallama ta share, suna fitowa suka shiga dakin Haulatu don su sake gaisawa itama su bata hakkinta, ita Kam tayi ta jansu da wasa har ruwa ta kawo musu da lemu tace su tsaya suci abinci kuma.. To ai kuwa zaman nan da suka yi dakin amaryarta ya tunzura Jamila, ta fito tsakar gida ta shiga masifa tana sakin habaici "Ahayye ayyririru, yau Ni za a gwadawa gulma da makirci irinta dangin miji, dadin abin kafin a auro wata Ni aka fara gani da sani dole a zauna dani komin kiyayya, magulmatan banza munafukan wofi.".. Ba Wanda ya futo balle ya tanka mata, ana haka Allah ya dawo da Hayatu gida daga wajen aiki, malamine a makarantar Shekara. Yana shiga gidan nasa yai katarin surutan da Jamila ke Fadi, Rabiu na jin muryarsa danuwansa ya fito Rahima ta biyo shi suja gaishe shi Yana amsa yace "Lafiya meke faruwa Rabiu?" Ya shafawa idonsa toka yace bai sani ba ya tambayi matarsa. Jamila tayi farat ta amsa "Dole kace baka sani ba mana algungumi, ka dauko wannan kekasasgahiyar matar taka Kun haddasa fitina, ta juya Kan mijin wallahi kayi mishi kashedi, hawainiyarsa ta kiyayi ramata.... Hayatu yaji zata zake ya buga Mata tsawa "Ke ar wallahi ko ki min shuru ko ranki ya baci sai in tattakaki yanzun nan inga me za ayi mutumiyar banza, ni kenan bani da ikon fita in dawo in tadda gidana lafiya, kaina farau aje mata biyu? To wallahi kinyi kadan, duk iskancin da za kuyi ku tsaya kaina Kar shegiyar data shiga sabgar 'yanuwana, sakararu marasa tunanin abinda zaije ya komo." Kafin ayi haka Haulatu ta banko labule ta fito a fusace " Ah ah Hayatu wasa yai wasa banda tsikarin uwar miji da tabarya, mene nawa a ciki Ni da na tarbesu nace su jira abinci, tambayesu kaji data fito tana masifarta wa ta bi ta kanta balle ya tanka, gaskiya ni ba shegiya ba ce da ubana kafi kowa shaidawa tinda Saida ka Kai masa sadakina ya baka aurena, shegun sakararru na inda suke." Tana rufe baki Jamila ta zabura sai tau! saukar mari, Haulatu ta rike kuncinta tace "Kika mare Ni? Wallahi baki isa ba sai na rama, itama ta zaburo tana jiran a dabance, Hayatu yai saurin riketa "Kyaleta Haulatu itace babbar kwabo ta yada girmanta.". Su ma bakin suka bata hakuri, da kyar aka ciwo kanta ta hakura suka iza keyarta ta shiga daki. Maimakon jamilan tayi shuru sai cewa tayi "Ai da Kun Kyaleta tazo ta rama din yau in gwada muku yadsa ake kirba mutum in lallasata in mata dukan da uwarta bata taba yi mata tunda ta fito duniya. Takaici ya kama Hayatu ya harzuka ya dumfareta yace "Bari ni in karairayaki kafin ki lallasata, tana ganin ta dau faskaren icce ya dumfareta ta sheka daki ta danne kofa gudun kar a sabauta ta. Suka bar su Rahima tsirma-tsirma a tsakar gida, yana basu hakuri, suka dawo gida su basu ci abinci ba su hankali bai kwanta ba.. Tun a lokacin bata sake marmarin zuwa ba, gidan Ya Haseeb Kuma iya yin Aunty Zuwaira ke damunta 04/09/2020, 00:24 - Anty saliha: ...RAHIMA...doc by Jami 9 Sauran watanni uku kacal su zana jarabaea akayi bukin Maryam ta auri Alh Abbas dinta, matarsa guda da yara shidda maza da mata suna zaune a sabon fegi. Da alamun Maryam ma Bata dace da Uwargida ba sai abinda Allah yayi kenan domin ita ma ba baya ba wajen kishi da rashin hakuri sam bata yarda a takata ko a wulakanta ta. An dai yi buki an kare lfy babu wani gagarumin tashin hankali sai 'yan kunji -kunji ko Kuma don Alhaji Abbas namiji ne daya iya rike gidansa ba kamar Hayatu ba da ya zama shakulatin bangaro, yayi sake iyalinsa suka fi karfinsa. A kwana a tashi Rabiu da Rahima sun kare jarabawarsu sai adduar Allah yasa ayi nasara. Bayan sun huta na sati biyu ta rokeshi ya kaita gidan 'yaruwarta, ya amince ya dauketa suka tafi. Sun shade awa uku suna hira amma Rabiu bai sa niyyar tashi ba, Maryam tace "Ni fa ban gane ba shin ba tafiya zaka yi ka bar min ita anjima ka dawo daukarta ba?" Ya kwashe da dariya "Kina nufin in koma gida Ni kadai? Gaskiya ba zan iya ba, kafarta kafata." Maryam ta kalli Rahima "Say something kinji Wai ba zai barmu muyi hirar zumunci ba." Ta danyi dariya "To shin din bare ne?" Yace "Kyaleta kawai ta nuna min 'yan ubanci alhalin an zama daya Ni da Rahima. Maryam ta daga Kai "Ai ga alama nan na gani tun zuwanku, Ina ruwan Romeo & Juliet. Yayi dariya "Kuma ba a hanaku ba." "Ah ah Wannan irin soyayyar sai ku yara, Ni mijina tsohone bayan haka ina yaga wani lokacin soyayya Yana can yana neman mana na sakawa a bakin salati." Rahima ta jinjina "Ke din yadda kike?" "To naji na amince Amma don Allah Rabi'u ka tsahirta mana kona rabin awa ne, magana Nike son yi da ita, zancen na Mata ne Kasan akwai sirri." Ya kalli matarsa "Kin amince in tai in dawo Nan da awa guda?" Rahima tayi masa irin kallon soyayyar nan tace "Is okay, nagode." Ya mike ya sumbaci gefen kumatunta "Sai na dawo kenan.". Yana fita Maryam ta juyo gareta "You surprised me, I was impressed Kar dai ince kun kamu?" Ta kishingide ta amsa "Ina zaton hakan Nima, a hankali so da kaunar mijina suka rinka shigata saboda duk da kasancewar sa yaro matashi ya iya tafiyar da al'amarin rayuwar aure yadda yakamata, ko ya fahimci feelings dina ne ya bi duk hanyoyin da suka dace ya mallaki zuciyata, idan kinga irin kishina da yake sai kin rike Baki, ya fara fadin Wai anya zai barni inyi aiki kuwa, ga kulle, idan kuwa ya bari na fita to ki tabbatar da tare zamu fita, ke al'amarin nasa tun Yana ba Hajiya shaawa ta fara nuna damuwa tace tun kafin aje ko Ina zai bullo da sabon al'amari? Ni kuwa maimakon ya dameni ko inji haushi sai dadi nike ji, Ina Kuma ji a zuciyata muddin ya tsaya kan va zanyi aikin ba zan amince don ko kusa ban son abinda zai batawa masoyina rai." Maryam ta kura Mata idi sosai tace "Tabbas kina kaunarsa amma har yanzun da sauranki baki shiga matakin da Zaki ji amsarki ba, akwai sauran lokaci tukunna." Rahima tace "Haba dai duk nike ji dinnan da saurana?". "Kwarai kuwa idan lokaci yayi zaki fada min da kanki, yanzun kashi talatin kike dashi cikin dari kina awo aiki ko rabi baki Kai ba." Ta nisa "Ashe in Kara zage damtse tun kafin bakon dake tafe ta/ ko ya kutso kai ana hanamu shakatawa." Maryam ta bude baki cikin mamaki "Lah kema ciki gareki Rahima? Labarin da zan fada miki kenan Nima, shikenan za mu yiwa Umma tagwaye sunan da take kiranmu." Suka rungume juna suna adduar Allah ta inganta musu ya Kuma saukesu lfy idan lokacin yayi." Bai Kara ko minti guda ba, awa dayan na cika suka ji horn din motarsa suka kalli juna, Rahima ta mike ta dau Jakarta ta gyara mayafinta tace "Mu zamu tafi sai kinzo kenan?" Tace Insha Allah, uhhmm did he know about the pregnancy?" Tace "No but yau zan sanar dashi tunda na tabbatar" Suna fita Maryam ta riko hannunta ta mika masa tace "Rabiu manya, to ga matarka, ban cinyeta ba balle in gutsuri namanta " Ya sosa keya "Ba haka bane Aunty... Ta katsesa "Kwarai na fahimta to Allah ya bamu alkhairi, sai nazo." A wannan ranar wani sabon nishadi ya rufesu suka jima suna hirar soyayya kasancewar a ranar suka shekara daya cif da aurensu, sunyi nafilfili da adduoin godiya ga Allah SWT kana suka kwanta. Bata yi hanazarim shaida masa batun cikin ba Saida dare ya tsala ta tashesa daga barci, ya tashi ya kunna fitila ga zatonsa ita a bata da lfy yace "Lafiya? Ta kura masa idanu tana nazarinsa, duk da cewan barci ya farka yai Mata wani irin kwarjini, fuskarsa sai sheki, ya Kara kiba da haske, tayi ajiyar zuciyar, Rabi'u yarone matshi amma girman jikinsa kansa ayi kuskuren shekarunsa, suna mugun kama da Hayatu sai dai ya darashi tsayi da jiki, Hayatu farine mi yar doguwar fuska,mutum ne Mai fara'a da son mutane ga ban dariya, kusan ko yaushe ka gansa hakoran nan bude suke Yana dariya, da wuya ayi masa Abu ya bata masa rai har yai fushi, wadannan kyawawan halayen nasa yasa yake da jama'a da abokai babu iyaka. Ya kagu da kallon da take masa ya girgizata "Wai shin lfy. Tayi "yar dariya "Hakan nan kawai kwana nan sai inji kana matukar burgeni ko kallonka nayi sai inji wani dadi a zuciyata.". Ya zumburi baki cikin wasa "Kawai kika tasheni barci don ki kalleni kinji sanyi a ranki ne?" "To me zanyi maka da dare Nan, kishi ko yunwa?" Ya janye matashin da take rungume dashi a cinyarta ya maida kansa ya kwanta a wurin Yana mai sakin kyakkawar ajiyar zuciya yace "Ni kuwa ni'ima nike ji duk lokacin dana kalleki, shin Rahima kinsan irin mutuwar son da nike miki kuwa? Ta rufe bakinsa "Rayayyen so dai mijina idan kace mutuwa ai ba zance kenan, na yarda da so da kaunarka, nima hakan yake a zuciyata, domin Ubangiji ya karfafa mana dankon soyayyarmu ne ya bamu wannan." Ta kamo hannunsa ta dafa cikinta. Da farko bai fahimci inda zancen ya dosa ba, daya dago ya zabura ya cakumota ya riketa gam ya fara tsalle Yana sumbatarta "Da gaske cikine dake Rahima alhamdulillah." Tace "Da gaske Ina dauje da bebinka Rabiu amma idan baka daina juyi dani haka a tsakar daki ba zamu ita rasawa don likita ya shaida mun saina rinka kukawa in bi a hankali mahaifata Bata da kwari. Nan da Nan ya ajiyeta a hankali yace "Are you ok?" Tace "Banda wata matsala sai adduar Allah ya rabamu lfy." Murna ta rufesa ba sauran barci kenan, ya zauna ya fara plan din tarbon jaririn da sauran kusan watanni bakwai kwarara kafin ya fito duniya. Alla- alla yake ya kare sallar asuba, ya shuga gaida Hajiya yai Mata albishir, saboda tsabar farin ciki ranar tuni tayi Bata ci komi ba, farin ciki ya kosar da it's, can gidansu Rahimar ma abinda iyayenta suka kashe suka tsare kenan, jiran ranar haihuwar 'ya'yansu biyu, Maryam da Rahima. 04/09/2020, 13:45 - Anty saliha: ...RAHIMA..doc by jami 10 Lokacin tafiya bautar kasarsu yazo, Rabi'u ya shiga ya fita aka barsu a garin Kano, inda shi yake Bank Rahima Kuma ke koyarwa a makarantar kurame. Watanni bakwai da 'yan kwanaki Rahima ta kamu da zazzabin malaria, Rabi'u ya rikice musamman da yaji likita ya gaya masa ba a son mai ciki ta kamu da zazzabin saboda yana iya haddasa miscarriage ko yaiwa uwar lahani. Kowa ya dukufa adduar Allah ya bata lafiya ya kareta da abinda ke cikin, kwana biyu kamar taji sauki ana uku zazzabin ya dawo wannan karon hade da ciwon baya da mara. Likitoci sunyi kokarinsu amma kafin awa guda nakuda ta taso haihuwa ce gadan-gadan, da taimakon Allah ta haihu lafiya ta sami danta bakwaini. Iyaye da 'yanuwa da abokan arziki suka cika asibiti sai dai kash da kyar aka barsu suka ga jaririn a hannun nurse aka wuce dashi aka saka shi cikin incubator sabida bai gama yun kwari ba ga rashin lafiyar jundice da akan haifi wasu jariran dashi. Ba a sallamesu ba sai ana gobe suna tare da gargadin Kar a bari a rinka daukar yaron gudun jagwalgwalo Hajiya Kaltume ta Kira Rabiu don su shawarata sunan da za a sanyawa jaririn yace "Hajiya na riga nayi masa huduba tun ranar da aka haifesa kinsan addini ya koyar daamu da zaran an haihu mu yiwa yaranmu huduba,bayan munyi musu Kiran sallah da kalimatu-shahada a kunnuwansu ba sai an jira sai wani ranar suna ba. Koyar Manzon Tsira ne." Tace "Naji ustaz, wane suna ka saka masa Ina fatan ba irin na zamanin nan masu wuyan Fadi ba." "Ko daya, wannan ko sau nawa zaki iya fadi cikin mintu guda kacal." "Wai zaka fada min ko sai ka gama ja min rai Rabi'u?" Yayi dariya "Sunan Ya Haseeb yaci, Abdul Haseeb karami ne Hajiya." Ta gintse dariyarta tasha mur "Maimakon ka sa sunan mahaifinku da Allah yaiwa rasuwa, mene naka na saka sunan wanda yake raye?" Rabi'u yace "Ina Sunusin Ya Hayatu sunan baban yaci Hajiya, tunda yasa ba lale nima sai na saka ba, bukata a samu magaji an samu ai, ba Kuma sai mutum ta mutu ake saka sunansa ba, Hjy Ya Haseeb ya cancanci wannan adalcin daga garemu din da taimakonsa Allah ya hadamu aure, don haka kiyi fatar alkhairi kawai.". Daman ba Wai bata ji dadi bane, ah ah ta yaba da kaifin hankali da tunaninsa kwarai, ta gyara zama tace "To Rabiu Allah ya raya mana shi yasa dadin musulmi ne yasa ya gaji mai sunan." "Yauwa yanzun ki Kai magana, Ameen Hajiyata." Anyi suna an ci an sude, Hasseb babba yana can wani aiki a babbar asibitin dake kasar Morocco, sai labarin haihuwar yaji da labarin anyi masa takwara. Da zai dawo sayayyan musamman ya yiwa uwa da namesake dinsa din nuna jin dadin karamcin da aka yi masa, yazo har gida yaga jaririn da ake fadin yafi kama dashi a bisa mahaifinsa. Cikin watanni biyu Abdul Haseeb ya murje yayi 'yar kiba har ya fara wayon gane iyayensa da kakarsa da yake yini can wajenta. Suna gab da kare bautar kasa wata rana, Rahima ta gama shiryawa maigidan abincin rana ta girka masa tuwon shinkafa miyar alayyaho abincin da yafi so kenan, sai gashi ya dawo ya hayo sama dauke da Abdul a kafadarsa yana rike da jakar aikinsa a hannu daya. Ta tarbesu ta amshi jikar tana masa sannu, ya amsa Yana ci gaba da yiwa dansa wasa, ta tsaya ta zuba tagumi tana kallonsu tace "Kana bani mamaki, yanzun daga shigowarka kaje ka dauko yaron nan ko kunyar Hajiya baka ji, haba ana son kawaici don Allah." Ya kyalkyace sa dariya "Ita Hjyr bata damu ba, ki tuna tun safe yake wajenta sun yini tare, Ni kuwa sai yanzun na Sami damar wasa dashi." Ta kalli Abdul "Hhmmm ko baka koya masa kimi ya koyi kyuya, duba yadda ya kura maka ido Yana kallonka." Rabiyu ya zaunar da Abdul bisa cinyarsa yace "Da Kuma fa gaskiyarsa gashi ba nine babansa ba." Ta bude baki cikin mamaki "Ba kaine ba to waye ubansa?" Ya amsa "Maida wukar, nina haifi abina mana Amma Ya Haseeb ne babansa." Ta hararesa cikin wasa "Tunda aka haifi yaron nan kake wannan furucin, kowa yasan a mtsayinsa na yayanka dole a kirasa baban Abdul ka taba ganin an raba anta da jini?" Yace "Inda Mai iyawa ai sai a basa ya gwada mu gani." Ta gyara zama "Hhhh Ni dai kawo sa kaci abinci." Ta karbesa ta goya, ta jera masa abincin ta zuba masa suna hira, yana cin abincin yana dan tsayawa , can ya ture plate gefe yace "Na koshi." Ta kallesa cikin damuwa" Abinda na lura kwanannan baka son cin abinci ka koshi har ka fara rama, wani Abu na damunka ne?" Ya girgiza Kai "Ba wani abu bane, just cikina ne ya cushe ko naso cin abincin sai inji na koshi dole nakan hakura." Tace "To muje asibiti mana, mutym ya zauna sa cuta a gida?" Ya taso ya dafa kafadarta "Karki damu kanki da yawa, dazun da ya taso min a office Nan da Nan na ziyarci clinic dinmu suka ban magani nasha naji dadi wallahi sai anjima karfe tara na dare zan Kara sha." Fuskarta ta canza "Rabi'u baka da lafiya ka boye min?" Ya rungumota "Afwaan Rahima ba wani sabon Abu bane da baki sani ba, kinsan na kanyi ciwon ciki muna school amma after 3-4 days nakan sami sauki inci gaba da harkokina, a gaskiya na dade ma banji ya tashi ba that's nima ban koma asibiti ba amma insha Allah gobe sai mu tafi." Tace "A takaice ma baka San kowacce irin cuta ke damunka ba." Yace "Sun Fadi Amma ban wani rike ba na manta." Ta sassauto "Hhmmm to Allah ya saukaka ya baka lfy, Amma don Allah ka kula da kanka, we do need you." Yayi murmushi "I need you too my love." Gari ya waye, bayan sun kammala ibadarsu da yin kalacin safe suka fara Shirin fita wajen aikinsu, Rahima na duke tana shirya Abdul taji wata irin kara mai firgitarwa, ta saki Dan ta nufo Rabi'u dake kwance dafe da cikinsa tabbacin karar daga makoshinsa ta fito, a rude tazo ta dafa shi tayi kokarin dagasa ta kasa, ta kira sunansa ya amsa da kyar yana numfarfashi yace "Cikina Rahima.... "Sannu, bari in Kai Abdul wajen Hjy mu tafi asibiti... Ta sungumi Dan ta sauka kasa a guje ta isko Hjyr na azkar ko gaisheta bata tsaya yi ba ta mika Mata Abdul tana fadin "Hajiya babansa babu lafiya asibiti zamu tafi." Ganin yadda take a rude itama ta goya Abdul ta bi bayanta suka hau saman tare a ranar bata ji wuyar data kance yana mata ba . Taga halinda yake ciki, har kamaninsa sun canza, ta sake fitowa tayi waje neman makwabta suzo a taimaka musu a fito dashi. Kafin kiftarwa ido maza sun taru an daukoshi an saka a mota suka nufi asibiti, Rahima da aka hana binsu kuwa gidansu ta nufa tana kuka, suna jin abinda ke Nan, Alh Mamman da kansa ya daukota da Ummansu suka nufo gidan Hajiyar inda suka taras ta kira Yayyinsa tana fada musu su wuce asibiti suma gasu nan tafe. Asibitin Murtala aka kaisa inda da shigarsu ba bata lokaci manyan likitoci su kayi caa a kansa, nan da nan babban likita yace aje ayi hoton cikin don sanin matakin dauka da gaggawa. Dr Haseeb da Hayatu suka isa hankali a tashe, suna ganin halinda yake ciki suka dimauta. Anje anyi hoton, likita ya duba ya fara rubuce-rubucen magungunan da za a fara bashi kafin su gama bincike Rabiu ya bude ido da kyar ya hango dushi-dushin Haseeb, ya dago hannu a galabaice ya miko masa, Haseeb ya fahimci magana yake sonyi don haka ya duka daf da bakinsa... Cikin rada maganar ta fito "Ga amanar Rahima da Abdul.... Yace "Na karba Rabiu Allah zai baka lafiya... Haseeb bai gama rufe bakinsa ba Rabiu yai kalimatu-shahada ya cika.. Nan aka yita . Dagowan da bai ita yi da kansa ba kenan Saida aka kamashi yana salati .Innalillahi wa Inna ilahirrajiun. Mutuwa kenan, daci Mai kore Zaki, Mai raba da da mahaifi, Mai raba Mata da miji, Mai raba danuwa da danuwa, Mai raba masoyi da masoyi, Allah yasa mu cika da imani. Duk da cewa Ubangiji yace bai halicci wani don wani ba, a ko yaushe muka yi rashin daya daga cikinmu al'amarin Kan zama sabo, bamu iya dauriya dole muyi juyayin rashi da tausayin kanmu tare da fargaba da tunanin cewan muma fa komin dadewa wata rana sai mun tafi lahira. Allah yasa mu cika da imani Maganar halinda yanuwa da abokan arzikin marigayi Rabi'u suka kasance bata ko taso ba balle matarsa Rahima, Hajiyarsu kawai Allah ya saukarwa dauriyya ta dake ita ke baiwa jamaa hakuri Bayan kwana bakwai kowa ya watse sai wasu daga cikin dangin uban Rabiu da kanun Hjy Kaltume Mata biyu don suci gaba da debe musu kewa. Hayatu ma Kan kawo matansa su yini. Wani ikon Allah rasuwar Rabiu ne ko shiriyar Ubangiji ne yasa yasa su natsuwa da kama kansu har jamaa na mamakinsu oho. Shima Haseeb matarsa na zuwa ta koma da laasar, Maryam ma na tafe duk bayan kwana biyu, jamaa kowa nata kokarin ganin an debe mata kewa. Ita kuwa sai kallonsu take, hawaye sunki kafewa a idanunta musamman idan ta dauki Abdul tana bashi nono. To tun hawayen na zuba har sun kafe ta fara kukan zucci. Idan ta tuno rayuwar da suka yi, watau haka Allah ya kaddari rabon Abdul ne yasa akayi aurensu a gaggauce, rabuwar ma Allah ya kawo kwatankwacin hakan. Oh Allah ka jikan Rabiu ka sanyaya masa, hakika sunyi rayuwar auren daya dace, rayuwa mai cike da nishadi da farin ciki abin shaawa fa kowa, da karshen tazo Allah yasa shakuwa tsakaninsu bayan so da kaunarsa da suka fara tasiri a zuciyarta, Ashe Wai ba za akai ko Ina ba, Ashe rayuwar tazo karshe.... Hawaye masu zafin gaske suka gangaro zuwa kumatunta suka diga kirjin Abdul, ya saka kuka, ta lallasheshi, ita tama manta Yana bisa cinyarta, da Hjy Kaltume ta lura ta shiga yi Mata fada, ta dawo tayi nasiha taci gaba da lallashi, maimakon tayi shuru hawaye sai Kara fitowa suke Saida ita kanta Hajiyar da sauran mutane suka koka. 04/09/2020, 17:24 - Anty saliha: ...RAHIMA..doc by jami 11 Kafin ta gama takaba 'yanuwa, iyayenta da dangin mijinta kaf sun nuna mata gata Kuma ita wata ce a gare su don Haseeb ma ba a batun dawainiyar da yake musu ita da danta Abdul karami, tun bai saba da wan uban nasa ba har yai sabo dashi kwarai saboda yawan dauka da fita dashi yawo da yake in baida aiki sosai a asibiti... Kwanci tashi ba wuya Rahima ta gama takaba, ta Kara sati guda da kyar kana ta tattara kayanta tace gidansu zata koma. Wani sabon tashin hankalin, ranar Abu ya koma sabo to amman barin gida ya zama dole don ci gaba da harkokin rayuwa. Bisa yarjejeniyar ba zasu amshi Abdul ba sai ta sami wani mijin ta goya danta suka koma inda tafi wayo, gidan Alh. Mamman. Makarantar da take koyarwa basu saketa ba ko bayan gama bautar kasarta nan suka dauketa aiki taci gaba da koyarwanta. Gama takabarta keda wuya masoya suka ce sallamu alaikum, harda wani abokin Rabiu da suka kare school tare, wani ikon Allah saurayine shi ko auren fari bai yi ba, ya kasa dumfararta da kansa sai letter ya tura mata Wai Yana jin nauyi, yadda bata saurare shi ba haka taki sauraren kowa cikin zawarawan dake mata Kara kaina tun daga wajen aiki har gida, da ma wani abokin Alh Abbas mijin Maryam Wanda uwargidansa ce ta rasu ta bar diya biyu, Yana son suyi aure ya rike Mata da ta rike masa nashi, shima bata cewa Abbas din tana yi ko ah ah ba, kusan duk Wanda ya nemi kusanci sai tace a bata lokaci tayi shawara, a zahiri kuwa ra'ayin sake auren ne bashi a zuciyarta, a nata tunanin ma da za a barta haka zata yi zamanta din tasan zata iya tsare mutuncin kanta dana iyayenta tunda Allah bai halicceta kharija ba, wai don a matsa mata da batun auren ne taki yaye Abdul da ya Kai kusan shekaru biyu. Umman tayi-tayi ta gaji tasa mata ido, gara bata son bacin ran Rahima daidai da kwayar zarra, suka ci gaba da lelen Dan da yake gudu koina, wani burgewa ma sai ya gama yawonsa ya dawo ya zauna yace 'Mami zan Sha mama' Irin sangarcewar da yayi Maryam ta taho ta gani ta fara masifa, Umma ta fara kakkare Rahima, ita din ma tace Umma karki kula surkulenta, shin don ta yaye Walida sai tace sai na yaye Abdul?" Umma tace "itama ba yayen Allah tayi ba ciki ya sa akayi saurin hanata nonon.". Rahima tayi dariya "Ah to gane min hanya Umma na makaho da yaso tsegumi. Kin ganni ni ba miji ba, Ni ba wani kwakwkwaran bazawari ba mene nawa na hanzarin cire yaro a bakin nono, Maryam ko tausayin Abdul ma ba kya ji." Taja tsaki "Ke da Umma ke ban tausayi sabida ga gaskiya kiri-kiru Kun take, shun Umma kin kalli diyar taki da kyau Kinga yadda ta kode tana kanjamewa?" Cikin damuwa tace "Na lura sosai, nima ramar nata har tsoro take bani, yarinya taki sakin ranta ta hakura, wallahi kullum fadar da nike mata safe da yamma kan ta fauwalawa Allah rashin da muka yi shi Kuma Allah yasa yana cikin rahamar Ubangiji.' Maryam ta gyara zama daman gangara take nema tace "Umma ban tari numfashinki ba, ya za ayi ta samu natsuwar hankali tana zaune muku haka kawai. Ni a ganina duk halinda data shiga laifinku ne, baku matsa mata ta samu miji tayi aure? Kawai Kun Kyaleta sai biye mata kuke, har kin yayen nan don kar a sami kafar mata batun aurene." Rahima ta harari Maryam "Umma ki daina saurarenta kinsan halinta da zuga." Umma ta nisa "Wannan karon Kam gaskiya take Fadi na Kuma gano kamshinta bari Baffanku ya dawo." Ta sunkuyar da Kai ta dafa Umma "Don Allah karki hadani da Baffa Umma nayi alkawarin yayesa cikin satin nan.". Maryam tayi Mata gwalo tukunna kafin taci gaba "Ai ba yayen ba ta fitar da miji shine batu, tayi alkawarin zata amince ba zata kara kin sauraren wani abu har Allah ya zaba mata mijin." Rahima ta rike haba. "Oh ni na shiga uku, Maryam hala kudin kanfen Alh Surajo ya Baki?".. Umma ta kallesu "Wani ne Kuma haka?" Maryam ta gyada Kai "Kyaleta Umma da 'yar halas take magana, amma ba za aji mutuwar uwar sarki a bakina ba, ta fada miki ko waye shi." Baki dai shi kan yanka wuya, dole ta yaye Abdul din ranar jumma'a bayan an aikawa kakarsa. . Kaji, zabbi,madara dasu bornvita da sauran tarkace banda sabbin tufafi aka tarkato, banda buhun shinkafa da jarkar Mai, matan Hayatu suke takewa Hjy Kaltume baya wajen zuwa diba Dan yaye, shima wan baban nasa kudi ya bashi matansa kuma crates din kwai. Rahima na gida bata futa aiki ba saboda zazzabin da ciwon nono ya sa Mata, ganin bakin yasa ta tashi ta zauna. Bayan an gaisa Abdul ya dare bisa cinyar kakarsa yana baje sabbin kayansa. Umma nata zubawa su Hjy Kaltume godiya. Hajiya tace "Duk aikin iyayensa tawa tukunyar farfesun na gida sai ya taho zai ci. Umma ta kalli su Hayatu "Madallah Allah ya baku ladan zumunci." Yace "Ba komi Umma Abdul danmu ne koda Rabi'u na nan balle yanzun da kasa ta rufe idanunsa." Tun dai Rahima na dauriyyar Kar suga kwallan da take kokarin maidawa har ta bara sai nishin kukanta suka, hankalin kowa ya tashi din sun san ba shakka uban Dan ta tuna. Ana haka Baffa ya shigo cikin sauri ya tsugunna suka gaisa da bakin kana ya fara rarrashun diyarsa cikin kalamai masu taushi har hankalinta ya koma jikinta ya kara yin godiya ya fita.. 04/09/2020, 21:15 - Anty saliha: ...ˆRAHIMA...doc by jami 12 Sun dade suna taba hira tun Rahima bata saki jiki ba ta warware a nan ne Jamila ke ce Mata "Kiri-kiri kin guji gidanmu Rahima." Haulatu ta kalli uwargidanta tace "Ke dai bari Yaya nima abinda ke zuciyata kenan." Rahima tayi murmushi tace "Aikine yai min yawa a school amma kuyi hakuri Ina nan zuwa." Hayatu ya kalli matansa cike da jin dadin ganin yadda suke tafiyar da al'amurransu yanzun sabanin da, yayi murmushi yace "Idan baki taho don komi ba Kya zo mana murnan tafiya sauke farali ko don Allah yayi bana za muyi arfa Ni da Jamila." Tace "Iye! Shine baku Fadi ba tun zuwanku, laifinki nan wannan Aunty amarya." Haulatu tace "Yi hakuri wallahi labarin dana kunso in fada miki suna da yawa ganinki haka yasa nayi sanyi, da gaske Ya Haseeb ya biyawa Maigidan da Uwargida kujerar hajj bana." Jamila ta amshe "Itama amaryar anyi mata alkawarin badi da ita insha Allahu." Umma ta kalli Hjy Kaltume tace "Masha Allah Kai Allah yai wa wannan yaro albarka, shi dai dukiyarsa ta dawainiya da jama'a ce, kunga hidimar da yake yiwa su Abdul kuwa?" Hjy Kaltume tace "Don Allah ki bar wannan maganar Habiba, kula dasu ya zama dole." Rahima ta kalli su Hayatu tace "Naji dadin jin labarin nan, Allah ya nuna mana anje an dawi lafiya, shi Kuma Allah yai masa sakayya yasa muji na Aunty amarya haka badi idan muna raye." Daga nan sukayi sallamar tafiya, Rahima ta rakosu kofar gida tayi musu alkawarin ziyartarsu wani satin. Bata tafin ba sai wajen sati na uku bayan tayi sarai ta koma tamkar bata taba wani shayarwa ba. Tana isa gidansu Hayatu ta kara tabbatar da ba abinda yafi zama lfy da kwanciyar hankali, yanayin gidan ya canza, maigidan ya Kara gyara ko'ina tsaf, mata da yara sunyi shar, shima yayi fes har kiba yayi ya fara teba. Ta kasa boye sha' awarsu cikin hira tace musu "Nifa kun burgeni, Ina mamakin canzawarku, wani shahararren malami yai muku waazi ya shige ko Yaya? Suka kalli juna suna murmushin fahimta kafin Jamila ta fara magana "Alamarun Allah ne, kinsan idan yaso mutum da shiriya, ba abinda myuke yanzun sai godiyar Allah da ya ganar damu." Haulatu ta karba "Wallahi mun fahimci ba abinda ke jawo tsiya irin tashin hankali da masifa." Hayatu yace "Nima kullum cikin godiyar Allah nike, da har fargabar shigowa gidana nike, dana doso kofar gidan sai gabana ya Fadi don ban San bala'in da zan shigo in taras ba, Ina kuwa shigowa abinda nike gudun zan taras, kiji harshensu na tashi kamar zasu dafa naman junansu, inyi -inyi su bari ko kallo ban ishesu ba sabida sun riga sun hau dokin shaidan Yana sukuwa dasu. "To kuma meye na tashin tashina, kuskure ne munyumi, mun gane mun tuba mun dawi hanya. Jamila ta koro jawabin... Haulatu tace "Rabu dashi dai Hajiya to waye bai kuskure?. Rahima tayi dariya "Kwarai dukkan Dan Adam ajizi ne dole a samemu da aikata kura-kurai yau da kullum shiyasa ake son mutum ya rinka rokon Allah ya shiryar damu hanya madaidaiciya ya Kuma ganar damu ya bamu ikon bin tafarkin gaskiya, kana ya yafe Mana zunubanmu na biye da sarari, wadanda muka sani da wadanda bamu sani ba.Amma Ina ganin fa tun farko laifinka ne Ya Hayatu.".. Ya kalleta cikin mamaki "Kamar yaya? Alhalin kullum Ina kokarin yin adalci tsakaninsu, fitina ce kawai amma da suka ga ba riba sun sauke.". "Au Kuma haka zaka ce?" Suka tara Fadi Rahima tace "Ni dai na fahimci bala'in son Yaya kuke shi ya jawo muku bakin kishin Nan." Ya sosa keys "Haka ake so? Ina ce in har son ne competition din kyautata min ya dace suyi ba rigima da juna dani kullum kaina dana aje su ba, tsaya kiji wani sirrin kanwata wallahi da sunci gaba da shirmensu ko da yanzun na Kara aure din har na kusa gama shirya komi, Kuma banyi niyyar hadasu gida guda ba, in. Koma can in tare hankalina kwance su kuwa suci tsiyarsu nan inga karyar kishi." "Allah ya tona maka asiri, ashe amanar mu kaso ci muna zaune tun baka da komi daka samu shine zaka dauko wata taci arzikin? Da wallahi kun gane kurenku data gwammace bata aureka ba." Rahima ta dafe kai tana dariya tace "Wai ni kaina Ya Hayatu ka yarda da batuna, Kuma na baka goyon baya muddin suka ci gaba da halinsu ka aikata abinda kace daga nan a ga wacce tafi sonka.". Suka taso kamar zasu cinyeta danya dyk da sun san wasa take, Saida ta basu hakuri tace ai ba sauran batun wata amarya tunda kun hada Kai Kunji ance zama lafiya yafi zama dan sarki, muddin za ayi hakurin zama da juna sai kuga Allah na taimakanku, wadata ya sameku, maigida yaji dadin kyautata muku, yaranku su tashi cikin ingantacciyar tarbiyya da kyakkyawar hadin Kai da zumunci da son junansu ga kwanciyar hankali da samun natsuwa.".. Suka ce wallahi mun gane kanwarmu Allah ya ganar da sauran mata Ina alfanun mugun zama, mun gode da shawarwarinki, Allah ya kawo mana suruki nagari." Nan da nan ta bata fuska "Anya zaku same shi da wuri?" Hayatu yace "To aure dai sunnar manzo ne nasan kinsan hakan, mu ba zamu so ki zauna ba aure bayan rasuwar Rabiu ba sai a rinka zargin wani abu." Ta nisa "Ai ba cewa nayi ba zanyi ba, Kai kasan zaman da mukayi da kaninka, Ina zan samu Mai kwatankwacin halayensa?" Jamila tace "Su din dangin gujiya ce, sai an fasa ake sanin na kwarai, ki fasa ki gani Mana." "Na tabbata zata sami Mai gari kuwa, mu dai mun kosa mu sha buki." Tace "Tsokanata ma kuke, bari in shige gidanmu. Ta koma gida tana tunanin hirarsu dasu Hayatu. Aure? Ita har tsoro kalmar ke bata ba don komi ba sai domin rashin cikakken kwanciyar hankalin zabin wanda zai zama abokin rayuwarta da tunanin yadda zata Kara sake koyo kaunar wani da namiji tunda har lokacin bata sami Wanda ma ya kwanta mata a rai ba ko jininsu ya hadu balle a kai ga batun aure.. Maganar abokin marigayin ma bata taso ba don a ganinta da zata aureshin ma taci amanar marigayin kenan duk da ba addini ne ya hana ba, a daya bangaren surutun jama'a fa kasancewarsa saurayi Wanda bai taba aure ba, ita kuwa harta haihu, shin zata iya daure gutsuri tsoman daka iya yiwa auren dabaibayi? Ina batun danginsa, shin zasu karbeta ba tareda wata tsangwama ba,? Ajiye batunsa a gefe shine alkhairi,to Alh. Suraj fa dake da magoya baya irinsu Maryam harda Umma da ta fara shiga ciki, idan bata yi taka tsantsan ba sarkin yawa yafi sarkin karfi lalle suna iya taruwa sufi karfinta, ta tsaya tayi nazarin Alh Surajo lalle yes mutum kamili sai dai ba nan gizo ke sakar ba ta kwatanta kaunarsa a zuciyarta abu ya faskara in ba hakuri zata yi ta auresa hakan Nan ba ta koyi so da kaunarsa yadda tayi na Rabiu amma idan tayi hakan shikenan bata da ranar jin dandanon zakin zumar soyayyar da Maryam ta kwadaita mata kenan? Oh oh Allah gani gareka, kayi min zabin abinda yafi zama alkhairi a rayuwata. Wasa-wasa watanni sun Mika sunyi nisa har ana neman hada shekara da rasuwar mijinta, amma ba amo ba labari ba alamar zata fidda miji cikin masoyanta da suka kasa rabuwa da ita suyi fushi. . Abdul karami har ya shiga nursery, mamansa kuwa ta Kara sadaukar da kanta ne a aikinta, lokacinta na yaran da take koyarwa ne Wanda Allah ya dorawa lalurori iri daban-daban, kullum tausayinsu karuwa yake, kusancinta dasu ya fiye mata komi don haka ta manta shaf da wani batun aure, tunanin zama da wani ya shafe ya goge a ranta. 04/09/2020, 23:29 - Anty saliha: ...RAHIMA..doc by Jami 13 Akai-akai take zuwa gaida tsohuwar sarakuwarta, duk sati ta Kai Abdul yai mata hutun karshen mako, su da kansu dangin uban suka raba yadda yaron zai rinka ziyaryar ko'ina don ya saba da sauran 'yanuwansa. Ko yaushe Rahima ta ziyarci Hajiya saita yi mata fadan kin yin aure, a gida ma tun iyayen nayi sun gaji sun saka mata ido, yaruwarta Maryam ma na irin nata kokarin don ta ciwo kanta su zama matan abokai duk tayi kunnin uwar shegu. Wannan satin Abdul gidan takwaransa yai weekend, ya daukosa ya maido gidan Hjy don mamansa nan zata taho daukarsa kasancewar Zuwaira bata gari. Tunda suka shiga gidan Abdul ke manne da Haseeb yaki yarda ya sauka daga cinyarsa balle yaje wajen kakar Saida tayi masa dabara aka samu da kyar mairo mai aikinta ta goyasa suka nufi wake sannan ya gaisa da mahaifiyarta.. Hajiya tace "Yaron Nan ya shaku da Kai Kwarai da gaske.".. Ya amsa "Haka kowa ke Fadi, gashi yana jin maganata ko rigimar banzan sa ya fara yaki sauraren kowa Ina masa magana zai daina." Tayi shuru cikin tunani kafin ta furta "Daman Rabi'u yace danka ne dole yaji maganarka." Yace "Dalili kenan da in har ya gama nursery mamansa bata yi aure ba zan karbi dans kawai tunda daman an bar mata shi bisa yarjejeniyar zamu amshi abinmu ne idan zata sake aure to tunda ba alamun hakan gara mu karbeshi kawai." Ta zaro ido " Zaka tayar mata da hankali, da wanne zata ji, yaron nan shi take gani tana jin sanyi, idan an nuna mata fun karfi a kansa zaku dau hakkin yarinyar Nan." Ya bata fuska "Ai munyi mata Kara Hajiya, Ni ke, 'yanuwanta ita kanta da sauran jamaa sun san haka sai dai in za aki gaskiya." Ta daga masa hannu "Naji, naji meye hujjarka na son amsar sa?" Ya gyara zama "Hujjata ya dawo cikin 'yanuwansa ya zauna gaba days ba a rinka yawo da hankalinsa ba, Kuma ke da kike wannan magana da zaran ita iwar tasa ta sami miji ba dawo mana dashi za a ayi ba?" Ta dade Bata ce dashi komi ba zuwa can tace "Hakane na amince da batunka amma Ina ganin da abinda za ayi a magance wannan matsalar ta bangarenmu da na uwar yaron saurara: Ni a hakikanin gaskiya tunda Allah ya amshi ran danuwanka nike tunanin baka shawarar auren Rahima.... Bai bari ta karisa bs ya buga kirji ya zabura kamar zai tashi tsaye ya koma ya tsugunna jikinsa ba inda baya rawa, ya kama kansa da hannu biyu ya rinka jinjina maganar a ransa, nan take idanunsa suka rikide suka canza launi maimakon farare sol, ya bude baki yai magana kalmar ta kasa fitowa ya koma ya zauna yaraf saboda matukar sanyin da jikinsa yayi sai kace Wanda ya kwana ya yini Yana aikin wahala ba ci ba Sha. Ta dauki tsawon lokaci kafin ta kallesa da kyau tace "Maganar da nai maka na auren ne ya firgita ka har ka fita hayyacinka?" Yaja dogon numfashi ya saki ajiyar zuciya, sannan ya dago Kai a hankali ya kalli mahaifiyarta yace "Hajiya idan ma auren zan kara in rasa wace zan aura sai matar kanina da ya rasu, ki tuna yadda muke dashi fa, idan anyi hakan ba a kyauta ba." Ta danyi murmushi saboda tayi niyyar hada auren nan ikon Allah ne kadai zai hana yuwwarsa. Tace "Ni kuwa a nawa tunanin yadda kuke da danuwan naka ne zaisa ka amince a kulla wannan abu don kaji dadin rike amanar da ya damka maka?" Ya girgiza Kai "Kayya ba sai na kaiga hakan ba duk inda take zanyi kokarin taimaka mata gwargwadon zarafina, yaro kuwa dama namu duk da haka ba Zan tauye mata hakkinta matsayinta na uwa ba dole zamu bata damar kulawa da al'amuran danta a duk lokacin da bukata ta taso." Hjy tasha mur "To ka ga ni shawarar dana yanke kenan kaje kayi nazari, na baka sati guda kacal bayan haka ka taho ka fada min abinda ka yankewa zuciyarka, yi ko tsallake maganata?" Da jin zancenta yasan ba zata kara saurarensa ba,bai hana ya durkusa yana rokonta Allah da Annabinsa ta bar wannan batun da baida ko dadin ji. . Tace " Ka daina yi min magiya, Wai ma tsaya tunda ka girms kasan ciwon kanka na taba tursasaka kayi min abinda nike so ko kuwa na taba baka shawarar da ba kaga amfaninta a rayuwarka ba? Yace "Ah ah! Tace "To kaje ka dawo bayan sati guda Ina saurarenka, na riga na gama maganata." Yayi shiruuu ya rasa me zai sake ce Mata in har zata sauraresa kenan, yafi kowa sanin halin mahaifiyarsa kaifi daya ce ita, idan ta tsaya akan abu babu daga kafar ba ja da baya don haka Kar ma yace zai sake bata baki, ta riga ta kudurtawa ranta sai abinda Allah yayi kenan. 05/09/2020, 12:14 - Anty saliha: ...RAHIMA...doc by jami 14 Hjy Kaltume bata tsaya nan ba, aikawa tayi makarantar da Rahima ke koyarwa tace direba ya daukota yace tana nemanta. Ba a jima ba ya hangeta ta fito tare da wasu malaman bayan an tashi, ya tareta ya durkusa ya gaisheta ta kallesa cikin mamaki "Bala lafiya?" Ya amsa "Lafiya kalau Hajiyar ce ke nemanki da gaggawa." Alamun damuwa ya bayyana a fuskarta, kace kuma lfy? Bata taba min haka ba ka tabbata ba matsala Bala?" Yace "A sanina ba komi." To shikenan mu hanzarta Amma sai mun tsaya in shiga gida in Fadi Kar Umma taga ban dawo da wuri ba su damu.". Yace "Ai tun hanyata ta zuwa na shiga na fadowa Umman uzurun Hajiyar kamar yadda ta umurceni." Jikinta dai yai sanyi, ta shiga sake-saken zucci har suka isa. Ta shiga cikin gidan da sassarfa, ta isko Hajiyar a tsakar gida tana alwala, ta saki ajiyar zuciya don a zatonta ko rashin lafiya ce, Hajiyar taga alamun a firgice take, ta danyi dariya tace "Maraba lale Rahima, yi hakuri 'yan nan ban so firgita ki ba, zo ga buta kiyi alwala." Saboda jin nauyinta tace "Na riga nayi, a zahiri kuwa tana period. Kai tsaye ta shige dakin, Hajiyar ta miko mata kulolun abinci tace "Ci abinci kafin inyi Sallah." Ta zuba abincin amma ta kasa cin ko loma guda sabida tsananin tunani. Ta kosa ta kare adduoin da take yi bayan idar da Sallah. Zuwa wani lokaci ta Kai makura kagara da son jin dalilin nemanta, da kyar ta amsa gaisuwar Mairo data shigo daidai lokacin. Hjy Kaltume ta aje tasbaha bayan shafa adduarta ta juyo tana fuskantar Rahima tare da kallon plate din abinci ta danyi murmushi " Ba ki ci abincin ba lafiya?" "Na koshi ne.' "Ko dai kin razana da sakona ne?" Ta gyada kai "Gaskiya na dan firgita tunda baki taba min irin wannan Kiran ujula ba." "Karki damu alkhairin." Rahima tace " Hajiya meke faruwa?" Hajiya tace "Kafin kiji komi Ina son sanin shin ya kika daukeni lokacin da kike auren marigayi da yanzun?" Tayi wani da fuska "Hjy ban fahimce ki ba." Hajiya tace "Abin nufi wane matsayi kika bani a zuciyarki." Ta saki fuska tace "Baki da wani matsayi a gareni daya wuce na uwa tun a da da Kuma yanzun saboda kin rike tamkar 'yar da kika haifa a cikinki, baki taba nuna min rashin kauna ko na dakika guda ba, akwai lokutta da dama dana kan tuna korafin marigayi kan cewa kamar kin fi sona dashi, na kance don baki da diya mace ce shiyasa kike kaunata amma a zahiri kishin yadda muka shaku yake." Hajiya tace "Alhamdulillah naji dadin wadannan kalamai, Ina so ki sani har gobe ina kaunarki Rahima, kauna fisabilillah irin Wanda Allah ke dasawa mutum, halayenki suka karfafa kaunarki a zuciyata. Itace Kuma tasa nayi tunanin sama miki miji Wanda banyi hakan ba Saida nayi nazari sosai na tabbatar idan Allah ya hada zuciyoyinku anyi auren nan zaku dace da juna matuka. Rahima tayi wani irin gingirin tace " Miji Hajiya? Gaskiya ban shirya sake aure yanzu ba don ban samu Wanda ya kwanta min a rai kamar Rabiu." Hajiya Kaltume tace "Na fahimci haka, wanda na sama miki zai kwanta miki a rai ne idan kuka shaku da juna, ina tabbatar miki zaku sami ingantacciyar rayuwar auren da zai ba kowa sha'awa. Nasan haka ne kuwa saboda sanin halayyanku kusan daya ne, na lakanci ke yarinyace data san ya kamata, kinsan girman na gaba, kina da hakuri da juriya da dauriyyar kowacce irin matsala ta taso miki, kinada tawali'u , kinsan yadda ya dace ki zauna da wanda ke matsayin mijinki cikin ladabi da biyayya, kin iya mutunta mutum cikin kowanne yanayi, kinada tausayi da jin maganar na gaba dake koda abinda zai gaya miki bai miki dadi ba. Rahima ke yarinyace mai yawan ibada, rayuwar duniya bata shagaltar dake barin bautar Ubangijinki ba, kina daure rashi, kiyi farin cikin samu komin kankantarsa, kinada yasan kyauta ba irinta almubazzaranci ba, da wuya inji kin Fadi karya komi rashin gaskiyarki, a yayinda gaskiyar ta zama Miki abin Fadi duk runtsin da kika shiga, baki da kyashi balle hassada ko munafunci. Kin zauna da mijinki damu tsakani da Allah.. Wadannan halayye naki sunzo daidai da namijin da nike so ki aura Rahima, zan iya cewa ma wasu abubuwan sunfi naki inganta kasancewarsa namiji, Kuma ya dandani wahalhalun rayuwa fiye dake amma duk da haka bai gaza ba." Rahima tayi kasake, gaskiya tayi mata yawa, ba shakka Hajiya ta santa tamkar tafin hannunta, lalle ta lakanceta tsaf fiye da yadda ta lakanci kanta, idan kuwa haka halin mutumin yake lalle ta samu abokin rayuwar aure irin Wanda take mafarkin samu tun tasowarta zata Kuma iya zama dashi saboda halayyensa ko bata son sa... Tunanin So da tayi yasa ta juya ta kalli Hajiyar dake kallonta, tayi saurin dukar da Kai kass tace "Hajiya naji bayaninki Kuma nagode sai dai abin tunani, ya ayi kisan shi din Yana son wannan auren hadi yadda kike so?" Tace "Amincewarki kawai nake jira, Ina son ji daga bakinki kin amimce da shi ko Yaya?" Ta Kara sunkuyar da Kai tace "Amincewarki dashi shine nawa Hajiya don nayi imani ba zaki sani hanyar da zan wahala ko yin dana sani ba." Hajiya tace "Alhamdulillah kamar yadda amincewata ya zama naki shima din amincewata shine nasa, Amma kafin a fara wanzar da komi kije kiyi nafila ki karanta istikhara ki roki Allah zabinsa Kan al'amarin kamar na kwanaki bakwai, idan kin gama sai inji daga gareki. Nima zan tayaku, Allah ya taimakemu, ameen." Rahima tace "Wai a Nan garin yake ko danuwanki ne da ban sani ba?" Ta boye murmushinta " Me kike ci na baka na zuba, zaki San ko waye, karewa ma muna fatar kuyi zaman aure tare, kije dai bayan sati dayan zamu fahimci komi da yardar Allah." 05/09/2020, 22:21 - Anty saliha: ...RAHIMA..doc by jami 15 Ta koma gida cike da mamakin Hajiyar, ta zayyanewa Umma dukkan yadda suka yi, Habiba tace "To Allah ya yaji shemu alkhairi ai zaman ya isa haka, muma za muyi adduar, Baffanku ma zaiji dadin labarin nan don da yadda zaiyi da tuni ya aurad dake ga duk wanda ya dace... Kwanaki hudu bayan maganarsu da Hjy Kaltume ta fara sakankancewa sa ikon Allah, Al-Hakeem gwanin hikima da basira. Bayan adduoin data dukufa yi haka kawai take jin wani irin dadi da nishadi a ranta, zuciyarta ta fara kamuwa da kaunar mutumin da labarinsa kawai taji, ko sunansa Bata m sani ba abinda ta manta ta tambayi Hjyr kenan. Shin wanene wannan mutumin da kaunarsa ke neman mamaye mata ilahirin zuciyarta tun kafin suyi ido biyu dashi? Shin wanene mutumin da yake da kwatankwacin halayenta? Wanene wannan mutumin da take rokon Allah dare da Rana cewan ta hadata da irinsa tun tana budurwa? Shun wane irin gwagwarmarya ratuwa ya fuskanta da yasa Hjy ke jinjinawa? Tun kafin ta gansa tausayunsa ya cikata har taji ta matsu ta kosa ta gansa ko hankalinta ya kwanta." Umman tasu ta sade tsaye tana magana bata ji ba har Saida ta buga kofar dakin da karfi tayi firgigit ta dago Kai... "Meke damunki haka na dade tsaye Ina magana baki san Ina yi ba?".. Ta tashi zaune "Umma tunanine kawai ya isheni.... "Kiyi taka tsan-tsan da tunane-tunane nan Rahima, yaro dai ya riga ya rasu, kafin shi maza nawa suka rasu suka nar matansu, ki sahalwa kanki kici gaba da duain Allah ta tabbatar mana da wannan da Hjy tayi batun,itama fa kenan data haifesa ta dangana har itace ke kawo miki wani mijin, don me ba Zaki hakura ba, ko sai kin jawowa kanki wata cutar?"... Ta mike tsaf tace "Umma naji na daina, bari in shirya inje gidan Maryam, idan kunji shiru can Zan kwana ".. Umma tace "Shine nazo in tambayeki zaki biya ki dauki Abdul ne ku tafi tare?" Ta girgiza Kai " A kyalesa can Unma, damunmu za suyi idan suka hadu da Walida.. "Kuma fa gara ya saba da zaman can din ku rinka nesa da juna Kar ayi aurenku ya ishenmu da rigima." Ta kalleta "Kaji Umma da wani zance, sai kace an sa ranar auren daga magana, bamu ko San juna ba fa, idan muka hadu abin bai yuwwu ba fa?" Tace "Ai Ni Ina ji a jikina wannan auren an gama daura shi da iznin Ubangiji.". Haka kawai taji sanyi a ranta ko meyasa oho.. Mhmmm ta suri Jakarta ta saka after dress ta lullubeta kanta suka yi sallama ta nufi gidan 'yaruwa... Bata sami damar ba 'yaruwar nata labarin labarin dake cinta ba saboda ta taras da gidan nasu a hargitse, itada Uwargidanta basa ko ga maciji, karin abin haushi harda raba Kan 'ya'yansu kowa harkarta take da diyanta. Ran Rahima ya baci,hankalinta yai matukar tashi, bata saurari Maryam don ita ta dorawa lefin abubuwan dake faruwa. Maryam tace "Banyi tsammanin zaki ki fahimta ta ba Rahima, ki duba irin bautar dana yiwa matar Nan da yayanta tun zuwana gidannan tun kafin in haihu na kula da yaranta, Ina bata girmanta, yanzu kuwa na gaji don shiru ba tsoro bane gudun fitina nike yi, yanzun kuwa ban damu ba aje ayi tayi idan tace kule zance cas! Ba abinda zata nuna min, idan tana takama da miji ne nima dashi nike, idan yarane nima ina dasu to sai me? Haka siddan mace ta isheni ta gallabeni tamkar ita ta aje Ni? "Hhmmmm inji Rahima "Maryam don Allah numfasa ki saurareni da kyau, ya za ayi ki taho ki taras da mace da mijinta da yara kice zaki nuna mata iko? Mijinta fa kika aure... "Don na auri mijinta sai me, don ita kadai aka halilto shi ne, mijin mace hudu yake, don me idan ta yayo shararta bata zubewa a kansa sai nawa? To na gaji da rainin wayo, ya isa haka." Rahima tace "Ban ce bata da irin nata laifin ba don bai yiwwa ace koda yaushe mutum guda ne ke da laifi da duk magana ta tashi, dole ace tanada irin nata problem, kawai so nike ki fahimci bai kamata ki biye mata duk ku haukace koma ince ku kafirce gaba daya ba, haba 'yaruwa a matsayinki na musulma ki tsiri gaba da 'yaruwarki musulma, makwabciyarki Kuma?" Ta kada Kai "To ya kike son inyi, ita ta fara, sau nawa Ina gaisheta tana shareni tun ina daurewa nace mu zuba mu gani, ko abinci na aika mata bata ci sai ta maido min ta wanke tukunya ta dora wani ta ci, naga bai dau wani mataki ba bayan ya gani da idonsa, nace tunda haka ne bari nima in maida martani tunda ni ba shegiya bace da ubana, ta hana yaranta shigowa dakina balle suyi wasa da yanuwansu, tun Ina damuwa na dake na fara ramuwar gayya Wanda tafi gayyar zafi inji hausawa." "Kash! Inji Rahima, da baki biye mata ba, me zaisa ki bar shaidan ya samu gurbin gina katangarsa a zuciyarki, don me ba za kiyi aiki da ilmin da Allah ya hore miki ba ki nuna mata abubuwan da take yi tsagwaron jahilici ne?" Ta tabe baki "Kishi da jahilar mace ko masifa, duk yadda kika so ki fahimtar da ita ba zata taba ganewa ba, kullum inda kika dosa daban inda ta dosa daban, kina gabas tana yamma, to yaushe zan bata lokacina a aikin banza." Rahima tace "Da kike kiranta jahila ba gara ita dake ba? Laifinta ragagge ne don dama bata da sanin, ke kuwa kin sani kin take sanin laifi biyu kenan, to wai shi maigidan bai san abubuwan dake faruwa cikin gidansa tsakanin iyalinsa ba?" "Kwarai ya sani Mana, cewa yayi in dominsa muke muje mu kashe kanmu ba ruwansa tunda yai kokarin sulhunta mu Abu ya faskara." Taja tsaki "You see, ya maisheku mahaukata wadanda basu San ciwon kansu ba, tun anan bai isa ku hankalto ba? Shi da kuke kishin dominsa bai damu ba Wai ma in mutuwa za kuyi ku mutu, eh lalle yace muku haka, in Kun kashe kanku ai bashi kuka yiwa asara ba illa iyaye, 'ya'ya da 'yanuwanku, baida asara Kona miyaun barci iyaka ya auri wasu ya zuba a rufe chapter dinku ku bar 'ya'ya da abun kunya." Maryam ta juyo "To naji ustaziyar zamani, zanyi nazari in kwatanta in gani, idan da canji in ci gaba, idan babu riba Zan watsar mu ci gaba da zaman doya da manjan don babu macen da zata takani in kyale." Rahima tace" Allah ya ganar damu baki daya, Kinga da na taho da niyyar kwana amma na fasa don ba zan iya zama gidan da ake gaba ba " Nan da nan ta marairaice "Don Allah yi hakuri na bari, muyi kwanciyarmu.". Ta nufi kofa "Ba zan tabbatar da kin bari ba sai munje har dakinta na gaisheta tukunna, mu dawo in baki labarin dalilin zuwana." Da kyar ta amince suka tafi, suka sallama ta amsa,suka shiga ciki. Tayi mamakin ganin 'yaruwar kishiyarta da suka shafe sati biyu suna gaba da juna, da ita kanta. Rahima ta gaisheta tamkar bata san me ke faruwa ba ta amsa, suka Dan jima suna kame-kamen magana, zuwa can Nafi'u yaron da Maryam ke goyo ya nufi gaban Tv ta ya dauko wata flower vase na glass, uwar tayi saurin tashi ta amsa ta bubbugeshi. Hjy Suwaiba ta kalleta "Meye na dukan wannan Dan yaron kinada hankali kuwa? Ta amsa "Ba kiga barnar da zai yi bane?". Hjy Suwaiba ta dauki vase din ta sake mikawa yaron "Idan ya fasa naki ne? Maryam tayi shiru Rahima tayi murmushi "Nima shi na gani yaro da kayan uwarsa.". Hjy Suwaiba tace "Kila so take in bar mata danta ko daman Walida ce tawa, ta rike kayan barnarta kin ganshi mummuna." Maryam ta kalli Rahima "Kinji ta ko? Wallahi tunda aka haifeshi take tsangwamarsa Wai Walida ta fishi kyau ko Ina kyaun da katon hanci oho._ Hajiya Suwaiba tayi dariya " munji ba komu muma da kayan gyara, naki a sa masa 'yankunne da janbaki mu gani." "Ah ah Hjy gaskiya cun fuskar tayi yawa, ki dai rike taki mu rike namu." A haka suka ci gaba da wasa da dariya har kusan magriba sannan suka koma dakin Maryam suka yi Sallah. Suna idarwa Hjy Suwaiba ta aiko musu da kulolin abinci wai a kawowa Rahima, da gani abincin yafi karfin ita kadai dole suka ci tare da Maryam din ita ta fasa dora tukunya. Rahima ta kalleta tace " Don Allah da kika shiga dakinta, kikai Mata magana gashi har kinci abincinta me ya rage a jikinki? Inda za a bude Miki file dinki yau kiga dimbin ladan da kika samu da ba zaki yards ki kara yin gaba ba koda wasa." "Wallahi Kuma Nima sai naji wani irin dadi a Raina, duk kuncin da nike ji a zuciyata ya yaye na yarda sai kaso abu ya dameka yake damunka din.".. Rahima tace abinda har yanzun mu mata bamu gane ba kenan, mu ke creating ma kanmu problems din da zasu dawo su dame mu, namiji ba ruwansa, sai un har kunyi dace da Mai kula ne zai fahimci halinda kuke cikin, wani ko ya gani ba abinda ya damesa tunda yawancinsu sunfi son haka, su tara Mata cikin gida ayita adawa a kansu, ya fito Yana jin dadi da hura hanci ya rinka ikrarin sabida tsananin son da kuke masa kishi ya hanaku zaman lafiya. Wani shaidanin zaman lafiyar ce bai so, yana ganin kun hada kai sai ya kasa sukuni ya shiga zargi da fargaban shifa sai yadda kuka yi dashi kenan domin da wuya daya ta yarda a ci amanar guda shi kuwa bai son hakan, yafi son ya zama bakin ganga, ya buga nan, ya Fadi gaibu can, yai munafunci a nan sai kunada kyakkyawar kula zaku gane in ba haka ba sai kuga kowacce ta fito tana kuri da fankamar ita yafi so. Idan anyi dace da irin mazan da suka san ciwon kansu sai kiga su zaman lafiyar suke matukar bukata a gidajensu, idan Allah yasa ya dace da matan kwarai sai sai ya kula dasu matuka ya rinka kyautata musu har kiji danginsa na fadin sun mallakeshi sun gama Mana dashi alhalin jin dadin zaman lafiya da kwanciyar hankalin da yake samu dasu ya haifar da hakan. Kin ganni nan Maryam bana shakkar zama da kowacce irin mace Allsh zai hadani da ita matsayin kishiya." Ta gatsina baki "Karki cika baki Rahima, me kika sani game da zama da kishiya, kowacce mace fa da nata salon munafunci da kisisinar data kware, idan an debe masu shige-shigen gidan bokaye da malamai don wata ba zata zauna dake da bakin hura wuta kadai ayi kishi ba." Tayi murmushi "Aunty Maryam kenan ai ba wani cika baki, in har hakane Kuma Ina iya ce miki yes na cika baki ne domin nima da nawa baiwar da Allah yai min, ba wani abu bane da ya wuce kakkarfar madogora." Ta kada Kai "Ko Zan San wane irin madogara ne?" Ta girgiza Kai "Nima ki bini bashi zuwa nan gaba in har Allah ya kaddareni da auren kiga matsayins zamana a gidan mijin da wajen shi kansa mijin tukunna, yanzun dai muyi sallar isha'i ki bani amsar tambayata ta tuntuni don Ina jin ga wannan karon na fada kogin nan na so da kauna sai dai ko za ku iya tsamo ni?" 05/09/2020, 22:48 - Anty saliha: ..RAHIMA..doc by jami 15 Ta koma gida cike da mamakin Hajiyar, ta zayyanewa Umma dukkan yadda suka yi, Habiba tace "To Allah ya yaji shemu alkhairi ai zaman ya isa haka, muma za muyi adduar, Baffanku ma zaiji dadin labarin nan don da yadda zaiyi da tuni ya aurad dake ga duk wanda ya dace... Kwanaki hudu bayan maganarsu da Hjy Kaltume ta fara sakankancewa sa ikon Allah, Al-Hakeem gwanin hikima da basira. Bayan adduoin data dukufa yi haka kawai take jin wani irin dadi da nishadi a ranta, zuciyarta ta fara kamuwa da kaunar mutumin da labarinsa kawai taji, ko sunansa Bata m sani ba abinda ta manta ta tambayi Hjyr kenan. Shin wanene wannan mutumin da kaunarsa ke neman mamaye mata ilahirin zuciyarta tun kafin suyi ido biyu dashi? Shin wanene mutumin da yake da kwatankwacin halayenta? Wanene wannan mutumin da take rokon Allah dare da Rana cewan ta hadata da irinsa tun tana budurwa? Shun wane irin gwagwarmarya ratuwa ya fuskanta da yasa Hjy ke jinjinawa? Tun kafin ta gansa tausayunsa ya cikata har taji ta matsu ta kosa ta gansa ko hankalinta ya kwanta." Umman tasu ta sade tsaye tana magana bata ji ba har Saida ta buga kofar dakin da karfi tayi firgigit ta dago Kai... "Meke damunki haka na dade tsaye Ina magana baki san Ina yi ba?".. Ta tashi zaune "Umma tunanine kawai ya isheni.... "Kiyi taka tsan-tsan da tunane-tunane nan Rahima, yaro dai ya riga ya rasu, kafin shi maza nawa suka rasu suka nar matansu, ki sahalwa kanki kici gaba da duain Allah ta tabbatar mana da wannan da Hjy tayi batun,itama fa kenan data haifesa ta dangana har itace ke kawo miki wani mijin, don me ba Zaki hakura ba, ko sai kin jawowa kanki wata cutar?"... Ta mike tsaf tace "Umma naji na daina, bari in shirya inje gidan Maryam, idan kunji shiru can Zan kwana ".. Umma tace "Shine nazo in tambayeki zaki biya ki dauki Abdul ne ku tafi tare?" Ta girgiza Kai " A kyalesa can Unma, damunmu za suyi idan suka hadu da Walida.. "Kuma fa gara ya saba da zaman can din ku rinka nesa da juna Kar ayi aurenku ya ishenmu da rigima." Ta kalleta "Kaji Umma da wani zance, sai kace an sa ranar auren daga magana, bamu ko San juna ba fa, idan muka hadu abin bai yuwwu ba fa?" Tace "Ai Ni Ina ji a jikina wannan auren an gama daura shi da iznin Ubangiji.". Haka kawai taji sanyi a ranta ko meyasa oho.. Mhmmm ta suri Jakarta ta saka after dress ta lullubeta kanta suka yi sallama ta nufi gidan 'yaruwa... Bata sami damar ba 'yaruwar nata labarin labarin dake cinta ba saboda ta taras da gidan nasu a hargitse, itada Uwargidanta basa ko ga maciji, karin abin haushi harda raba Kan 'ya'yansu kowa harkarta take da diyanta. Ran Rahima ya baci,hankalinta yai matukar tashi, bata saurari Maryam don ita ta dorawa lefin abubuwan dake faruwa. Maryam tace "Banyi tsammanin zaki ki fahimta ta ba Rahima, ki duba irin bautar dana yiwa matar Nan da yayanta tun zuwana gidannan tun kafin in haihu na kula da yaranta, Ina bata girmanta, yanzu kuwa na gaji don shiru ba tsoro bane gudun fitina nike yi, yanzun kuwa ban damu ba aje ayi tayi idan tace kule zance cas! Ba abinda zata nuna min, idan tana takama da miji ne nima dashi nike, idan yarane nima ina dasu to sai me? Haka siddan mace ta isheni ta gallabeni tamkar ita ta aje Ni? "Hhmmmm inji Rahima "Maryam don Allah numfasa ki saurareni da kyau, ya za ayi ki taho ki taras da mace da mijinta da yara kice zaki nuna mata iko? Mijinta fa kika aure... "Don na auri mijinta sai me, don ita kadai aka halilto shi ne, mijin mace hudu yake, don me idan ta yayo shararta bata zubewa a kansa sai nawa? To na gaji da rainin wayo, ya isa haka." Rahima tace "Ban ce bata da irin nata laifin ba don bai yiwwa ace koda yaushe mutum guda ne ke da laifi da duk magana ta tashi, dole ace tanada irin nata problem, kawai so nike ki fahimci bai kamata ki biye mata duk ku haukace koma ince ku kafirce gaba daya ba, haba 'yaruwa a matsayinki na musulma ki tsiri gaba da 'yaruwarki musulma, makwabciyarki Kuma?" Ta kada Kai "To ya kike son inyi, ita ta fara, sau nawa Ina gaisheta tana shareni tun ina daurewa nace mu zuba mu gani, ko abinci na aika mata bata ci sai ta maido min ta wanke tukunya ta dora wani ta ci, naga bai dau wani mataki ba bayan ya gani da idonsa, nace tunda haka ne bari nima in maida martani tunda ni ba shegiya bace da ubana, ta hana yaranta shigowa dakina balle suyi wasa da yanuwansu, tun Ina damuwa na dake na fara ramuwar gayya Wanda tafi gayyar zafi inji hausawa." "Kash! Inji Rahima, da baki biye mata ba, me zaisa ki bar shaidan ya samu gurbin gina katangarsa a zuciyarki, don me ba za kiyi aiki da ilmin da Allah ya hore miki ba ki nuna mata abubuwan da take yi tsagwaron jahilici ne?" Ta tabe baki "Kishi da jahilar mace ko masifa, duk yadda kika so ki fahimtar da ita ba zata taba ganewa ba, kullum inda kika dosa daban inda ta dosa daban, kina gabas tana yamma, to yaushe zan bata lokacina a aikin banza." Rahima tace "Da kike kiranta jahila ba gara ita dake ba? Laifinta ragagge ne don dama bata da sanin, ke kuwa kin sani kin take sanin laifi biyu kenan, to wai shi maigidan bai san abubuwan dake faruwa cikin gidansa tsakanin iyalinsa ba?" "Kwarai ya sani Mana, cewa yayi in dominsa muke muje mu kashe kanmu ba ruwansa tunda yai kokarin sulhunta mu Abu ya faskara." Taja tsaki "You see, ya maisheku mahaukata wadanda basu San ciwon kansu ba, tun anan bai isa ku hankalto ba? Shi da kuke kishin dominsa bai damu ba Wai ma in mutuwa za kuyi ku mutu, eh lalle yace muku haka, in Kun kashe kanku ai bashi kuka yiwa asara ba illa iyaye, 'ya'ya da 'yanuwanku, baida asara Kona miyaun barci iyaka ya auri wasu ya zuba a rufe chapter dinku ku bar 'ya'ya da abun kunya." Maryam ta juyo "To naji ustaziyar zamani, zanyi nazari in kwatanta in gani, idan da canji in ci gaba, idan babu riba Zan watsar mu ci gaba da zaman doya da manjan don babu macen da zata takani in kyale." Rahima tace" Allah ya ganar damu baki daya, Kinga da na taho da niyyar kwana amma na fasa don ba zan iya zama gidan da ake gaba ba " Nan da nan ta marairaice "Don Allah yi hakuri na bari, muyi kwanciyarmu.". Ta nufi kofa "Ba zan tabbatar da kin bari ba sai munje har dakinta na gaisheta tukunna, mu dawo in baki labarin dalilin zuwana." Da kyar ta amince suka tafi, suka sallama ta amsa,suka shiga ciki. Tayi mamakin ganin 'yaruwar kishiyarta da suka shafe sati biyu suna gaba da juna, da ita kanta. Rahima ta gaisheta tamkar bata san me ke faruwa ba ta amsa, suka Dan jima suna kame-kamen magana, zuwa can Nafi'u yaron da Maryam ke goyo ya nufi gaban Tv ta ya dauko wata flower vase na glass, uwar tayi saurin tashi ta amsa ta bubbugeshi. Hjy Suwaiba ta kalleta "Meye na dukan wannan Dan yaron kinada hankali kuwa? Ta amsa "Ba kiga barnar da zai yi bane?". Hjy Suwaiba ta dauki vase din ta sake mikawa yaron "Idan ya fasa naki ne? Maryam tayi shiru Rahima tayi murmushi "Nima shi na gani yaro da kayan uwarsa.". Hjy Suwaiba tace "Kila so take in bar mata danta ko daman Walida ce tawa, ta rike kayan barnarta kin ganshi mummuna." Maryam ta kalli Rahima "Kinji ta ko? Wallahi tunda aka haifeshi take tsangwamarsa Wai Walida ta fishi kyau ko Ina kyaun da katon hanci oho._ Hajiya Suwaiba tayi dariya " munji ba komu muma da kayan gyara, naki a sa masa 'yankunne da janbaki mu gani." "Ah ah Hjy gaskiya cun fuskar tayi yawa, ki dai rike taki mu rike namu." A haka suka ci gaba da wasa da dariya har kusan magriba sannan suka koma dakin Maryam suka yi Sallah. Suna idarwa Hjy Suwaiba ta aiko musu da kulolin abinci wai a kawowa Rahima, da gani abincin yafi karfin ita kadai dole suka ci tare da Maryam din ita ta fasa dora tukunya. Rahima ta kalleta tace " Don Allah da kika shiga dakinta, kikai Mata magana gashi har kinci abincinta me ya rage a jikinki? Inda za a bude Miki file dinki yau kiga dimbin ladan da kika samu da ba zaki yards ki kara yin gaba ba koda wasa." "Wallahi Kuma Nima sai naji wani irin dadi a Raina, duk kuncin da nike ji a zuciyata ya yaye na yarda sai kaso abu ya dameka yake damunka din.".. Rahima tace abinda har yanzun mu mata bamu gane ba kenan, mu ke creating ma kanmu problems din da zasu dawo su dame mu, namiji ba ruwansa, sai un har kunyi dace da Mai kula ne zai fahimci halinda kuke cikin, wani ko ya gani ba abinda ya damesa tunda yawancinsu sunfi son haka, su tara Mata cikin gida ayita adawa a kansu, ya fito Yana jin dadi da hura hanci ya rinka ikrarin sabida tsananin son da kuke masa kishi ya hanaku zaman lafiya. Wani shaidanin zaman lafiyar ce bai so, yana ganin kun hada kai sai ya kasa sukuni ya shiga zargi da fargaban shifa sai yadda kuka yi dashi kenan domin da wuya daya ta yarda a ci amanar guda shi kuwa bai son hakan, yafi son ya zama bakin ganga, ya buga nan, ya Fadi gaibu can, yai munafunci a nan sai kunada kyakkyawar kula zaku gane in ba haka ba sai kuga kowacce ta fito tana kuri da fankamar ita yafi so. Idan anyi dace da irin mazan da suka san ciwon kansu sai kiga su zaman lafiyar suke matukar bukata a gidajensu, idan Allah yasa ya dace da matan kwarai sai sai ya kula dasu matuka ya rinka kyautata musu har kiji danginsa na fadin sun mallakeshi sun gama Mana dashi alhalin jin dadin zaman lafiya da kwanciyar hankalin da yake samu dasu ya haifar da hakan. Kin ganni nan Maryam bana shakkar zama da kowacce irin mace Allsh zai hadani da ita matsayin kishiya." Ta gatsina baki "Karki cika baki Rahima, me kika sani game da zama da kishiya, kowacce mace fa da nata salon munafunci da kisisinar data kware, idan an debe masu shige-shigen gidan bokaye da malamai don wata ba zata zauna dake da bakin hura wuta kadai ayi kishi ba." Tayi murmushi "Aunty Maryam kenan ai ba wani cika baki, in har hakane Kuma Ina iya ce miki yes na cika baki ne domin nima da nawa baiwar da Allah yai min, ba wani abu bane da ya wuce kakkarfar madogora." Ta kada Kai "Ko Zan San wane irin madogara ne?" Ta girgiza Kai "Nima ki bini bashi zuwa nan gaba in har Allah ya kaddareni da auren kiga matsayins zamana a gidan mijin da wajen shi kansa mijin tukunna, yanzun dai muyi sallar isha'i ki bani amsar tambayata ta tuntuni don Ina jin ga wannan karon na fada kogin nan na so da kauna sai dai ko za ku iya tsamo ni?" 06/09/2020, 19:35 - Anty saliha: ...RAHIMA...doc by jami 16 Karfe tara na dare sun nutsa cikin hira, har Hjy Suwaiba ta shigo neman shawara wajen Rahima, sun tattauna kan problem din yaron kanwarta data haifa kurma, tayi musu sallama ta tafi da yake Alh a dakinta yake. Har zasu rufe kofa, Alh. Abbas ya shigo suka gaisa da Rahima kana ya roketa data fita su gaisa da abokinsa da har lokacin yana magiyar son aurenta. Ta shiga falon ta sallama fuska a murtuke ta gaisheshi, ya amsa yaci gaba da 'yan dabarunsu na maza don ta saki ranta. Rahima ta zauna kamar wata mutum-mutumi,ta rinka mamakin lokacin da ta rayawa zuciyarta amincewa ta auri Alh. Abbas, Lalle da tayi wauta, yes a da can da bata San muhimmancin soyayya ba zata iya zama dashi but a yanzun Kam sai dai yayi hakuri, soyayyar wani ya riga ya fara shiga zucciyarta. Wani wa? Ta tambayi kanta, hhmmm wannan wauta nata da yawa yake, to Wai why take jin son bawan Allah nan da aka mata maganarsa? Alh Suraj ya gaji ya gyara zama tumbinsa ya Kara bayyana cikin babbar rigarsa yace "Rahima ko don nace ba Zan amince kici gaba da aiki bane yasa ba Kya ra'ayina? Idan wannan ne na canza shawara wallahi, na amince kici gaba da aikinki, gidanki Kuma daban zan aje ki " Ta gyada Kai "Ko kusa Kar tunaninka ya Kai can, aure ai nufin Allah ne, idan ya kaddaro ba makawa, mu dai ci gaba da adduar zabinsa." Yace "Lalle kin cika 'yar boko, Baki ce eh ko ah ah ba duk da na fahimci komi, duk mai hankali zai gane inda kika dosa, sai dai na hakura, ban Kuma ji zafi ba saboda baki nuna kwadayin abin hannuna ba, nagode Zan tayaki addua, Ina rokon idan lokacin auren ta taho a kawo mun kati da goron gayyata, Zan m bada gudumuwata matsayin yayan amarya.".. Tace "Godiya nike sosai Allah saka da khairan." Yace "Ba komi Rahima." Goma da mintoci har Maryam ta fara barci Rahima ta tashe ta "Barci tun yanzun?" "Yes tunda ranar hutun kenan da Alhajin ba nan yake ba." "Kina nufun idan yana nan ba Kya hutawan?" Ta amsa "kusan hakan ne kina wasa da Alhajin nan da kike gani, wallahi duk ta sangarce, daidai da spoon bai iya dauka da hannunsa ya Kai baki idan ina kusa." ."Su soyayya masu gari." Maryam ta gyara kwancita "Karki zargeni, ke din wa yasan abunsa za kiyi nan gaba, ya kuka kare da Alh Suraj?" Rahima ta sanya rigar barcinta kafin ta amsa "Na fada masa gaskiya yai accepting wai sai Kun Kai masa Iv." Maryam tace "Ko nifa bana amince dashi bane just tsokanarki nike da naga baki da niyyar fidda kowa, yanzun shi Wanda Hajiyar tayi magana ne a fagen?" Wani irin murmushi da farin cikine suka bayyana a fuskarta, Maryam ta daki kafadarta da matashi tace "Lalle wannan ya samu karbuwa a zuciyarki, fada mini ya kike ji?" Saida ta kwanta ta tasa kafadarta da matashi tace "Za kiyi mamaki Yaruwa domin nima cikinsa nike, ashe mutum Kan so Wanda bai taba gani ba, ni fa ko sunansa ban sani ba, labarinsa ma not in details naji amma na kagu na kosa in gansa inji yaya zanji ranar dana fara ganinsa?" Tayi dariya "To ya zaki kwatanta abubuwan da kike ji yanzun da wanda kika ji game da marigayi." Ta tashi ta zauna "Ai sun Sha banban 'yaruwa, son Rabiu a hankali ya riga shigata kwatankwacin mutum ta dora ruwan zafi bisa wuta, a hankali ya fara dumi, ya kai ga zafi har ya nuna alamun tafasa sai wutar ta mutu, to yadda ya fara zafi hakan ya rinka hucewa yana sanyi a hankali har ya zamto yanzun na hakura, dana tunasa adduar samun rahama nake ci gaba da yi masa kullum, wannan kuwa gaba daya ruwan ya dau zafi, kafin in ankara har ya tafaso ya fantsama koina, zuciyata na kuna, babban abinda ke firgitani addua nike lamarin na kara tsanani, ko yanzu ji nike kamar in rufe ido in gansa a gabana don inga wane irin mutum ne da yai saurin raunana min zuciya?" Maryam ta gyara "Tirkashi! Babbar magana, Lalle lokaci yayi da ya dace in baki amsar tambayarki akan menene so? To a iya fahimtata soyayya itace ni'imar mafi daukaka da Ubangiji yaiwa bayinsa baiwarsa, soyayya itace zuciyoyi dunkule ko a cure waje guda, abin nufi idan mutum yaso wani ko wata son nan kesa ko yaushe a kasance cikin tunanin masoyi, rashin damuwa da kowa sai shi/ita, mutum yakan zama bai jin son ji da ganin kowa sai masoyi kamar yadda kika kasance a halin yanzun. Ba abinda so bai haifarwa, so na sa mutum yai hauka ya zauce, idan zuciyar bata samu abinda take so ba ta Kan fita hayyacinta, tayi rauni wani har sai an hada da addua kafin a sami komawa normal. So kansa mutum yanke hukuncin da bai Dana sani matukar ya shafi masoyin, a cikin lamarin so na hakika babu shakka, ba munafunci ba yaudara, ba karya balle zargi, so nasa masoyi tsananta addua ga Wanda yake so ko da sani ko basa saninsa ba. Mutum Kan gane ya kamu da son wani/wata ce ta faduwar gaba a duk lokacinda aka ambaci sunan masoyi, ko gani a zahiri, hoto ko murya. Zaki yawaita son ambatonsa ko son kiji ana labarinsa ko hirarsa, zaki rinka jin son sirrinsa maana halinda yake ciki, jin dadin zancensa, tausayi, fadar gaskiya, nisantar karya in har son na gaskiya ne, haka nan zaki rinka yaba kyautarsa komin kankantarsa da son kema kiyi masa alkhairin komin yawansa, zaki so ki kula da al'amurransu ko yaushe, sannan uwa uba akwai kishi tsakanin masoya na gaskiya but ba irin kishin nan Mai haifar da zargi ba saboda da zaran Kun amince da so da kauna tsakaninku, girmamawa, yarda da aminci ne za suyi tasiri a zukatanku. Ki kula ba kowanne so ne na hakika ba, majority mu kanyi kuskuren fassara shaawa da kalmar so, irin sa za kiga ko an Kai ga aure lokaci kalilan an fara samun problem musamman idan an riga an gusar da sha'awar, hakuri da juna sai yai karanci saboda ba a gina zaman kan tubalin so da kauna na gaskiya ba. Masoya na hakika Kan jure komi don su zauna da juna. Maryam ta numfasa ta kalli Rahima kina fahimta kuwa?" Ta amsa "kwarai kuwa, karance-karancenki ya amfana ta wannan bangaren, kinji bayaninki kamar wata marubuciya?" Tace "Da kenan dana rinka mafarkin zama daya daga cikinsu.. Rahima tace "Ko yanzun kina iya farawa dauko alkalami da takarda ki gani, gashi kina tsaro min zance kamar kina karantawa ba?" "Rufan asiri don Allah, ai na kwatanta naga ba ci dole na hakura, nan na Kara yarda da batun wani malaminmu cewa rubutu baiwa ce, duk Wanda Allsh yaiwa baiwar hikima da basira yaita gode masa kullum domin a cewarsa koda mutum ya sauke kundin karatu ba lale ya iya rubutu ba, don sai in Allah ya bashi hikimar ne zai rubuta a karanta a fahimta har a sami darasi ciki a amfana, Kinga shiga hurumin da Allah bai kaddaro maka bama shishshigi ne da karanbani in dai ba so kike in rinka satar basirar wasu ba." "Ah ah a Kan me, zauna matsayin da Allah ya aje ki,in kinyi hakan ma ai baki kyautawa kanki ba ko?" Maryam ta kyalkyace da dariya "Ban ma ja da nisa ba kin sani, dana gwada naga bai yuwwa bane na hakura, na dai ci gaba da saye Ina karantawa Ina karuwa.... "Karuwa ta wani fannin ba, wani bangaren kam karatun kawai kike don jin dadin labari amma ba Kya daukar darasin komi. Da kina dauka da baki biyewa Hjy Siwaiba kunyi gaba ba, da baki bi nata Kun raba kan yaranku ba, zumunci fa kenan kuke neman yankewa tsakaninsu alhalin Ubangiji yace Duk Wanda ya yanke zumunci bai tare dashi gobe kiyoma, ban da haka, mijin Nan naku fa na iya mutuwa ya barku kowa ta kama gabanta zaman tsakaninku ya farraka, amma yaranku dole suyi zumunci da juna sabili da jininsu daya, ko Allah ya karbi ran daya daga cikinku takalihun yaran ya koma hannun dayanku dole, ko Kuma ma ya kasheku gaba dayanku, mijin naku ya auro wasu su o suci gajiyar yaran da kuke tinkahon Kun haifa, kinsan dai ba yadda Allah bai iya juya lamarinsa ba don haka ake son mu kasance masu hangen nesa, idan ka ciza ka hura, idan kace zaka biyewa zuciya sai ya kaimu ta baro tunda batavda Kashi, shyasa ake son mu rinka adduar Allah yasa mufi karfinta, Kar shaidan ya rinjayeta, ya karfafa mana imaninmu, Ni da zanga dayan marubutanmu ko dana nunaki cikin days daga cikin makarantarsu amma masu karatu suji dadin labari kawai ba daukar darasi balle ku amfana." Ta bude baki "Tafdijan Rahima yau kin gama dani tsaf... "No ba haka bane 'yaruwa, wajibine in taroki idan naga Zaki ksuce hanya in fada miki gaskiya komin dacinta, marubutan fa suna yi don gyaran tarbiyyarmu dana zuriyyarmu don al'ummanmu su samu nagarta mu gyara rayuwar duniya dana lahira." Maryam tayi kasake tana saurarenta, yes Rahima gaskiya take fada mata ba karya ko kadan, Ina amfanin badi ba rai? Wajibi ta taho ta gyara halinta dana zamantakewarta da abokiyar zamanta ko tace makwabciyar ta inji Rahima,ko bata kyautata mata don komi ba tayi don samun ladan, shin sai nawa ma wani lalura ke tasowa daya daga cikinsu Wanda suke takamar shi ya ajiyesun bai nan bai kusa balle ya magance musu? Su jawa suka taimaki juna musamman lalurar rashin lafiya maigidan na can bai ma sani ba sai ya dawo yaji labari? Idan har Ubangiji zai jarabci bawansa ba mu san ta hanyar da jarabawar zata zo mana ba kuwa ya dace mu saduda mu zauna lafiya da juna muyi hakuri tunda ba wace ke zaune kan wata, babu mai korar wata sai in kaddara ta gitta Wanda ba a fata, kowacce da halinta take zaune kota bangaren mijin ne, to wahalar da Kai na menene? Me zai hana suyi hakuri da juna har mai hadawa ya raba, ko tunanin mutuwa ya isa katsewa duk mai imani hanzari, rayuwar guda nawa take mutum ya tsaya Yana batawa kansa lokaci, duniyar guda nawa take, dubi yadda Allah ya dauke Rabiu farad daya aka raba Rahima da mijin da suke zaune lafiya, yaronta ya shiga maraici ko shi bai isa bawa tsoron Allah ba? Wannan duniyar da ba matabbata ba? Hawaye suka rinka gangarowa zuwa kuncinta. Rahima ta gani ta gigizata cikin damuwa "Lafiya kuwa?" "Hawayen godiyar Allah ne da ya kubutar dani ya ganar dani ya hana min biyewa sharrin zuciya, wallahi ba domin zuwanki na na kuduri aniyar mugun zama za muci gaba da yi nida Suwaiba don nayi sakacin barin shaidan ya shiga zuciyata ya fara dora min tubalin gina katangar da zai ci gaba da dora bulo Yana zugani Ina hauka, yanzun nasihohinki sunsa duk nayi sanyi na saduda na hakura na barwa Allah dukkan lamurrana, nayi imanin tunda bana nufun kowa da sharri zai kareni idan an nufoni, zai Kuma yi min sakayya muddin aka zalunceni." Rahima tayi murmushi "Alhamdulillah tsarki ya tabbata ga sarkin sarakuna, munyi salati ga Manzonsa Masoyinsa Muhammad SAW, mun godewa Allah da ya baki ikon ruguje wannan ginin, Ubangiji ya Kara Mana kariya da kayangar karfe da shaidan la'ananne ya karemu daga dukkan sharrin abin ki. Abinda Nike son ki gane dukkanmu Nan masu laifi ne kullum cikin daukar zunubi muke amma Ubangiji ya Kan yafe mana idan mun roki gafararsa, wani zunubin ma ko bamu roka ba sai ya shafe mana kasancewarsa Mai tausayi da jinkan bayinsa, to kai waye da zaka ce ba zaka yi hakuri da wasu al'amurra dake faruwa da Kai ba, balle ka yafe, kana ajizi kaskantacce? Haba don Allah ki zage damtse ki bautawa Ubangijinki, ki kyautatawa mijinki, kiyi tarbiyyar 'ya'yanki, kiyi zumumci domin Allah, ki kyautatawa iyaye da yanuwa kiga irin daukakar da Allah zai miki." Maryam taja numfashi ta rike hannyn Rahima "Wallahi naji na amince na dauka na Kuma gode da nasihohinki 'yaruwa Allah ya saka miki da khairan. Yanzun kenan mun shafe chapter mutumin naki?". Ta zabura ta mike "Ina ai hankalin rabuwa yayi, Ina nan, Ina can, yanzun dai kiyi kwanciyarki don sulusin dare yayi, Sallah zanyi da adduoi na musamman in roki ya Azeez ya nuna min shi ko mafarki ne don hankalina ya kwanta." Maryam ta gyara kwanciya " In Kun hadu Ina Mika gaisuwa da jinjina masa saboda ya sace min zuciyar kanwata ya Kuma tsamota daga duhun jahilcin rashin sanin menene *so* Ta shifa toilet ta dauro alwala ta shumfiea sallaya ta fuskanci alkibla tare da natsuwa da kaskantar da Kai domin ganawa sa Mai rufan babu dogara, Mai amsa adduar bayinsa babu shamaki ... Ta dade tana zuba adduointa, ta rufe da salatin Manzon tsira, ata kwanta ba saida sallaci asubah kana tayi matashi da hannunta na dama ta bingire bisa sallayar. Hanyace data kasu har uku, ta rasa wace zata bi, dama,hagu ko tsakiya? Ta yanke shawarar bin hanyar dake damanta, 'yar siririyar hanyar cike take da itatuwa da ciyayi Korra shataf, bata yi nisa ba sai gata gaban wani tafkeken kogi Mai shakare da wasu garai-garain ruwa masu kalar sararin sama, nan ta gane baby hanyar wucewa kenan. Ta juyo cikin hanzari da niyyar ta koma baya nan ta rikice dalilin hanyar ta rikide ta hade danyen ciyawa da itatuwa ga ruwa male-male ta ko' Ina, daga saman bishiyoyin wasu irin kyawawan tsuntsaye ke kuka tamkar suna busa sarewa, sanyin tafkin nan ya fara ratsata, sanyi ya kadata ta shiga makyarkyata, hakan yasa ta waige-waigen da tunanin ratsawa ta cikin ruwan ta fita wannan wajen, tsoro ya kamata, nan take ta daga hannayenta sama ta fara rokon Maiduka ya kawo mata dauki.. Cikin ikonsa Allah sarkin sarauta sai taga wani mashahurin haske ta ko'ina, wani doki Mai fuka-fuki da ya ratso ta cikin hasken nan a guje ya sauko daf da ita. Jikin dokin ba irin dawakan data sani bane, wannan ilahirin jikinsa kalar azurfa ne, gashin bayansa gazar-gazar da kwarar idanunsa ne kawai bakin kirin. Tsananin ganin wannan halitta daya cikata yasa bata lura da mutumin dake Kan dokin ba, bata ankara ba taji an dagta sama an dorata bisa dokin nan ya tashi sama suna tafiya tamkar wasu tsuntsaye, basu dade ba taga sun sauka daf da kofar wani farin gida gewaye da furanni, hancinta ya shaki wani hadadden kamshin data rasa inda yake fitowa, kamar tafiyar slow motion ta tsinci kanta cikin wani lambu cike da kayan marmari, ta mika hannu don ciro nunanniyar goba tsawonta bai Kai ga iccen ba, Mai dokin Nan ne ya matso yasa hannunsa ya ciro goban Nan har zai Mika Mata sai dokin yai haniniya ya kada fukafukinsa sai ya fasa bata Saida ya saka a bakinsa ya gutsura kana ya mika Mata sauran ta karba cikin mamaki, har zata Kai bakinta ta tuna bata san ko waye ba, ko kafin ta dago Kai ya haye dokin ya fara tafiya, ta daga masa hannu tana kiransa da muryar data shake, waigo wan da yayi yasa taga fuskarsa a zahiri ... Ganin ko waye yasa ta nemi yar da rabin gwaibar da ya bata Amma abin mamaki taki faduwa kamar ansa gam an manne gwaibar a hannunta, cikin hanzari ta sake juyowa ko za tayi katarin sake ganin fuskar.. aka yi dace shima ya sake waigowan yana murmushi a gareta, kamar walkiya dokin da Mai dokin suka bace... Alhamdulillah Hamdan Kaseeran... A nan littafin RAHIMA na daya yazo karshe. Za mu ci gaba dana biyun insha Allah. Ina godiya ga Masoyana a duk inda kuke ina muku adduar fatar alkhairi a gareku. Nayi kuskure ban bada number waya ba a farkon wannan littafi, to ga masu son saye da nemana ta WhatsApp a neme ni a wannan num 08034243456 WhatsApp kawai plss Masu son kirana Kuma a nemi a wannan num 07036391747 06/09/2020, 19:50 - Anty saliha: ...RAHIMA..doc by Jami 16 Karfe tara na dare sun nutsa cikin hira, har Hjy Suwaiba ta shigo neman shawara wajen Rahima, sun tattauna kan problem din yaron kanwarta data haifa kurma, tayi musu sallama ta tafi da yake Alh a dakinta yake. Har zasu rufe kofa, Alh. Abbas ya shigo suka gaisa da Rahima kana ya roketa data fita su gaisa da abokinsa da har lokacin yana magiyar son aurenta. Ta shiga falon ta sallama fuska a murtuke ta gaisheshi, ya amsa yaci gaba da 'yan dabarunsu na maza don ta saki ranta. Rahima ta zauna kamar wata mutum-mutumi,ta rinka mamakin lokacin da ta rayawa zuciyarta amincewa ta auri Alh. Abbas, Lalle da tayi wauta, yes a da can da bata San muhimmancin soyayya ba zata iya zama dashi but a yanzun Kam sai dai yayi hakuri, soyayyar wani ya riga ya fara shiga zucciyarta. Wani wa? Ta tambayi kanta, hhmmm wannan wauta nata da yawa yake, to Wai why take jin son bawan Allah nan da aka mata maganarsa? Alh Suraj ya gaji ya gyara zama tumbinsa ya Kara bayyana cikin babbar rigarsa yace "Rahima ko don nace ba Zan amince kici gaba da aiki bane yasa ba Kya ra'ayina? Idan wannan ne na canza shawara wallahi, na amince kici gaba da aikinki, gidanki Kuma daban zan aje ki " Ta gyada Kai "Ko kusa Kar tunaninka ya Kai can, aure ai nufin Allah ne, idan ya kaddaro ba makawa, mu dai ci gaba da adduar zabinsa." Yace "Lalle kin cika 'yar boko, Baki ce eh ko ah ah ba duk da na fahimci komi, duk mai hankali zai gane inda kika dosa, sai dai na hakura, ban Kuma ji zafi ba saboda baki nuna kwadayin abin hannuna ba, nagode Zan tayaki addua, Ina rokon idan lokacin auren ta taho a kawo mun kati da goron gayyata, Zan m bada gudumuwata matsayin yayan amarya.".. Tace "Godiya nike sosai Allah saka da khairan." Yace "Ba komi Rahima." Goma da mintoci har Maryam ta fara barci Rahima ta tashe ta "Barci tun yanzun?" "Yes tunda ranar hutun kenan da Alhajin ba nan yake ba." "Kina nufun idan yana nan ba Kya hutawan?" Ta amsa "kusan hakan ne kina wasa da Alhajin nan da kike gani, wallahi duk ta sangarce, daidai da spoon bai iya dauka da hannunsa ya Kai baki idan ina kusa." ."Su soyayya masu gari." Maryam ta gyara kwancita "Karki zargeni, ke din wa yasan abunsa za kiyi nan gaba, ya kuka kare da Alh Suraj?" Rahima ta sanya rigar barcinta kafin ta amsa "Na fada masa gaskiya yai accepting wai sai Kun Kai masa Iv." Maryam tace "Ko nifa bana amince dashi bane just tsokanarki nike da naga baki da niyyar fidda kowa, yanzun shi Wanda Hajiyar tayi magana ne a fagen?" Wani irin murmushi da farin cikine suka bayyana a fuskarta, Maryam ta daki kafadarta da matashi tace "Lalle wannan ya samu karbuwa a zuciyarki, fada mini ya kike ji?" Saida ta kwanta ta tasa kafadarta da matashi tace "Za kiyi mamaki Yaruwa domin nima cikinsa nike, ashe mutum Kan so Wanda bai taba gani ba, ni fa ko sunansa ban sani ba, labarinsa ma not in details naji amma na kagu na kosa in gansa inji yaya zanji ranar dana fara ganinsa?" Tayi dariya "To ya zaki kwatanta abubuwan da kike ji yanzun da wanda kika ji game da marigayi." Ta tashi ta zauna "Ai sun Sha banban 'yaruwa, son Rabiu a hankali ya riga shigata kwatankwacin mutum ta dora ruwan zafi bisa wuta, a hankali ya fara dumi, ya kai ga zafi har ya nuna alamun tafasa sai wutar ta mutu, to yadda ya fara zafi hakan ya rinka hucewa yana sanyi a hankali har ya zamto yanzun na hakura, dana tunasa adduar samun rahama nake ci gaba da yi masa kullum, wannan kuwa gaba daya ruwan ya dau zafi, kafin in ankara har ya tafaso ya fantsama koina, zuciyata na kuna, babban abinda ke firgitani addua nike lamarin na kara tsanani, ko yanzu ji nike kamar in rufe ido in gansa a gabana don inga wane irin mutum ne da yai saurin raunana min zuciya?" Maryam ta gyara "Tirkashi! Babbar magana, Lalle lokaci yayi da ya dace in baki amsar tambayarki akan menene so? To a iya fahimtata soyayya itace ni'imar mafi daukaka da Ubangiji yaiwa bayinsa baiwarsa, soyayya itace zuciyoyi dunkule ko a cure waje guda, abin nufi idan mutum yaso wani ko wata son nan kesa ko yaushe a kasance cikin tunanin masoyi, rashin damuwa da kowa sai shi/ita, mutum yakan zama bai jin son ji da ganin kowa sai masoyi kamar yadda kika kasance a halin yanzun. Ba abinda so bai haifarwa, so na sa mutum yai hauka ya zauce, idan zuciyar bata samu abinda take so ba ta Kan fita hayyacinta, tayi rauni wani har sai an hada da addua kafin a sami komawa normal. So kansa mutum yanke hukuncin da bai Dana sani matukar ya shafi masoyin, a cikin lamarin so na hakika babu shakka, ba munafunci ba yaudara, ba karya balle zargi, so nasa masoyi tsananta addua ga Wanda yake so ko da sani ko basa saninsa ba. Mutum Kan gane ya kamu da son wani/wata ce ta faduwar gaba a duk lokacinda aka ambaci sunan masoyi, ko gani a zahiri, hoto ko murya. Zaki yawaita son ambatonsa ko son kiji ana labarinsa ko hirarsa, zaki rinka jin son sirrinsa maana halinda yake ciki, jin dadin zancensa, tausayi, fadar gaskiya, nisantar karya in har son na gaskiya ne, haka nan zaki rinka yaba kyautarsa komin kankantarsa da son kema kiyi masa alkhairin komin yawansa, zaki so ki kula da al'amurransu ko yaushe, sannan uwa uba akwai kishi tsakanin masoya na gaskiya but ba irin kishin nan Mai haifar da zargi ba saboda da zaran Kun amince da so da kauna tsakaninku, girmamawa, yarda da aminci ne za suyi tasiri a zukatanku. Ki kula ba kowanne so ne na hakika ba, majority mu kanyi kuskuren fassara shaawa da kalmar so, irin sa za kiga ko an Kai ga aure lokaci kalilan an fara samun problem musamman idan an riga an gusar da sha'awar, hakuri da juna sai yai karanci saboda ba a gina zaman kan tubalin so da kauna na gaskiya ba. Masoya na hakika Kan jure komi don su zauna da juna. Maryam ta numfasa ta kalli Rahima kina fahimta kuwa?" Ta amsa "kwarai kuwa, karance-karancenki ya amfana ta wannan bangaren, kinji bayaninki kamar wata marubuciya?" Tace "Da kenan dana rinka mafarkin zama daya daga cikinsu.. Rahima tace "Ko yanzun kina iya farawa dauko alkalami da takarda ki gani, gashi kina tsaro min zance kamar kina karantawa ba?" "Rufan asiri don Allah, ai na kwatanta naga ba ci dole na hakura, nan na Kara yarda da batun wani malaminmu cewa rubutu baiwa ce, duk Wanda Allsh yaiwa baiwar hikima da basira yaita gode masa kullum domin a cewarsa koda mutum ya sauke kundin karatu ba lale ya iya rubutu ba, don sai in Allah ya bashi hikimar ne zai rubuta a karanta a fahimta har a sami darasi ciki a amfana, Kinga shiga hurumin da Allah bai kaddaro maka bama shishshigi ne da karanbani in dai ba so kike in rinka satar basirar wasu ba." "Ah ah a Kan me, zauna matsayin da Allah ya aje ki,in kinyi hakan ma ai baki kyautawa kanki ba ko?" Maryam ta kyalkyace da dariya "Ban ma ja da nisa ba kin sani, dana gwada naga bai yuwwa bane na hakura, na dai ci gaba da saye Ina karantawa Ina karuwa.... "Karuwa ta wani fannin ba, wani bangaren kam karatun kawai kike don jin dadin labari amma ba Kya daukar darasin komi. Da kina dauka da baki biyewa Hjy Siwaiba kunyi gaba ba, da baki bi nata Kun raba kan yaranku ba, zumunci fa kenan kuke neman yankewa tsakaninsu alhalin Ubangiji yace Duk Wanda ya yanke zumunci bai tare dashi gobe kiyoma, ban da haka, mijin Nan naku fa na iya mutuwa ya barku kowa ta kama gabanta zaman tsakaninku ya farraka, amma yaranku dole suyi zumunci da juna sabili da jininsu daya, ko Allah ya karbi ran daya daga cikinku takalihun yaran ya koma hannun dayanku dole, ko Kuma ma ya kasheku gaba dayanku, mijin naku ya auro wasu su o suci gajiyar yaran da kuke tinkahon Kun haifa, kinsan dai ba yadda Allah bai iya juya lamarinsa ba don haka ake son mu kasance masu hangen nesa, idan ka ciza ka hura, idan kace zaka biyewa zuciya sai ya kaimu ta baro tunda batavda Kashi, shyasa ake son mu rinka adduar Allah yasa mufi karfinta, Kar shaidan ya rinjayeta, ya karfafa mana imaninmu, Ni da zanga dayan marubutanmu ko dana nunaki cikin days daga cikin makarantarsu amma masu karatu suji dadin labari kawai ba daukar darasi balle ku amfana." Ta bude baki "Tafdijan Rahima yau kin gama dani tsaf... "No ba haka bane 'yaruwa, wajibine in taroki idan naga Zaki ksuce hanya in fada miki gaskiya komin dacinta, marubutan fa suna yi don gyaran tarbiyyarmu dana zuriyyarmu don al'ummanmu su samu nagarta mu gyara rayuwar duniya dana lahira." Maryam tayi kasake tana saurarenta, yes Rahima gaskiya take fada mata ba karya ko kadan, Ina amfanin badi ba rai? Wajibi ta taho ta gyara halinta dana zamantakewarta da abokiyar zamanta ko tace makwabciyar ta inji Rahima,ko bata kyautata mata don komi ba tayi don samun ladan, shin sai nawa ma wani lalura ke tasowa daya daga cikinsu Wanda suke takamar shi ya ajiyesun bai nan bai kusa balle ya magance musu? Su jawa suka taimaki juna musamman lalurar rashin lafiya maigidan na can bai ma sani ba sai ya dawo yaji labari? Idan har Ubangiji zai jarabci bawansa ba mu san ta hanyar da jarabawar zata zo mana ba kuwa ya dace mu saduda mu zauna lafiya da juna muyi hakuri tunda ba wace ke zaune kan wata, babu mai korar wata sai in kaddara ta gitta Wanda ba a fata, kowacce da halinta take zaune kota bangaren mijin ne, to wahalar da Kai na menene? Me zai hana suyi hakuri da juna har mai hadawa ya raba, ko tunanin mutuwa ya isa katsewa duk mai imani hanzari, rayuwar guda nawa take mutum ya tsaya Yana batawa kansa lokaci, duniyar guda nawa take, dubi yadda Allah ya dauke Rabiu farad daya aka raba Rahima da mijin da suke zaune lafiya, yaronta ya shiga maraici ko shi bai isa bawa tsoron Allah ba? Wannan duniyar da ba matabbata ba? Hawaye suka rinka gangarowa zuwa kuncinta. Rahima ta gani ta gigizata cikin damuwa "Lafiya kuwa?" "Hawayen godiyar Allah ne da ya kubutar dani ya ganar dani ya hana min biyewa sharrin zuciya, wallahi ba domin zuwanki na na kuduri aniyar mugun zama za muci gaba da yi nida Suwaiba don nayi sakacin barin shaidan ya shiga zuciyata ya fara dora min tubalin gina katangar da zai ci gaba da dora bulo Yana zugani Ina hauka, yanzun nasihohinki sunsa duk nayi sanyi na saduda na hakura na barwa Allah dukkan lamurrana, nayi imanin tunda bana nufun kowa da sharri zai kareni idan an nufoni, zai Kuma yi min sakayya muddin aka zalunceni." Rahima tayi murmushi "Alhamdulillah tsarki ya tabbata ga sarkin sarakuna, munyi salati ga Manzonsa Masoyinsa Muhammad SAW, mun godewa Allah da ya baki ikon ruguje wannan ginin, Ubangiji ya Kara Mana kariya da kayangar karfe da shaidan la'ananne ya karemu daga dukkan sharrin abin ki. Abinda Nike son ki gane dukkanmu Nan masu laifi ne kullum cikin daukar zunubi muke amma Ubangiji ya Kan yafe mana idan mun roki gafararsa, wani zunubin ma ko bamu roka ba sai ya shafe mana kasancewarsa Mai tausayi da jinkan bayinsa, to kai waye da zaka ce ba zaka yi hakuri da wasu al'amurra dake faruwa da Kai ba, balle ka yafe, kana ajizi kaskantacce? Haba don Allah ki zage damtse ki bautawa Ubangijinki, ki kyautatawa mijinki, kiyi tarbiyyar 'ya'yanki, kiyi zumumci domin Allah, ki kyautatawa iyaye da yanuwa kiga irin daukakar da Allah zai miki." Maryam taja numfashi ta rike hannyn Rahima "Wallahi naji na amince na dauka na Kuma gode da nasihohinki 'yaruwa Allah ya saka miki da khairan. Yanzun kenan mun shafe chapter mutumin naki?". Ta zabura ta mike "Ina ai hankalin rabuwa yayi, Ina nan, Ina can, yanzun dai kiyi kwanciyarki don sulusin dare yayi, Sallah zanyi da adduoi na musamman in roki ya Azeez ya nuna min shi ko mafarki ne don hankalina ya kwanta." Maryam ta gyara kwanciya " In Kun hadu Ina Mika gaisuwa da jinjina masa saboda ya sace min zuciyar kanwata ya Kuma tsamota daga duhun jahilcin rashin sanin menene *so* Ta shifa toilet ta dauro alwala ta shumfiea sallaya ta fuskanci alkibla tare da natsuwa da kaskantar da Kai domin ganawa sa Mai rufan babu dogara, Mai amsa adduar bayinsa babu shamaki ... Ta dade tana zuba adduointa, ta rufe da salatin Manzon tsira, ata kwanta ba saida sallaci asubah kana tayi matashi da hannunta na dama ta bingire bisa sallayar. Hanyace data kasu har uku, ta rasa wace zata bi, dama,hagu ko tsakiya? Ta yanke shawarar bin hanyar dake damanta, 'yar siririyar hanyar cike take da itatuwa da ciyayi Korra shataf, bata yi nisa ba sai gata gaban wani tafkeken kogi Mai shakare da wasu garai-garain ruwa masu kalar sararin sama, nan ta gane baby hanyar wucewa kenan. Ta juyo cikin hanzari da niyyar ta koma baya nan ta rikice dalilin hanyar ta rikide ta hade danyen ciyawa da itatuwa ga ruwa male-male ta ko' Ina, daga saman bishiyoyin wasu irin kyawawan tsuntsaye ke kuka tamkar suna busa sarewa, sanyin tafkin nan ya fara ratsata, sanyi ya kadata ta shiga makyarkyata, hakan yasa ta waige-waigen da tunanin ratsawa ta cikin ruwan ta fita wannan wajen, tsoro ya kamata, nan take ta daga hannayenta sama ta fara rokon Maiduka ya kawo mata dauki.. Cikin ikonsa Allah sarkin sarauta sai taga wani mashahurin haske ta ko'ina, wani doki Mai fuka-fuki da ya ratso ta cikin hasken nan a guje ya sauko daf da ita. Jikin dokin ba irin dawakan data sani bane, wannan ilahirin jikinsa kalar azurfa ne, gashin bayansa gazar-gazar da kwarar idanunsa ne kawai bakin kirin. Tsananin ganin wannan halitta daya cikata yasa bata lura da mutumin dake Kan dokin ba, bata ankara ba taji an dagta sama an dorata bisa dokin nan ya tashi sama suna tafiya tamkar wasu tsuntsaye, basu dade ba taga sun sauka daf da kofar wani farin gida gewaye da furanni, hancinta ya shaki wani hadadden kamshin data rasa inda yake fitowa, kamar tafiyar slow motion ta tsinci kanta cikin wani lambu cike da kayan marmari, ta mika hannu don ciro nunanniyar goba tsawonta bai Kai ga iccen ba, Mai dokin Nan ne ya matso yasa hannunsa ya ciro goban Nan har zai Mika Mata sai dokin yai haniniya ya kada fukafukinsa sai ya fasa bata Saida ya saka a bakinsa ya gutsura kana ya mika Mata sauran ta karba cikin mamaki, har zata Kai bakinta ta tuna bata san ko waye ba, ko kafin ta dago Kai ya haye dokin ya fara tafiya, ta daga masa hannu tana kiransa da muryar data shake, waigo wan da yayi yasa taga fuskarsa a zahiri ... Ganin ko waye yasa ta nemi yar da rabin gwaibar da ya bata Amma abin mamaki taki faduwa kamar ansa gam an manne gwaibar a hannunta, cikin hanzari ta sake juyowa ko za tayi katarin sake ganin fuskar.. aka yi dace shima ya sake waigowan yana murmushi a gareta, kamar walkiya dokin da Mai dokin suka bace... Alhamdulillah Hamdan Kaseeran... A nan littafin RAHIMA na daya yazo karshe. Za mu ci gaba dana biyun insha Allah. Ina godiya ga Masoyana a duk inda kuke ina muku adduar fatar alkhairi a gareku. Nayi kuskure ban bada number waya ba a farkon wannan littafi, to ga masu son saye da nemana ta WhatsApp a neme ni a wannan num 08034243456 WhatsApp kawai plssðŸ™ðŸ¿ Masu son kirana Kuma a nemi a wannan num 07036391747 Kasancewar littafin RAHIMA na sayarwa ne masu son saye Acccnt number mu shine 0598537268 GT Bank. 07/09/2020, 21:32 - Anty saliha: ...ˆRAHIMA..doc by Jami 17 Ta farka cike da mamakin murdadden mafarkin da tayi, cikin gigita ta rinka karanto adduar shugaban ayoyin alqur'ani kana ta dora da adduar neman tsari daga mugun mafarki, tsorene ya hanata jin sautin muryar Maryam da take karatun qu'ani can gefe daya, ta kasa yin wani kwakwkwaran motsi, da kyar ta tashi ta nufi toilet ta sake dauro alwala ta gabatar da sallar dhuha sannan itama ta dauko qur'anin ta fara karatu . Basu tashi Kan sallayarsu ba saida suka dauki dogon lokaci don sun saba tyn suna gida duk bayan sallar asubah sai sunyi karatun sa'annan su dora sa azkhar din safe don kwadayin dacewa da lokacin amsar addua. Goma daidai sunyi wanka sun kintsa tsaf, Rahima ta kalli Maryam 'Ba zanyi breakfast ba, gida zan koma yanzun nasan Umma na zuba idon ganin na koma da wuri." Ta kura mata ido "Akwai abinda ke damunki duk kin canza wayewar garin nan, ko baku hadu da surukin nawa a mafarki bane?" Ta koma ta zauna jiki babu kwari kamar wace aka zare mata lakka tace "Ke dai bari 'yaruwa, nayi adduoi na roki Allah yadda kika sani but Wanda na gani cikin mafarkina... Kai!!! Ta girgiza Kai, na firgita wallahi." Maryam ta kalleta "Shakka kike?" Ta kada Kai "No mamaki nike ji da fargaban mafarkin nawa ya zama real." Maryam ta kalleta cikin damuwa "Kinata kwanare, shin wa kika gani ne?" Rahima ta jinjina "Hhmmmm bana jin zaki amince da abinda zan fada miki." "Me zai hanani yarda after all Allah muka roka Ya amsa mana mene na al'ajabi? Ni wallahi ko waye na yarda na amince shi dinne zabin Allah." Ta kauda Kai tayi shiru na dakika kana tace.. Maryam *Ya Haseeb* fa na gani a mafarkina." Duk da dakewan da tayi itama taji mugun mamaki ta buga kirji "HASEEB! Ba dai Dr Haseeb wan Rabiu ba?". Hawaye suka ciko a idanunta yayinda ta amsa " Shi din ne, me hakan ke nufi Maryam?" Ta taso ta matso kusa da ita ta dafata cikin rarrashi "kwantar da hankalinki za kiyi mu saurari Hajiya muji nata manufar amma a hakikani mafarkinki gaskiya ne,zaiyi wuya aure bai shiga tsakaninku dashi ba Ina ganin tun farko shi Hajiyar ma ke nufi." Cikin sheshekar kuka ta dago "In hakura dame? Haba Ina! Idan har shi take nufi na fasa amsa batunta, ba Zan iya zama dashi matsayin miji ba." "Kina son zancen yai tsawo kenan, shikenan mu bari har zuwa sauran kwanaki ukun data diba miki mu gani, mu ci gaba da addua Allah ya tabbatar mana da khairan" Hankalinta a tashe ta shiga tayi sallama da Hjy Suwaiba ta wuce gida. Nan da Nan Umman ta gane akwai abinda ke damunta tana cikin matsala saboda tunda ta shigo ba walwala a tareda ita, abin mamaki ko Abdul bata tambaya ba. Har zuwa karfe biyar na bayan la'asar babu canji a tareda Rahima hakan yasa a matsayinta na uwa Umma ta kira cikin daki ta yambayeta meke damunta. Nan take ta musa cewa babu komi, Umman ta kalleta cikin damuwa tace "Shikenan tunda ban isa ki fada min matsalarki ba." Rahima ta saka mata kuka tace "Idan ma akwai matsala nina janyowa kaina Umma imda nayi aurena tuni da ban shiga kangin Nan ba, yanzun ya zanyi da Raina?". Umma ta Kara rudewa "Ya za ayi in baki amsa tunda ban san damuwar taki ba?" Da yake sun saba basu boye Mata komi ta zayyane mata labarin mafarkinta da yadda suka yi da Maryam" Ta dade bata iya magana saboda zancen ya daketa itama amma ta daure ta kalli 'yarta "To in banda shirmenki mene na tada hankali harda koke-koke? Aure ba nufin Allah bane, matar mutum kabarinsa, kin taba ganin mijin da bai auri matar da ba tasa ba? Idan Allah ya kaddaro Haseeb mijinki ne babu Wanda ya isa ya hana, don haka ki natsu ki barwa Allah muga abinda zaiyi tukunna." Tasa handkerchief ta share hawayen dake fitowa tace "Ba abinda ke damuna irin alkawarin dana daukarwa Hajiya na amince da zabinta ba tare da tunanin wai shi take nufi ba, haba Umma ya za ayi wannan danyen aikin?" Umma ta kalleta "Ta yaro kyau take bata karko, tashi jeki share hawayenki, Zan nemi Hajiyar mu tattauna mai yuwwa in har hakanne." Tace "Don Allah Umma idan zaki, ki kwashe kayan Abdul ki Kai musu na hakura dashi, don ina ganin ita kanta Hajiyar sabida shi ta yanke hukuncin Nan, watau Kar in auri wani can daban in tafi dashi." Ta bude baki tana mamakin kalaman diyarta, lakle sai sunyi da gaske, tace "To Ina Kuma ruwan Abdul da za ayi masa mai gaba daya, ki bari zan maidashi gidansu idan lokaci yayi Kuma don Allah kar in sake jin kin zargi Hajiya kinsan ba zata cuceki ba, ko alama bai dace kiyi furucin da kika yi ba." Ta kwana ta yini cikin zulumi da fargaba abinda zau faru. Gaba daya komi yai mara dif, brain dinta ya hargitse, zuciyarta ta kasa sarrafa komi sai tunanin yadda akayi ta amince da so da kaunar wanda bata taba gani ba, to ai yanzun ta daina ikrarin haka, shin ba Ya Haseeb ne ta tsunduma cikin kogin soyayyarsa ba? Satin data dauka tana adduoi suka cika amma ta kekasa kasa taki komawa gidan Hjy Kaltume, bata aika an dauko Abdul din ba ma, ko da tanada tabbacin Umma ta ziyarci Hajiyar amma bata ce mata komi, ita da Baffa sun sa mata ido sai wani lallabata suke, ta share kowa a gidan hatta Maryam data taho ta rasa gane kanta. Babu Wanda bai san asibitin nan mai suna *HASEEB MEDICAL CENTRE* ba, ba don komi asibitin tayi fice ba sai domin kwarewan babban likitan(CMD). Dr Haseeb Junaid Galadanci dogo ne mai dan jiki, launin fatar jikinsa chocolate ne hakan yasa tsakar mallacin da aka yi masa suka fito sosai a gefen kumatunsa a 'yar doguwar fuskarsa wadanda suka kara fito da kyaunsa na zahiri. Yana da zafin nama sosai, hanzarin nasa ya dace da irin aikinsa watau kwararren likitan da ya shahara yai suna bangaren daya shafi rashin lafiyar kwakwalwa, kashin baya da halittun da suka danganci wadannan ababe masu matukar muhimmanci a jikin Dan Adam Dr H.J.G yadda ake kiransa yasan hallitar kwakwalwar bil adama tamkar yadda yasan tafin hannunsa, kazaliza don ya bude kan mutum ko baya ya mayar ya dinke ba wani abu ne mai wuya a wajensa ba, da taimakon Allah duk wata matsala da aka kawo masa akayi sa'a ya duba yai aiki ko bada magani a kanyi nasara. Dalili kenan da sunansa ya bunkasa tun daga gida Nigeria har kasashen waje, manyan asibitocin ketare ma dashi suke takama don ba inda kafafunsa basu taka ba. Sabida yawace-yawacen da yake yi ne yasa shi jin harsuna daban-daban, yana jin harshen larabci, faransanci, jamusanci, dangane da yaren harsunan kasarmu kuwa tun Yana jami'a ya iya yaren yarbanci, fulatanci dana igbo, abin ban sha'awa duk yaren daya juya harshe Yana yi sai mutum ta rantse daman shine mother tongue dinsa. Ganin yadda ayyuka suka yi masa yawa, zirga-zirga na neman tauyesa wajen sauke hakkin iyalinsa dana iyaye yasa ya yanke shawarar gina makekiyar asibiti Wanda ya nemi wasu kwararuj likitocin suka hadu suna gudanar da harkar asibitin gadan-gadan. Babban abin shaawa da yawanci maganar da mutane suke fadi shine ma'aikatan asibitin nada karamci tun daga leburori zuwa nurses da doctor's dinsu balle shi kanshi uban tafiyar, ta ta shahara wajen tsabta sosai, babu wulakanci tsakaninsu da patients, sun dauki Mai kudi da talaka gudane, patient sunansa patient Kuma Abu guda suka zo nema (lafiya) don haka babu banbanci. Ba nan ya tsaya ba da kyautatawa patients dinsa ba, da duk ya lakanci basu da halin biyansa hakkinsa ya kan taimaka yayi aikin kyauta tareda kulawa ta musamman. Daga bayan nan yawanci manyan asibitocin gwamnati ke turo masa da patients yai musu abinda ya dace gwamnatin ta biyasa hakkinsa. Can kasashen waje ko yaushe irin aikinsa ya taso sukan bugo masa waya ya tafi don ceton rayuwar Al'umma, a dalilin hazakarsa ne suka yiwa sunansa laqani da Mr Brain. Ga Wanda bai taba ganinsa ba kuna yin ido biyu fuskarsa zata nuna maka alamar mutum ne mai ji da kansa domin miskili ne na karshe. Wani irin mutum ne da samun irin halayensa sai an tona, fuskarsa a daure take ko yaushe, baya dariya gaban kowa amma kuma mutum ne mai saukin kai idan aka fahimci halinsa. Dr Haseeb mutum ne da bai dauki abin duniya da ita kanta duniyar wata tsiya ba face wajen gwaji da neman tsiran gobe kiyama har ya kance mutane na shirme wajen maida duniyar wajen zama tamkar ba za a mutu a barta ba, mutum ne shi mai sadaukar da kai da maida dukkan al'amurranss ga Allah. Bai da saurin karaya don haka ya fita zakka cikin abokai da sa'oinsa musamman ma da wuya suke gane inda yasa gaba. Mutum ne Mai son rayuwa don ance ka nemi duniyar tamkar ba zaka mutu ba, ya rike addininsa matukar gaske saboda ance ka gyara lahirarka tamkar yanzun zaka tafi. Ya kanyi wuya a tabashi ya hakura in dai har ya tabbatar da gaskiyarsa, mutum ne Wanda baya karya yakan Kuma kure duk Wanda ya nemi yai masa hassada har sai yaga abinda ya turewa buzu nadi. Bai da fargaba, bai da tsoro, bai da hayaniya, mutum ne natsatstse kamilalle, bai son raini don bai rana na gaba dashi ba, yana son ayi masa biyayya, bai daukar jita-jita, baya son girman Kai ko nuna Kai wani ne, bai taba daukan kansa wani abu ba, Yana son hira da Wanda ya amincewa, idan har an zauna dashi mutum ne da ake karuwa dashi ta hanyoyi da dama, Allah yai masa laqanin iya zama da mutane. Haka nan yakan kaunaci duk Wanda ya nuna masa kauna ya Kan guji makiyinsa cikin kowanne hali. Dr Haseeb mutum ne Mai tsananin kusantar Ubangijinsa, wajen ibada da adduoi neman taimakon Mahaliccinsa a dukkan al'amurran da suka jibanci rayuwarsa, bai Kuma taba tunanin Ubangiji bai amsa bam Ranar da Mahaifiyarsa tayi masa batun auren matar kaninsa Rabiu ya razana sosai, batun ya dameshi ya tsaya masa a rai matuka, amma damuwar data fi masa ciwo itace yi mata musu sabida in har yana kaunar mutuwarsa to zai so abinda zai bata mata rai, baya kaunar abinda zai sosa Mata rai ko kadan. A kullum yana danganta samun nasarar da yake a rayuwa da dimbin adduointa ne garesa bayan albarkar da take sa masa kullum. To yanzun data gangamo aure, auren ma na wace ko a mafarki bai taba tunanin faruwarsa ba ya zaiyi da bukatar ta? Ba wani abinyi illa amincewa da bin umurninta da fatar Allah yasa ya zame musu alkhairi duka. Amma ya yankewa kansa the most difficult decision in his life duk da bai yanke shawarar ba sai da yayi adduoi kamar yadda ya saba ya roki Ubangiji fa'ida kan al'amarin, da alamu akwai haske sai kara neman taimakon Allah. Tunaninsa ya koma Kan yarinyar ko yace matar da ake son ya auran, zuciyarsa ta amince Rahima yarinya ce mai natsuwa da hankali, tanada biyayya tunda bai taba jin ance wani sabani ta shiga tsakaninta da marigayi ba, yasha jin irin yabawar da Hajiya ke Mata, yasan yadda ita din take girmama Mahaifiyarsu wanda mutuntata da take yi me ya Kara haddasa son hada wannan auren. Idan ya tuna yaronsu Kuma, Abdul ya shaku dashi, shima jaksn fiye da 'ya'yan cikinsa ma wanda bai rasa nasaba da matsalar uwar yaran da tafi son 'ya'yanta su yini su kwana a can gidansu fiye data kawosu wajen Hajiyarsu. Da ya nuna rashin amincewarsa ta kawo masa uzurin sunfi sakeea a can saboda akwai yara sa'oinsu Kuma tunda shi ba mazauni bane meye na complain. Yan kwanakin nan da Hajiyar ta diba masa ayyuka sunyi masa sauki don hakane ya Sami daman yin nazari da adduoinsa a natse, ysi reaching decision don haka bai bata lokaci wajen dumfararta da shawarar da ya yanke ba. 07/09/2020, 23:52 - Anty saliha: ...ˆRAHIMA...doc by Jami 18 Ganinsa tunda sassafe a Rana ta takwas da yin maganarsu baisa ta saki fuska, ya durkusa ya gaisheta ta amsa a dakale. Daga can cikin uwar daki Abdul yaji muryar babansa ya tashi daga barci ya fito yana mutsuke idanu, Haseeb ya riko sa ya zaunar dashi cinyarsa ya rungume ya kalli Hajiya yace "Ashe har yanzun bai koma ba?" Tace "Mamansa bata zo ba Ni kuma ban aika ba.".. Ya kalli yaron da kullum idan ya hansa sai ya Tina da danuwansa, ya kada Kai tare da kara rungumarsa, nan da nan ya koma barci, Hjy Kaltume tace "Wannan shakuwa taku tayi yawa, muryarka fa yaji yasa ya taso barcin bai ishe shi ba." Ya kada Kai hakane, ba a kaishi makaranta ne naga har kusan tara yana barci?" Ta amsa "Yana zuwa mana ka sani, bai jin dadi ne tun jiya da dare ya kwana zazzabi har yana firgita yana Kiran uwarsa Yana kuka." Ya dafa kansa "Ashsha subhanallah, ya taba jikinsa, gaskiya har yanzun da alamun zazzabin ko asibiti za a kaishi?" Tace "Nima tunanina kenan." Ya Kara duba shi Kuma yace "Ba sai yaga likita ba idan yasha magani ma zazzabin zai sauka bari inyi masa addua yanzun." Dr Haseeb ya dafa jikinsa ya karanto *BISMILLAHI A'UZU BILLAHIL AZEEM MIN SHARRI KULLI URQIN NAARIN WA MIN SHARRI HARRIN NAAR... Ya kara dora hannunsa na dama saman goshinsa ya karanto *AS'ALUL LAHAL AZEEM RABEEL ARSHIL AZEEM AN YASHFEEYAKA... Bayan ya gama yace insha Allah zai samu waraka." Ya mike ya maida shi cikin dakin ya kwantar dashi kana ta dawo ya zauna.. Ta daina abinda yake yi ta fusksnce shi sosai tace "Tun shigowarka nike alla-allah inji ta bakinka ka barni inata ci da kuda, wace shawara ka yanke?" Ya sunkuyar da Kai tare da yin kakkarfar ajiyar zuciya, to in ba domin uwa, uwa ce ba wa ya isa ya tursasa masa yin abinda baiyi niyya ba? Ya dago Kai a hankali yace "Tunda kin ganin auren alkhairi Kuma kin amince shikenan." Ta saki murmushin jin dadi tukunna kafin tace "Fito fili kayi min bayani, shikenan kamar yaya?" Ya sake jan dogon numfashi "Ina nufin na yarda Zan aureta, sai dai kin tuna ina tsoron ajiye mata biyu domin shakkar rashin yin adalici tsakaninsu bayan haka kina ganin zamu zauna cikin kwanciyar hankali bayan Ni da ita ba son juna muke ba?" Dariya ce ta kubuce mata tace "Itama Zuwairar da bata zake a kanka ba da tasha wuya, miskillancinka ba boyw yake ba, wannan Kuma batun soyayya bata ko taso ba ya ma rage naku, ko kuso juna ko ki da zaran Allah ya hadaku addua kawai za muci gaba da yi muku.' Hhmmmm ya Fadi a zucci Hajiya mahaifiyarsa ce yana alfahari da hakan, har bugun gaba yake yana ganin yafi kowa sanin jakinta but akwai so many times da ya kanyi doubting hakan musamman idan ta murde ta rikice ya kan rasa inda zai bullo mata kamar yanzun. To in ma banda abinta ya za ayi mace da namiji suyi zaman aure da ya dace bayan babu so da kauna tsakaninsu? Har gara ace mutum guda na so, in tafiya tayi nisa sai dayan yaja ra'ayin gudan amma wannan halin kaka Ni kayi dane yai kama?, Da shi da ita duk basa so, sai yaya kenan?.. Tayi kamar baya dakin ta jawo tarkaccenta zata fara kulle-kullen ta, yasan hali muddin bai sake magana ba ta kare nata zancen kenan don haka yai saurin tambayarta"Yanzun me zanyi abin nufi wane mataki za a dauka nan gaba?". Taci gaba da hidimarta "To ni Kuma zaka tambaya kana namiji kace baka san yadda ake neman aure ba, Kai don Allah baka ji kunya ba, lokacin da kaje samartakat auren farin nina koya maka yadda zaka yi?" Ya dafe Kai!Oh oh ya shiga uku, ya lura so take ta tursasa shi, ya daure yace "Hajiya wancan da wannan ba daya bane, kin manta inada matsayi a gidansu Zuwaira tun fil azal bayan kaunar dake tsakaninmu?" To nan dinma sai ka gwada gidansu Rahimar ka gani su ma wanne matsayin zasu baka idan itama kana neman samun gurbi a zuciyarta kasan hanyoyin da suka dace ka bi, Allah yass a dace.' Yadda ta hakikice tana maida mishi martani yasa shi dariya da sha'awa yace ",Idan naje anjima da laasar na ganta banyi laifi ba ko?" "Wane Kuma irin laifi ai sai fatan Allah ya kulla alkhairi, kaje ka gabatar da kanka matsayin mijin dana ce nayi Mata Kuma tayi alkawarin ta amince, idan zaka tafi ka biyo ka tafi da takwaranka yaga uwarsa don da biyu taki zuwa gidannan, Nima naki aikawa dashine saboda jiran wannan ranar, sai kaje Ina saurarenki, Ina gaishets da kyau.".. Ya fita Yana murmushi itama haka. Ranar a gida Maryam ta yini, Rahima na dawowa makaranta kenan direba na ajiyesu, Walida tasa kuka bata ga Abdul abokin kirinyyarta ba, Saida aka tula mata kayan wasansa tayi shiru. Su kuma iyayen nata hidimar dora sanwar abincin rana saboda Umman tasu ta tafi Gumel dubo mahaifinsu da bai ji dadi ba, amma tana gab da dawowa, hatta yaran gidan kanninsu basa gida. Bayan sunci sun koshi sunyi sallar laasar Rahima ta shiga wanka ta fito ta sake dauro wata alwalar kana ta shigo daki ta shirya tsaf Kai kace shirin zuwa buki take. Maryam ta kalleta "Sarkun kwalliya kina burgeni wallahi karki so kiji yadda Nike sha'awar kirar jikinki 'yar caraf dake, wa zai ce wannan dafaffen cikin ya dauki da kin haihu."" Rahima ta kanne mata ido guda "Aunty Maryam sarkin mita, ke din ai kike jawowa kanki katon ciki, inda halitta da rashin kulawa, irin naman da kike dankara lafiya ne, ki ci kowanne irin nama, kisha kayan Zaki, kefa duk inda kayan dake Kara kitse suke kina Nan ya ba zaki ajiye teba ba, gaki Nan haihuwa daya kin zama wata guzuma, idan kin Kara sai Alh Abbas ya auro daidai misali don har Hjy Suwaiba barakallsh Masha Allah." Ta wurgeta da maficin dake hannunta "Shima din ba kiga yadda ya koma ba har tozon wuya ya fara fa." Rahima tace "Hhmmmm da Rabiu na nan da ya kusan kibar Alhajinku, dubi yadda ya koma kafin rasuwarsa." Maryam ta shareta, ta sake maimaitawa, a nan ta kalleta tace "Saboda Allah Rahima ba zaki bar wannan bawan Allah ya kwanta makwancinsa lafiya ba, ke kenan da duk aka tada magana sai kin sako zancensa, Ina amfanin haka, adduarmu kadai yake bukata.".. Ta nisa tareda dafe kanta "Nima bana sanin time din da nike ambatonsa Maryam, Ina kokarin dainawa." . "Ah to gara ki yiwa tufka hanci don ba namijin da zai dauki Yana aurenki kina zancen wani wanda ya rigamu gidan gaskiya." "Nace miki zan bari, da kike fadin hakan ai mijin fari wuyan mantuwa gareshi, balle ma kowa na aura dole yai hakuri dani." Ta kalleta a shagube "Sai dai kuwa idan bai sonku, muddin Yana kaunarki zaku rinka Kai ruwa rana ne, Wai ma ba haka ba ya batun Dakta?" Rahima ta canza nan take "Ki bar batun nan don Allah, ai don in nunawa Hajiyar ba Mai yuwwa bane in har hakan take nufi naki komawa gidanta, har Abdul na bar musu in dominsa suke son aikata abin kunya, ko hausawa sunce ana barin halas.... Maryam ta harareta " Jiya dominki nayi tambaya a islamiyya kan shirmen da kike yi Kuma in fada miki don kin auri Dakta ba abinda ya kaucewa shariar musulumci bane, Malam yace addininmu nai hana wa ya auri matan kani na idan Allah yai masa rasuwa hakan shuma kani na iya auren matsn Wan sa in haka ta kasance.. Har da misalin cewan ko suna da rai ce dayansu ya kamu da rashun lafiyar da ya hana yin sunna da matarsa an nemi magani an rasa na tsawon shekarun da aka gindaya masa zai sahale mata gashi ya yaba hankalinta bai son tabar gidan don kyakkyawar dabi',unta Yana iya yiwa danuwansa maganar cewan iin ya saki shu ya aureta idan sun daidaita tsakaninsu, Kuma auren ya halasta, ke dinma banga abun tada jijiyoyin wuya bayan da bakinki kika fada min kina son Daktan . Ta kauda Kai "Na dai so mutumin da aka bani labarinsa, da lamarin ya juye Kuma na sanu canjun ra'ayi. Ta wani kalleta 'Karki kawi mun burgar banza, karyarki wallahi, was yace Miki ana yiwa soyayya yankan kauna, yadda mashin son wancan ya soki kirjinki haka na Daktan zai huda zuciyark tunda batun mutum guda ake in dai dama ba karya kike ba Wanda a sanina ba a karyar so da kauna." Da taji alamun ta kamo hanya zata kureta saita canza hirar cikin dabara.... Suna cikin hirar suka ji yar karamar muryar Abdul ya shigo a guje Yana fadin 'Mami Kinga jirgina baba ya saya min." Murnan ganinsa ya rufeta, ta daukeshi tana sumbatarsa "Oyo-oyo Abdul Ina Hajiya?. Hankalin yaron ma wajen Walida, ganin hakan ta sauke shi, Walidan ta fara kukan sai ya bata jirginsa. Rahima tace Baba ya hada rigima kenan dole gobe inje in sayo miki naki jirgin". Wani yaro Dan makwabtansu ne ya shigo Yana sallama suka amsa "Wai ance ana Kiran maman Abdul a waje."... Rahima ta kakki Maryam kinji Kuma Bala da gulma shi daya saba shigowa har cikin gida a gaisa ". Maryam tace "May be sauri yake, fita kiji in zai koma da Abdul dinne tunda ban gansa da kayansa ba." Maimakon ta tsaya saka hijab, katon gyalen Maryam ta dauka ta yafa ta fita cikin sauri. 08/09/2020, 13:42 - Anty saliha: ...RAHIMA...doc by jami 19 Tun daga kan soron farko kamshin turaren 'fame' ya fara dukan hancinta, zuciyarta ta fara bugawa cikin sauri, ba dai zarginta zai zan gaskiya ba? Ta karisa cikin tsakiyar soron gidansu inda tayi arba da *HASEEB* in person, rawar da jikinta ya fara, bai hanata saurin durkusawa cikin ladabi tace "Barka da yini, ya su Aunty Zuwaira?" Ko kallon arziki bata samu daga gareshi ba Ya amsa a takaice "Lafiya." Ya shiru Ta dan jima tsugunne tana jiran taji da wacce ya taho tunda bai taba zuwa gidansu ba. Da ya tuna bai da wata mafita dole ya fadi dalilin zuwansa kamar yadda yaiwa Mahaifiyarsa alkawari,ya cije, cikin isa da miskillancisa ya tambayeta "Magana ta kawo ni ko zan sami damar Fadi?" Kamar ta amsa cewan bata da lokacin saurarensa, saita tuna kaninsa,da irin girmansa da yake gani kamar uba ba wa ba, ta tuna dawainiyar da yake dasu, hakan yasa ta hadiye zuciyarta tace "Ba damuwa Ina saurarenka." Ya gyara tsayiwarsa sosai ya jingine da bango tareda goya hannayensa a kirji yace "Hajiya tace tayi miki bayanin komi don haka ba zan tsaya wani dogon bayani ba tunda kin amince da shirinta nima hakan akan dole yanzun ya rage naki kiyi shawarar yaushe kike ganin ya dace a daura auren?" Gabanta ya buga rugugu, aure? Haka ake zancen auren cikin isa da kasaitar mulki, aiki jawur, tun kafin tafiya tai nisa bata iya cewa ta fasa, daman ta amsa ne saboda bata san shine ba, wata zuciyar kuma tace zaki zan mai karya alkawari kenan wanda a addinance hakan ya zama munafuci, can ta nisa, tace "Bani da yancin kaina koda nike bazawara, iyayena keda hakkin wannan sai abinda kika ce." Shi kansa yasan nai kyauta, bai dace ya furta mata wadannan kalaman ba, ba ita ta Kar zomon ba, yaja numfashi yace "Okay zan jira su zartas da shawarwarinsu, nawa iyayen zasu taho in Sha Allah." Da yaji ba zata kara cewa komi ba,sai ya Kara gyara murya yace "Abdul kuwa bai ji dadi ba amma naga ya warware, dazun jikin yafi masa zafi." Tana dai tsugunne kanta sunkuye har zuwa lokacin, maganar da yake yi bai sa ta dago ba balle tayi responding. Ya kada Kai "Ni zan koma, na wani problem ko?' Ta girgiza Kai. "Ina Abdul, in koma dashi ko a bar shi?" sai a nan ta amsa "A tafi dashi, sai an jima a gaida Hajiya Aunty da Zuwaira." Tana gama magana ta yunkura ta mike ta shige cikin gida ta barshi nan a tsaye. Tana shiga ta cewa Maryam "Don Allah dauki Abdul ki mika sa waje zasu koma gidane." Ta kalleta taga fuskar nan tata a daure bata tsaya tambaya ba ta rike hannun yaron suka nufi kofar gidan. Ko da wasa ba tayi zaton shi zata gani ba amma ta danne mamakinta ta gaisheshi, Abdul ya ruga wajensa ya kama hannunsa suka shiga mota suka wuce. Har tana tuntube wajen saurin komawa cikin gida inda ta isko Rahima ta cika tayi dam, ta kalleta ta tuntsure da dariya tace "Yau Allah ya hadani da famous Dr Abdul-Haseeb Junaid din da ake magana, he's very handsome, ashe ganinsa a zahiri yafi ganinsa a tv." Rahima ta cafe "May be ganun baiwar kyaun da Allah yai masa da kirar jiki msi kyau ne yasa yake wani ji da kansa." Maryam tace "Ke fa na lura ba zaki kwantar da hankali ki fahimcesa ba, to komin ji da kansa dai gashi ya taho har gida, ya kuka yi?" Ta tabe baki "Maganar ma da kyar yake har Yana m fada min shi dole ne ya amince da batun auren Wai Kuma yaushe nike son a daura? Ke kinji wani galari, wallahi ba domin ina ganin mutuncinsu ba da yaji magana daga bakina, darajar Rabiu kawai yaci, ko an fada masa nima da son raina za ayi oho." Maryam ta tausayawa 'yaruwarta tace 'Gaskiya al'amarin da rikitarwa Rahima amma kiyi hakuri ki rungumi kaddara,Allah da ya shirya faruwan haka daku yasan dalilinsa, mu 'yan tayaku addua ne, ki daure karki dorawa Dakta laifi, shima na tabbatar abin na damunsa dole yaji a jikinsa." Ta share hawayen da suka gangaro tace "Ya zanyi hakuri ya zama dole but babban bakin cikina reaction din daya nuna min, koni na nemi auren nan iyakar cin fuskar da zai min kenan." Maryam tace "Ni kuwa ban dauka wulakanci bane, kisa kanki a position dinsa ki kwatanta ya za kiji... "Maganar ta wuce Maryam, I've already made up my mind and there is no going back, so zsn daure ko me zasu taso, hhmmm Allah dai yaji Kan Rabiu." Maryam ta mike tsaye "Zaki fara ba, to ba dani ba, naga alamun su Umma sai dare zasu iso ko in dan saurara zuwa karfe tara ma tafi gida?" "Yes idsn ba wani damuwa nasan suna gab da shigiwa insha Allah kinsan Baffa bai son tafiyar dare." Takwas saura kwata na dare suka dawo, Baffa yace su tsahirta yayi sallah sannan su gaisa, Umma Kuma ta zauna suna hirar 'yanuwa da abokan arziki na garin Gumel. Alh. Mamman ya shigo bayan ta fito daga masallaci ya fadawa Rahima tanada bako a waje, taso taki fita Umma ta fara fada. Direban Daktan ne jingine da mota yana jiran fitowarta, tana isa ya durkusa ya gaisheta kana ya bude motar ya fiddo wasu manyan ledoji guda biyu ya mika Mata Wai sakon ubangidansa.. Ta karba a sanyaye tace ya jirata kadan, ta koma ciki ta dauko masa tukwici ta kawo masa ya karba da kyar yana godiya. Ta sake komawa tana shifa dakin ta kwashi ledojin ta diresu gaban Umma "Gashi wai inji baban Abdul " Kafin Umma tace komi Maryam ta zaburo "Masha Allah, iye 'yar gidan Daktan ba, bari mu gani Musa albarka." Umma ta harareta "Wannan zarbabin na menene?" Ta kalli Rahima "Kinji Umma tafi son ki bude kyautar da hannunki ko kin ban izni in bude?" Rahima ta amsa "Idan kin ganin ki wuce dasu na baki banso." Tayi wani shewa ta shiga zazzage kayan, ledan farko tarkacen cosmetics ne, na biyun atamfar super ce biyu, Holland biyu hade da lallausar hadaddiyar shadda. Ta kyalkyace da dariya "Ashe ni ras, bari inga wace zan fara dinkawa, ta bude turmi guda wani envelop ya fado mai dauke da rafar kudi Wanda aka rubuta kudin dinki a bayan envelop din.. Sakonsa ya daure mata Kai, shi da ya taho Yana shan kamshi yana fadin an tursasa masa ne meye na wahalar da Kai, ko kayan ma matsa masan aka yi ya aiko? Baffa ya shigo dakin a lokacin suka gaidashi da tambayar mutanen Gumel, yace kowa lafiya duk zasu taho daurin auren Rahima da bukin tarewa." Ta zumburo baki ta kalli uwar "Yanzun Umma har Kun karas da abinda babu tabbas?" "Kunji munafuka inji Maryam, mu kam mun tabbatar tunda dazun nan Dakta Haseeb ya taho wajenta Baffa sannan ya aiko da sakon nan ace babu tabbas?" Umma ta harareta "Wane irin zuga kike mata ne, kina son Baffan yai fada ne ko yaya?". Rahima ta saki ajiyar zuciya "Ni nama kosa ta tafi gida hakan nan tunda tazo ta isheni da surutu har ciwon kai ya kamani." Iyayen suka kalleta cikin tausayi suka ce "Rabu da wannan babbar gwazar kinji sannu, nemi magani kisha ki kwanta ki huta." Maryam tace "Hhmmm bari dai in zo in gudu tunda sauran girmana tunda taron dangine abin." Rahima tayi murmushin cin nasara watau ta danawa Maryam bom. Cikin wasa da dariya suka ci gaba da hira har Alh Abbas yazo dauka matarsa, ya shigo ya gaida surukansa kana ya dauki Walida da tayi barci ya sallamesu ya fita. Rahima ta zubawa 'yaruwarta kayan shafan hade da turmin super ta mika mata, Umma ta diba Mata tsarabar Gumel sannan suka fita Rahimar na rike da kayan har wajen motarsu ta bude ta aje mata su a baya. Alh Abbas ya leko da kansa ya fara tsokanarta "Ni fa naji kamshin amarci.". Tace "Amarya za kayi ba labari?". Yace "Amaryar dai tadan kanta." Maryam tace "Rabu da ita Alhaji Wai Kai zata yiwa siyasa, bari mu isa gida kaga kayan da angon ya fara kawo toshi ka gani." Yace "Ki bari don Allah?". Ta amsa "Zancen kake so kenan." Ta juya wajen Rahima 'yaruwa kije ki kwanta karki wani wahalar da kanki shan kwayoyi kinsan dalilin ciwon kanki ba ruwana da akai min kazafi." Alh Abbas yace "In don ciwon kaine meye na raki kinada likita a hannu, hala bai San amaryar bata jin dadi bane?" Da taga sharrin nasu zaiyi yawa ta juya fuu tace "Mu kwana lafiya, sarakan sharri." Yaja motar Yana dariya. A dakinsu sun dade itada Umma suna hira, tun tana kaucewa har ta gaji ta kalli Rahimar maganar na cin ranta tace "Ashe yau likita ya zo." . Ta amsa a ciki "Eh ya taho Umma ko da yace dolene a garesa, wallahi Raina ya baci kwarai da furucinsa tunda nima ba son nike yi ba, Zan fi farin ciki idan Allah zai hadani da wani daidai Ni." Ta share hawaye Umma ta matsa kusa da ita ta kama hannayenta ta rike "Haba Rahima bai dace kin rika gaba kina dawowa baya ba, mun riga mun gama magana kince min kin amince yanzun ya kike son sakawa zuciyarki damuwa da bacin rai a banza? Ko wane hali ya nuna ai ya zan shiririta tunda gashi ya biyoki har gida ya baki mutuncinki na diya mace Kuma ki tuna ba fa mu iyayenki muka nema masa ke ba, daga can wajensu batun ya taso don haka bai isa ya wulakanta mana ke ba, kina da damar bugun gaba diyar Umma don haka share hawayenki kinji, muna nan muna adduar idan babu alkhairi a cikin al'amarin nan Ubangiji ya musanya miki da mafiyinsa." A nan ta danji dadi tace "Allahumma Amin Ummana, nagode." 08/09/2020, 23:11 - Anty saliha.....ˆRAHIMA...doc by jami 20 Dr Haseeb ya dade tsaye cikin office dinsa yana jangen motocin dake kara kaina ta windon amma kallon kawai yake tunanisa ya kasu. Na farko yana tunanin rabonsa da gidansu Rahima kwanaki uku kenan kacal amma zuciyarsa na kwadaita masa sake komawa ya ganta don wanke laifin kalaman da ya fada mata wadanda basu dace ba. A hakikanin gaskiya ya yaba da hankalinta, amma addinin data rike hannu biyu ya fara burgesa. Tunaninsa na biyu ya danganci matarsa Zuwaira, wajibi ya bata hakkinta ya fada mata halinda ake ciki na Shirin auren matar kaninsa, kana ya zama dole yaje ya nemi shawarwarin da suka dace wajen abokin mahaifinsa shahararren malami don Kara tabbatar da alkhairin auren, sai ziyartar surukinsa mahaifin Zuwaira saboda kar yaji daga sama ya dauka zaiyi auren ne don yaci amanar diyarsa." Bai san abinda yasa duk cikin wadannan tunanin zuciyarsa tafi karkata da son zuwa gidansu Rahimar gashi bai San dalilin da yasa da duk ya tuna yai mata alkhairi ya kanji wani irin farin ciki ya lullubesa ba. Itama Hajiyarsu taji dadi, tunda hakane kenan kafin ya sake komawa shiga boutique ya gansa.... Ya nutsa har baiji bude kofa da shigowar abokin aikinsa Dr Kabir office dinsa ba saida ya iso daf da teburinsa waya Kuma tayi ringing, kana ya dawo hayyacinsa yasa hannu ya daga wayar dake bisa tebur ya fara magana da harshen turanci kafin ya juya harshe zuwa larabci, sin dau lokaci suna magana da Wanda ke wancan bangaren kafin suyi sallama Ransa a bace ya kalli Dr Kabir yace "Dr Taariq ne daga Riyadh Wai suna neman taimakonmu by nextwk sabida suna da patient da patient da yake cikin *coma* suna tunanin zai sami amnesia idan ya farfado . Dr Kabir ya dan sosa keys "To ai wannan aikin kane Dakta." Dr Haseeb ya zauna ya jawo wani file yayi rubutu ya mayar ya rufe ya ajiye gefe sannan yace "Gaskiya I have commitments next week, so I think they've to do without me this time.". Dr Kabir ya zauna shima yace " Kana ganin in an kyalesu an kyauta kenan? They relied on your services ka sani.". Ya dago Kai ya kalli Dr Kabir yace "Nasan haka Dakta amma inada wani uzurine next week din, Ina sa ran a daura min aure by then kaga kuwa da wuya in sami yin abinda suke so." Dr Kabir ya bude baki cike da mamakin da al'ajibi don ko kusa bai taba tunanin Daraktan nasu zai Kara auren ba... Yayi murmushi ya daga masa hannu "Don't be surprise, kasan shi aure nufin Allah ne, sai kaga Wanda ya shafa ma bai taba mafarkin faruwansa but idan Allah ya rubuto mutum baida wani dabara " Ya gyada Kai "Kwarai da gaske, may I then offer my congrts Sir?" Cewan Dr Kabir. Ya sake daga masa hannu "Thanks a lot, by the way mahaifiyar yaron nan Abdul da ka sani amaryar." Yaga ya fadada murmushinsa sabanin yadda ya zata, ya Kuma Kara da fadin "Wallahi kayi abinda ya kamata, Allah ya sanya alkhairi " Dr Haseeb yai ajiyar zuciya "Nagode sosai Dakta, I really appreciate your support and prayers." Yace "Haba ba komi, Ni zan shiga office, batun tafiyar a bari a ga abinda haki zai yi ko?" Ya amsa "Gaskiya sai yadda na gani still a shigar da tafiyar cikin schedule dinmu mu gani.". Yace "Ba damuwa Dakta." Ya fita ya bishi da kallo, yasan yanzun batun auren nasa zai karade cikin asibitin. Yau kwanakinta takwas kenan da dawowarta Umrah amma basu yi zaman ko rabin awa ba tareda mijinta, ita wannan hali na Dakta na daure mata kai kuma ta fara gajiya don haka ta kashe ta tsare dole yau ta saurateta su tattauna problems dinsu, idan Kuma yaga bai auren ya gaji ne y sauwake mata taje ta nemi wansa zai san darajarta ya rinka kulata, amma Ina amfanin zaman aure irin nasu? Duk da tasan yawanci laifinta ne, zuciyarta taki amincewa, to yaushe zata yarda ta dorawa kanta laifi haka siddan. Ko da ya dawo gidansa bai taba tunanin zai sameta a gida ba tunda Allah yayi ta mai yawon tsiyace. Doguwar riga ce a jikinta Wanda duk da ta rufe tun daga hannayenta zuwa kafafu shara-sharar yadi ne marar kauri dake nuna duk ilahirin surar jikinta, kallo daya yai Mata ya kauda Kai, ta amshi briefcase dake hannunsa tare da rungumarsa "Sannu, ka dawo da wuri lafiya?" "Lafiya." Ya amsa mata yana tafiya zuwa bedroom dinsu domin yai wanka." Zuwaira ta hada kayan abinsa a bisa carpet saboda bai cin abinci bisa dining table, ya fito sanye da kananan kaya a jikinsa Yana zuba kamshi, ya zauna kafin ya fara cin abinci ya tambayeta "Ina su Khalifa?" Ta amsa "Suna can gida." Ba Kara ce komi ba, ya karbi plate din data shakare da shinkafa da miyar data dafa, yayi bismillah ya saka cokali daya a baki ya tauna ya hadiye da kyar, yaja tsaki ya aje plate din yace "Sabida Allah Zuwaira a matsayinki ta mace baki iya sarrafa wani nau'in abinci bane sai shinkafa da miya kullum, ta yau ma bata nuna ba, miya ga tsami sai kace ba mace ba?" Ta harzuka nan take "Yauwa daman maradinka bai kunya ai, kai kenan babu ranar da zan dafa abinci kaci lakadan ba tareda complain irin na sauran maza ba, ni kenan komi ban iya ba a idanunka." "Ni bance ba ki iya komi ba, ina fada miki ki rinka kwantar da hankalinki kina abinda ya kamata cikin gidanki, ai ga abincin nan dauki kici kiji Mana idan zuwa anjima indigestion bai kamaki da heart burn basu dameki ba... Tayi shewa "To idan kwarnafin ya taso ba sai ka bani magani ba? Kaga idan ba zaka ci ba kace da inda kake zuwa kana ci ka koshi, to da hakan kuwa gara ka aurota zaifi min nono fari." Ya shareta bai ce komi ba, ya dau remote ta canza channel zuwa CNN yaci gaba da sauraren news. Ta mike ta kwashe tarkaccenta ta mayar kicin ta dawi ta zauna, zuwa can tace "Ina son magana da Kai." Yace "Hhmmm Ina saurarenki bismillah.". Ta kura masa ifo na wasu dakikoki tukunna, ta gyara zama tace "Tambayarka zanyi, saboda Allah irin zaman da muke yi ya dace da tsarin rayuwarmu, kana ganin shine daidai?". Bai dagi ba ya kalleta ba ya amsa "Wane irin zama kike nufi?" Taji haushin amsar da ya bata tace "Ai baka ma sani ba ko? To in fada maka, Zama ne muke yi tamkar ba ma'aurata ba, kowannanmu na harkarsa, ba shakuwa, baka San halinda nike ciki ba, nima ban san halinda kake ciki ba, in har ya zama dole muyi magana bata kaiwa ko Ina m gayyar take watsewa, ko yaranmu baka ja su a jiki ba, Ina iya cewa ma yadda ka shaku da wannan yaron Abdul baka shaku da 'ya'yan cikinka ba, basu Sami wannan gatan ba." Yaji tayi shiru, ya aje remote ya fusknceta " kin gama?" "Eh ta amsa. Yace "Tunda Allah yasa yau da kanki kie son ayi batun sai ince alhamdulillah do n many times nayi yunkurin mu zauna mu tattauna issues dunmu kika ki yarda kika nuna abinda ke faruwa duk laifinane, Amma tunda kin yarda akwai problems a zamantakewar mu sai ki fadi muji a Ina na kuskureki? Zuwaira tace "Baka ji abubuwan dana lissafo bane?" Yace "Oh sune kike ganin problems dinmu kadai? To bari ni in bayyana miki ko ince in baki amsa ki hujjojina na sanya miki ido da nayi. Na farko duk matar arziki tana nunawa matukar kulawa da harkokin maigidanta na yau da kullum, har idan akwai shawarwarin da zasu amfaneshi ta bashi , idan gari ya waye ta kula da dawainiyar breakfast dinsa Dana yaranta in akwaisu, idan zai fita aiki tayi masa adduar fatar alkhairi, su rabu cikin farin ciki su yini begen juna, idan ya dawo ya sameta cikin suturar mutunci, ta tarbesa da da abinci masu gamsarwa, idan lokacin barcinsu yayi suyi hirarsu Mai sanyayar da zukatansu har in suna cikin mood su kusanci juna ta hanyar da Allah yai mana umurni Kuma Manzon Allah yai mana koyi a addinance sabida hakan zai haifar musu da nishadi da Kara musu shakuwa ba a kwana ana jin haushin juna ba. To ke kuwa duk safiya na Kan tashi ne in barki kina barci baki sa niyyar tashi ba ma saboda kinada rauni a addinin naki, batun hidimata dana Yara kuwa kin halastawa mai aikinki tayi Mana, lokacin da na dawo gida ba lale in sameki ba, kin dau mota kina garari a gari, ba Kya gidan wannan buki ba Kya gidan wancan abokiyar kasuwanci. Idan anci saa kin zauna a gidan, Zan shigo in taras dake da kawayenki ne yan duniya, wadanda suka fi karfin mazajensu iskar duniya na dibansu. Abincin da kikan girls so da yawa nakan gwammace zuwa ci a hotel da inci naki sabida baki zauna kin kula yadda mutum zaici hankali kwance ba, ke kanki ba Kya cin abinda kika dafa a tukunyarki kin gwammace kullum ki aika a sayo miki nama ki ci. Batun rashin kusantar yara da kike kin basu damar zama cikin gidansu ne? Ko kuwa kin kaisu wajen mahaifiyata tace na zata iya ba? Nasan gidanku kike kaisu but mun san zama gidan ubansu yafu musu fa'ida. A nan ta hayyayako "Ai da tuntuni ka nuna rashin amincewarka dana rinka barin maka yaranka muga tsiyar da zaka basu a gidan.. Yayi wanumi dan murmushi "Duk takamarki kudi ko? Gidanku ba matalauta bane, to Ni dinma ba matsiyaci bane. Yanayin aikina yasa na amince miki Kan ki rinka kaisu gidanku din sabida da kina zama a gida da yaran basu rinka watangaririya ba. 09/09/2020, 14:13 - Anty saliha: ...RAHIMA...doc by jami 21 Dr Haseeb yaci gaba da fadin "Shin kin taba tunanin kai yaran nan wajen Mahaifiyata su rinka debe mata kewa? Ah ah ke sam babu ruwanki da harkar dangina sai wadanda suka zama miki dole, yau satinki nasa rabonki da gidan Hajiyar? 'yanuwana sunyi korafin kin kama 'ya'ya kin rike basu san kowa ba sai danginku, sun gaji da complain sun hakura. Kina korafin bamu shaku da juna ba ko? Ta yaya hakan zai kasance bayan kin nunawa duniya mutanen da kike hulda dasu a waje sun fini mutunci da matsayi a zuciyarki, ya za kiyi tsammanin ni Haseeb in zama second best a rayuwarki? To bari ayita ta kare yau Zuwaira, shin kinsan nasan fa duk shigi da ficin da irin mu'amalar da kuke yi da wasu mazan da sunan kasuwanci in and outside Nigeria? That's why naja baya dake, na sakawa sarautar Allah ido, duk ranar da Allah ya kawo karshen aurenmu shikenan don na gaji da zama da wace zuciyata ke mata zargin fasikanci." Tana jin yai shiru ta tuma gefe ya dafe kirji tareda zaro idanu "Kazafi Kuma za kayi min Haseeb?" Ya girgiza Kai "Kinji Kuma daya daga cikin halayenki dana tsana *karya* duk maganar da zaki Fadi aka yi nazari aka tace sai an gano karyarki tafi gaskiyarki yawa a cikinta, kinga bani ba har Allah daya haliccemu ya la'anci mai yinta, yai hani da yinta, kince Kuma kazafi wane irin kazafi ga dahir nan kowa na gani? Ba ma sai an kaita da nisa ba, fara tuhumar kanki tun daga Kan irin shigar da kike yi, yadda kike gudanar da tsarin rayuwarki, na mijinki da zuriyyarmu, yaya tarbiyyarki ke tafiya, shin kina kokarin tsare abubuwan da Allah ya umurceki kiyi, kina gujewa abubuwan da suke munkar a gareki? Look at you now, just look at irin shigar da kika yi a matsayinki ta musulma, fara da gashin kanki, gaki nan roba ce ko yizgar doki ko wace tsiya ce kika Kara a kanki oho wai ke gayu, gayu ko yin biris da hanin addininki, ke kin isa kiba kanki abinda mahaliccinki bai azurtaki dashi ba? Dubi tun daga yatsun kafarki zuwa hannu, yanke kumba bai cikin tsarinki abinda Manzon tsira yai mana koyi da yanketa duk ranar jumma'a don inganta tsabtar jikinmu da samun lada saboda ita din najasa ce, wani lokaci har fenti kike musu wai duk cikin gayu tunda ibadar bata tsaya miki bane, bki ma san hukuncin barin lam'a wajen al''wala ba, kalli suturar dake jikinki, gata nan har Kara amma bata kare a hango yanayin surar jikinki ba.... "Karfa kaga laifina a nan, wallahi kai nikewa kwalliya saboda idan banyi ba ka isheni da korafi.' Ya kalleta wani iri "In don nine kike sabon Allah irin haka na yafe. Duk matar data san mutuncin kanta ba zata rinka irin shigar da kike yi ba, idan Kuma domina kike, ai ko Ina kasar ko ba nan hakan kike shigarki, haka kike fita duk inda kuka ga dama keda kawayen naki, mutuncinki a zube, na iyayenki a watse, Ni Kuma duk irin matsayina a garin nan wasu na min kallon namijin hotiho wace matarsa tafu karfinsa, to ba fun karfina kika yi ba, Allah ne shaidata tunda naga kin fara canza salon rayuwarki na fara yi miki nasiha, baki ddauka ba, na gaji na hadaki da iyayenki duk a wofi,maimakon ki canza sai kika Kara fekewa, Kika ce wai Ina neman hadaki dasu ne, to sai na gaji na sanya miki ido kije duniya taci gaba da rudinki, shaidan yaita busa miki sarewa kina taka rawa, abinda na sani gida biyune, da inda zamu tafi komin dadewarmu a duniyar, yau Ina Rabiu, kina ganin lokaci kalilan Allah ya rabamu farad daya, kafin shi mutane miliyan nawa suka rigamu gidan gaskiya, mu din ma ba zama za muyi ba, tun muna jin na wasu wata rana za aji namu, ke don Allah ko tunanin mutuwa ba kya yi? A kance wanda duk yai nisa bai jin Kira, Zuwaira ta fara nisa, tafiyar ta tafi sai nema mata shiriyar Ubangiji saboda rabi -da rabi take saurarensa, hankalinta ya dauku da tunanin irin cakewar da zata yi wajen bukin wata kawarsu da za ayi a Hotoro, Kuma a kullum ta kanso tayi shiga ta burgewa da tsadaddun kaya don ta nunawa duniya ita 'yar business ne, matar shahararren likitan da ake damawa dashi a kasarmu Dr Haseeb Junaid. Ya lura hankalinta bai tare dashi, ya kakkabe rigarsa ya tashi ya dauko key din motarsa yai bar mata gidan Bai zame ko'ina ba sai gidansu Zuwaira ya wuce Kai tsaye cikin gidan y gaida matan gidan su uku, sarakuwarsa ce Uwargida sai masu bi Mata. Dr Haseeb ya koma falon surikin nasa ya zauna Yana jiran fitowarsa, nan ya tsudumma tunani, kwakwalwar sa ta tariyo masa tarihin rayuwarsa tun yana karami da dalilin haduwarsu da Alh. Muhammad.. Shi dai an haifesa a unguwar Galadanci, mahaifinsa Mal Junaid rikakken dan boko ne daya kware a fannin kimiyya, malamine a jami'ar Bayero. Ya mallaki mata daya Kaltume da albarka da guda daya tilo, sun day dogon lokaci basu Kara samun haihuwa ba a dalilin haka Mal ya nemi auren wata bazawara Kuma daliibansa ya aure. Tun tarewan amaryar ta nuna ita babu ruwanta da Uwargidanta balle wani danta daya tsone Mata ido. Yaron ya zama wajen uwarsa kadai yake samun sararawa wace ganin halin ko in kula da uban ke nunawa danta bayan ya Kara auren yasa ta ajiye kunya ta rungumi abinta. Yana kara shekaru yana fahimtar yadda mahaifinsa ke yin nesa dashi Wanda da ya dauka kunya ce irin wanda iyaye kanji na dan fari but daga baya ya gane wata irin kiyayyace da bai San mafarinsa ba Abinda ban mamaki ace farad daya uban daya haifeka ya dawo bai kaunarka, duk da haka daga Kaltume har Dan basu danganta hakan da komi ba. Amaryar malam ta fara haihuwar diya mace ta rasu, tun daga lokacin Abdul Haseeb ya fara karaya da lamarin mahaifinsa domin rashin jaririyar nan da akayi tamkar zautu yayi, bayan nan Allah ya bata haihuwar diya biyar, mata biyu, maza uku, Allah ya sake amsar matan ya bar Mata mazan. Duk da ya kasance shine babba, a kullum mafarkin mahaifinsu ya ta'allaka Kan kanninsa ne kawai na su din su gajeshi fannin karatu. Ba zai taba mantawa wata rana suna zaune gewaye da uban suna hira,kowa na fadin abinda yake son ya zama idan ya girma, Abdul Haseeb yace shi likita yake shaawar zama maimakon uban yaji dadi ta bashi kwarin gwiwa sai ya hantare sa ya daka masa tsawa yace "tafi can da wace dakusassar kwakwalwar? An fada make batcu ake a tashi a zama likita? Ko da wannan tsamin bakin da in inar taka ce zaka zama likita? A lokaci bai wuce shekaru goma sha biyu amma yaji zafin gorin da mahaifinsa yai masa, kalamansa sun sa hawaye masu zafi gangaro masa wadanda uban ya lura yace ya tashi ya bashi waje .. Kaltume ta gansa yana kuka ta tambayi dalili yaki fada Mata don ta fara wayon gudun bacin ranta, sai dai tun daga ranar ta Kara zage damtse ya daukarwa kansa alkawarin zama wani abu a rayuwarsa duk wuya iya wahala, ij karatu nasa mutum yai suna to sai yayi suna gabas da yamma kudu da arewa sai an San da zamansa. Ya dage da karatu ita Kuma uwa ta dage da neman maganin gyaran tsamin baki da in Ina da ya tashi dasu, duk inda taji magani zata nema ko Saida wani Abu nata ne ta amso ta bashi bayan adduoi da yake karya kummalo dasu,idan zai kwanta barci su din zasu masa bargo. Kullum cikin sanya masa albarka da Kara masa kwarin gwiwar cin ma nasarar abinda yasa a gaba take. Tsakaninsu da mahaifinsa ba wani canji haka yasa yaja baya dashi da 'yanuwansa da tun farko ba a nuna musu muhimmancin zumunci da junansu ba balle su kusance sa." Yayi kokarin gano dalilin rashin samun kyakkyawar kulawa daga mahaifinsu abu yaci tura a yayinda uwar ke kokarin hanashi kullatar mahaifinsa da komi cikin zuciyarsa tunda itama ta kasa gano komi zaman hakuri take duk da tana zaune dashi fisabilillah Kwatsam aka wayi gari malam ya saki Kaltume har saki uku, wannan Abu ya tsayawa Haseeb a rai, a nasa wautar yaso uwar ta zauna gidansu komi wahala amma zama ya kare. Tana gama idda ta sake aure inda Allah ya azurta ta da Yara biyu maza, Hayatu da Rabiu. Ba a taba tabbatar da hazakarsa ba saida ya shiga jami'a ya samu gurbin karatu kan koyon aikin likitanci. A nan Abdul Haseeb ke matukar neman taimako da dukkan kwarin gwiwar da ya dace iyaye da duk masu kaunarsa su bashi sai dai ina kana uban yayi alfahari da godewa Allah da ya bashi hazikin yaro amma Ina ! Bai samu ba, gashi uwa duk ta gama sayar da dan abinda ta mallaka a Kan neman ilmin da kwara daya tilo, hatta da yar gonar da tacu gado ta sayar anyi amfani da kudin basu isa ba. Shi Kuma bai son matsa mata saboda bai da kwanon abinci gidan ubansa, duk wata lalurar ci da sha da sauran abubuwan bukatunsa sun ta'allaqa ne kadai Kan mahaifiyarsa, tausayinta yake har dai da yaga mahainsa ya dara mahaifin su Hayatu karfi sosai, Kuma mahaifinsa na daukar nauyin hidimar sauran 'yanuuwansa shi kadai yake yiwa wannan yankan kaunar. Wata rana kudun sayen handout yai masa teahe ya rasa yadda zaiyi dole ya nufi wajen uban neman taimako amma me zai faru, fada ya rufeshi dashi yana fadin "Wa yace kaje ka zabi course Mai sa kashe kudin tsiya kassn ba Kai kadai na haifa ba don haka ba zan talike a kanka ba, ya wurgeshi da rabin kudin yace karya sake zuwa ya dameshi don da yai nasa karatun babu Wanda ya taimaka masa kwadago yayi shima yaje yayi ya nemi nasa. Ance gayawa Mai zuciya buki ba Mai dukiya ba, wadannan kalamai sun Kara zaburar dashi sunsa masa rai kwarai sun Kuma tunzura shi, ya zuciya, irin zuciyar da ake son yaro yayi ya ajiye girman Kai da tunanin shi wani ne ya tashi ya nemi na kansa. Ya fara yawon neman abinyi idan ya gama lectures ya shiga gari neman aikin, duk inda yaga ana gini ko aikin bulo ya nema ya tube yayi a biyashi, bashi wajen kafintoci bashi tashar mota wajen yun dako. Idan ya samu kudin aikin yinin ranar ya Kan raba uku, Kashi daya ya mikawa uwa, Kashi na bukatun yau da kullum Kashi gudan a jefa a asusu na hidimar karatunsa ne. Wata rana inda yake aikin bulo suka samu kwangilar ginawa wani dan kwangila sabin gida, a cikin maaikatar da aka dauka har dashi ga jarabawarsu ta matso ga bukatar kudin a tare dashi don haka ya kwashi takardunsa ya rinka tafiya dasu site din inda da ya samu lokacin tsaya sai ya duba tukunna kana yaci gaba da aikinsa. Lokaci lokaci Alh Muhammad Kan ziyarci site din don ganewa idanunsa yanayin aikin da ake masa, a nan ya hango wannan saurayi inda ta dade yana nazarinsa Yana karatu a natse, sau uku kenan yana ganinsa, haka kawai yaji yana son jin labarin yaron. Yasa aka Kira masa shi, ya kwaso littafansa ya zuba a jaka ya iso inda ake nemansa. Yana zuwa ya durkusa gaida Alhajin amma ya mika masa hannu su gaisa, ya dan tsaya saboda jin nauyi, Alh. Muhammad ya riko hannunsa Yana dariya, ya tambayi sunansa ya fada masa, ya sake tambayar dalilinsa na yawo da littafai Yana aiki ya bashi amsa da "Ina neman na kaina ne." Ya sake tambayarsa wanene mahaifinsa ya fada, nan da Nan ya gane don shi din sanannan mutum ne, Alh Muhd yai mamakin jin sunan mahaifinsa da yadda ya bar dansa na kwadigo bayan Allah yai masa rufun asirin da zai taimaki wani ma ba dansa kadai ba. Yana son jun ainihin tarihin yaron nan don haka ya mika masa katinsa yace ta samesa a gidansa a ranar, ya karba yana mamakinsa dalilin da yasa yake son ganinsa tareda alkawarin zuwa da dare. Karfe takwas na dareya isa gidan Alh Muhammad, da alamun an bada labarin zuwansa domin yadda maigadi ya tarbesa yai masa jagora har falon maigidan. Alh. Ya mike ya sake Mika masa hannu suka gaisa kana ya bashi umurnin ya zauna ya zabi abinda zai ci cikin nau'ikan abincin da aka baza a tsakiyar falon. Yasha lemu kawai yace ya koshi, Alh ya jima yana kallon yaron da ya shiga zuciyarsa farad daya ki domin baida da namijine ohom. Yaso yaji dukkan labarinsa but Abdul Haseeb ba haka yake ba, bayan miskillanci yanada rike sirrinsa domin ba ayi ciki don tuwo kadai ba, to ma haka kawai ne daga haduwa da mutum bai San kowanne irine bane zai zayyane masa sirrinsa, no bai san abinda zaije ya komo ba, bai san me mutumin ke nufi dashi ba. Alh Muhd ya tabbatar da ba zai Kara jin komi daga bakin bakonsa ba ya hakura ba don ya gamsu ba sabida har zuwa lokacin Yana mamakin uban da zai samu hazikin yaro kamilalle irin Haseeb yai biris da al'amarin neman ilminsa, da daure kai sosai amma tunda yaron ya dage kan cewan Yana kwadagon don ya taimaki kansa ne ya kyalesa a haka yai masa taimakon da zai iya yi masa. 09/09/2020, 23:56 - Anty saliha: ..ˆRAHIMA ...doc by jami 22 A ranar yaiwa Haseeb albishir din cewan saboda ya yaba dashi matuka gaya zai taimaka masa Kan harkar neman ilminsa tun daga kasarmu zuwa kasashen ketare har ya cimma burinsa. Yace Yana son ya dau masa alkawarin zai amince ya zama dansa saboda shi bai taba haihuwar da namiji ba, 'ya'yansa takwas duk matane. Bai yi saurin amincewan ba ya nemi ya bashi kwanaki uku yaje yai shawara tukunna, Alh.Muhd ya amince ya kawo kudi ya bashi yace yai kudin mota. Ya amsa yai godiya ya tafi. A ranar ya sallama gidan mijin mahaifiyarsa Yana kiransa Baffa, ya shaida musu duk abinda ya faru, Kaltume ta tsaya shiru ta rasa ta cewa, maigidanta yace mishi "Kaje ka amshi taimakon nan da hannu biyu ka rikesa da zuciya guda bisa amana tareda adduar Allah ya taimakeka bukatarka ta biya." Kaltume ta nisa "Anya? Ina jinjina batun mutumin nan Malam, kana ganin za'a kwashe lafiya, ka fa san halin mutanen zamanin nan na mu." Mal. Sunusi yace "Insha Allah na komi, Ubangiji fa ba yadda bai iya tsara al'amarinsa ba, idan cikin hikima da basirarsa ya kaddaro Alh. Muhammadu ya taimaki yaron nan ba makawa, ai shine kaddarar, zaki ga wani mutumin ba ko a mafarki tunani bai taba kaika cewan zaku hadu ba sai kwatsam Allah ya hadaku a shiga cin gajiyar juna. Kai dai har kullum gargadina gareku shine Wanda duk Allah ya hadaku dasu ku zauna dasu tsakani da Allah da zuciya daya, banda hassada ko kyashi, Banda biyewa zuciya ko mutanen duniya 'yan Kai kawo su shiga tsakaninku, banda daukar jita-jita. Ka sani daukaka Allah ke yiwa mutum ba kowa ba, idan ya so ka daukaka iya hassadar makiya basu isa su hana ba, kazalika in baiyi nufu ba ba Wanda ya isa ya kaika inda Allah bai Kai ka ba. Banda wulakanta mutum da kowacce irin halitta, banda kwadayi don yana janyowa mutum wulakanci da kaskanci, kayi imanin komi ya same ka cikin rayuwarka rubutacce ne daga Allah, wani ko wata, mutum da aljan basu isa suyi maka abinda ba Allah ya rubuto zai faru dakai cikin *Lauhul Mahfuz* ba. Ka riki gaskiya duk inda ka tsinci kanka cikin kowanne yanayi, Ina gargadinka daka rike addininka hannu biyu, ko da Allah zai daukaka nan gaba ta azurtaka karka butulce masa son duniya ya shagaltar dakai bauta masa gwargwadon iyawarka... Ka rike mutumin daya taimakeka da hannu biyu, ko da ace baiyi maka komi ba kaunar daya nuna maka ta isa domin duk Wanda ya kaunaceka irin haka, ba don wani Abu naka ba sai domin Allah ya gama maka komi, karka sake samun duniya ma'ana dukiya ta hadaka dashi, Kar ka zame masa mutum mugun icce. Da wadannan nasihohi masu mugun shiga jiki Abdul-Haseeb da mahaifiyarsa suka yi na'am da Alh. Muhd. Shi kuma can ya kosa yaron ya dawo yaji ta bakinsa domin har ya nemi alfarmar gwamna cewan yana da d'a idan mai girma gwamna zai tura hazikan dalibai karatu kasashen waje a saka sunansa. Gwamna ya amsa da alkawarin idan lokaci yayi nan da watanni uku zai sanar dashi. Lokacin da Abdul Haseeb ya koma gidan Alh Haseeb kansa ya daure, an nuna masa ya riga ya zama dan gida, kowa sai ji dashi yake kamar daman a gidan yake tafiya yayi ya dawo, hidimomi salamu Alaikum. Kaltume da maigidanta musamman Abdul Haseeb ya kaisu yi masa godiya shi da iyalinsa. Kafin watanni ukun Alh Muhd yaja Haseeb a jikinsa sosai ya Kuma bashi labarinsa tas, shima yace ya taso cikin wahala sakamakon iyayensa sun rasu tun Yana karami amma daga dangin uwa har na uba aka rasa Mai daukar nauyin karatunsa, nan ya shiga neman abinda zai hucewa kansa takaici, ya fara da yiwa wani attajiri kiwon doki, ya kanje ya yanko ciyawa ya share turkensa ya kula da dawakin ana biyansa, daga nan ya koma sayar da sigari, da goro, minti ashana da sauran tarkacce a tire a tashar mota, daga nan Allsh ta tarfawa garinsa nono,ya kafa dan tebur daga nan sai shagon kayan masarufi, daga nan Allah ya daga shi sannu-sannu ya fara kwangila tareda taimakon Allah, Ubangiji ya daga har ya Kai matsayin da yake ciki yanzun. Ya auri mata uku bai Sami haihuwa da wuri ba, da ya samun sai Allah ya azurta shi da diya Mata. Alkawarin da yayi suna gama sakandire zai aurad dasu, Amma duk ranar da Allah ya bashi d'a namiji sai inda karfinsa ya kare.. Zuwaira ce diyarsa ta biyu, Mai bala'in kama dashi saboda hakane yake sonta kwarai da gaske, irin son da ya janyo mata sangarcewar. A lokacin da ya hadu da Haseeb duk suna makaranta, Zuwaira na aji uku kacal. Duk wani takalihunsa ya koma hannun Alh Muhd, duk da haka bai saki jiki ya daina buga-bugan sa ba. A hankali ya fara koyon hanyoyin kasuwanci ya rinka aiwatar da abinda ya saukaka a garesa. Yayin da gwamnatin jihar Kanota dauki nauyin fitarsu zuwa kasar *Neatherlands* domin zama kwararren likita. Abdul Haseeb ya zama *Neurologist* ya zamewa uwa da uba dashi kansa Alh Muhd din d'a daya tamkar goma, ya cika dan halas domin matukar girmamawar da yake masa yasa koda yai masa tayin auren diyarsa Zuwaira bai musa ba duk da Yana ji da ganin irin gurbatacciyar tarbiyyarta. Wajen hidimar auren Alhajin yaso daukar nauyin hidimar komi, Abdul Haseeb yaki yarda yace hakkinsa ne ya dau nauyin iyalinsa. Tunda Allah ya azurta shi yake dawainiyya da iyaye, 'yanuwa dana matarsa. Da Allah ya tashi ikonsa ya aikowa Mal Junaid hadarin motar da yai sanadin dakushewan kwakwalwa, bai iya tuna kowa da komi, hatta mata da 'ya'yan cikinsa. Asibitin Murtala aka kwantar dashi lokacin bai bude nasa ba. Duk da haka shi ya dau nauyin hidimar komi Wanda yasa matar uban kuka da hawayenta sharaf -sharaf tana roko gafarar Kaltume da danta, Wai Ashe tun kafin ta auri Mal Junaid tayi asirin farraqa shi da mahaifin gudun Wai kar tazo ta haihu ya nunawa Haseeb fifiko (Kunji wani rashin tunanin) to ta cimma burinta amma ta dawo tana dana sani wace a baya takan tsaya inji hausawa. Shin mu mata bama tunanin cewan duk yaron da aka tsana cikin gidansu Allah na iya daukaka shi ba? Shin bamu tunanin tunda bamu muka halicci mutum ba bama iya tsarawa wance ko wane abinda zasu zama a rayuwa? Allah ya kiyashemu aikata aikin dana sani, domin da mutane sun san hassada takin arziki ga Wanda ake yiwa da ba ka yi ba. Ta roki Kaltume da danta gafara sun yafe mata to shu mijinta data ha'inta yake kwance bai san inda yake ba fa, wanda ya rasu kwanaki uku da yin hatsarin, wata shari'ar sai gobe kiyama. Bayan rasuwar mahaifinsa ya dauki nauyin kulawa da dukkan hidimomin kanninsa da uwarsu. Bayan an raba musu gado ya budewa kowannansu shago a kasuwa saboda sun nuna sunfi son kasuwanci ba karatu ba balle aikin gwamnati, ko da aurensu yazo ma shi ke kan gaba wajen basu gudumuwarsa, uwarsu sai godiya take tunda ta dawo hanya ta tuba Allah ya sahale mata bakin cikinta kullum cikin istigfari, tsakaninta da Haseeb sai san barka. Mahaifinsu ya rasu da shekara guda tal Allsh yaiwa mijin mahaifiyarsa rasuwa, Haseeb yayi babban rashi yai kukan rashinsa, a dalili da duk fadin duniya su hudu kawai ke zaunar dashi su fada masa gaskiya, daga mahaifiyarsa sai shi sai Alh. Muhd sai kuwa abokin mahaifinsa daya saba dashi tun Yana zuwa daukar karatun allo, to ko da ya girma bai yada malaminsa ba Bayan ta gama takaba ne ya saya mata gida a Yakasai da yake daman gidan Mal. Sunusi na tarayya ne, shekara na zagayowa ya kaita ta sauke faralli, ta dawo ta bata jali tunda ta nace sai tayi sana'a. Dr Haseeb Junaid ya saki wata doguwar ajiyar zuciya, ko me yasa brain dinsa tariyo masa abinda ya wuce oho don wasu tuni ya fara mantawa sai fa yau. Tunaninsa ya koma Kan yadda ya rike kaninsa da suke ciki daya, ko girmamawar da suke masa ya isa yai hidimta musu cikin kowanne hali in ya ture batun shakuwar da yayi dasu kenan, su Hayatu na kaunarsa fiye da zatonsa musamman marigayi Rabi'u, ya tuna yanayin aurensa da ya taso a gurguje haka ma haihuwar ashe ba dadewa zaiyi a duniya ba A kullum ya tuna wasiyyarsa garesa inda ya bashi amanar Rahima da Abdul ransa kan dugunzuma ya bacu ya rasa me ke masa dadi a sararin duniya, to sai gashi wai shine da Shirin auren matarsa, babu irin tunanin da bai yi ba kan issue din but tabbas akwai Shirin da Allah cikin al'amarin, yes da akwau hukuncin Malikal Mulk don haka gara ya cire komi a zuciyarsa ya rungumi kaddara. Shigowarsa biyu kenan yana ganinsa cikin zurfin tunani don bai ko san ya shigon ba sai a na uku ya sallama ya fada falon, ya amsa yaga kamar Daktan na share hawaye tunda ya cire glass dinsa, yai kamar bai gani ba ya mika masa hannu suka gaisa."Ka dade kana jira ko afwaan." Cewar surukinsa. Ya manna dark glasses din a fuskarsa tukunna kafin yayi dan murmushi "Ai ban wani dade ba Alhaji". Ya mayar masa. Sanin miskilancinsa da rashin son yawan magana yasa Alhajin baiyi masa shishshigi bai tambayarsa sai abinda yaso fada masa da bakinsa, ganin halinda yake ciki na damuwa ma baisa ya nemi jin ko menene ba har suka yu 'yar hirarsu, zuwa can Alhajin yace "Wai Ina Zuwaira ne tazo ta zubar da yara daga zanje un dawo yau kwana biyu kenan bata ba labarinta?" Ya amsa "Tana can suna hidimar bukin wata kawarta ce, nasan ko zata waiwayesu sai an kare komi." Uban yaja tsaki "Watau ita dai ba zata daina halinta ba ko? Amma ban zargin kowa sai kaina Dana shagwabata, na manta cewan diya mace ce komin dadewa aure zata yi, nasan da wani take aure da tuni ta sako min it's, an taba mace na sanin ya kamata ba kamun Kai?" Haseeb yace "Allah ya kyauta a ci gaba da yi Mata adduar shiriya don tayi nisa Alhaji." Ya nisa "Wallahi tuni na fahimta wace bata damu da yayan cikinta ba ma? Wallahi ko jiya Saida muka yi maganar nan da uwarta, duk dai kuskuren ne, gata ko cuta? Shawarar dana yanke idan ka gaji da halinta ka sakota ko Allah zaisa tayi hankali karta gurbata maka tarbiyyar yaranka." Haseeb ya sunkuyar da Kai "Allah ya tsare, tsakanina da ita babu saki unless haka Allah ya rubuto Mana Ina Nan Ina Mata addua." Alhaji ya girgiza Kai "Duba Nan Dakta wallahi kasan rantsuwar musulmi kenan ko? Idan kaga ba zaka iya zama sa ita ba ka sauwake mata ka huta, nuna haifeta nasan halinta sarai don haka na baka izni, kar kaji nauyin komi Kar Kuma kayi tunanin yadda muke da Kai, tsakaninmu da ban hulda da matarka daban, ni ba zanso ace ka zauna da ita tana cutar ka kana hakuri sabida ni ba, nima na fara gajiya da halinta, uwarta ma tayi fushi da ita muddin Kuma ba zata zauna gidan aurenta tabi dokokin Ubangiji ba bani bata." Ya fara rarrashun tsohon yace "Allah ya huci zuciyarta insha Allah muna fatar ta natsu, may be idan taji zanyi aure." Alhajin yace "Alhamdulillah kamar ka shiga zuciyata, shawarar da nayi niyyar baka kenan ince ka Kara aure ka huta da wahala wannan yar banzan." "Don Allah Alhaji ka daina zaginta kayi hakuri, daman abinda na zo shaida maka kenan batun auren amma har ga Allah bani na nema ba, iyayene suka ga ya dace in auri matar marigayi Rabiu, gaskiya da ban amince ba amma daga baya sai Ina ganin watakila auren ya zama sanadiyyar shiriyyar Zuwaira domin yarinyar tasan addinita na yaba da hankalinta kwarai." "To Masha Allahu haka ake so, Allah yasa ayi damu, yaushe ne daurin auren?" Ya gyara zama "To ai kune masu neman auren Alhaji shine nazo sanar maka gobe idan Allah ya nuna mana sai ku tafi, nan dai Yakasai inda aka daura auren marigayin, daga nan zan nufi wajen Malam Nuhu ne in sanar dashi shima." Alhaji yace "Karka damu amma Ina fatar ba za a dau dogon lokaci ba." Haseeb yace "Nima hakan nike so." Daga nan ya nufi Sharifai gidan Malamin nasa ya shaida masa halinda ake ciki. Malam yai murna ya shiga yi masa nasihohi musamman kan kwatanta adalci tsakanin matan daman tsoronsa kenan tunda yaga yadda mahaifinsa yaiwa Mahaifiyarsa. Malam ya Kara masa da shawarwari da adduoin fatar alkhairi da neman jagorancin Ubangiji. Yana Kan hanyarsa ta komawa gida yana mamakin irin na'am da farin cikin da kowa keyi Kan wannan auren, zuciyarsa ta Kara karfi, nan bisa hanya ta fara tsara yadda yake son a tafiyar da sha'anin amma har sai ya isa gida yaji ta bakin Zuwaira da ita kanta yarinyar da akeyi dominta. 10/09/2020, 06:02 - Anty saliha: ...RAHIMA..doc by Jami 23 Karfe goma sha daya na dare ya isa gida amma har zuwa lokacin Zuwaira bata koma ba, ya tube ya shiga wanka ya fito ya hada ruwan shayi tukunna kafin ya zauna kallon tv Sai sha biyu saura na dare yaji maigadi na bude mata gate din gida ta shigo da motarta. Ko da ta shigo falon bata lura yana kwance bisa settee ba, tana tafe tana 'yan wake-wakenta, sai wani irin kamshin turare Mai shegen haea Kai take, har zata wuce bedroom ta gansa taja ta tsaya masa kerere bisa Kai "Oh ashe ka dawo ban lura da motarka ba." Ance tankawa yabawa biyan bashin matsiyaci, bai ce Mata uffan ba, ta fasa shiga ciki ta dawi ta zauna kusa dashi ta fara kame-kame, kusan minti biyar tana ta surutu ba tareda ya tanka ba ta gaji tayi shuru. Ya kalli matar da suka shafe shekaru fiye da takwas da aure Amma m har zuwa lokacin Nan bai San dadin auren ba, bai San me zai karas ba, ya kanji dai abokansa na hirar hidimar da matayensu keyi musu. Ya sake kallonta ya rasa me zaice Mata, to bata jin wa'azi, in anyi mata fada ta tashi tana masifa tace an tsaneta, idan aka rarrasheta ta zake har tafi da don haka ya zabi yin biris da ita kawai yafi masa alkhairi ya ci gaba da yi mata addua Da taga yaki ce mata komi ta mike zata shige ciki harda sakin dogon tsaki... Takaici ya kamashi kawai ya sakin mata bom "Zuwaira Ina sanar dake Zan Kara aure." Tayi wani irin juyi gaba daya, hankalinta ya dawo garesa sosai taga Yana kwance lakadan kamar bashi ya furta Mata wadannan kalaman masu dacin gaske ba, ta buga kirji "Aure! Aure fa kace?? Ya amsa "Kwarai ba kince gara inyi ba zai fi Miki nono fari?" Ta sake buga kirji "Ni din wace sakaryar macece zata ce da mijinta ya kawo Mata kishiya?". " Sai ke Kuma shawarar taki na dauka." Amsarsa ya sake tunzurata "Oh ashe zargina ya Zan gaskiya da wace ka aje a waje that's why kake wulakanta ni kana nuna min halin ko in kula." Yace "Ni ban wulakanta ki ba, ban Kuma ajiye kowacce mace a waje ba don Ni ba fasiki bane." Tayi tafi " Abokiyar yin naka dai zaka auro a tahi a cakuda min 'ya'ya da shegu." Ya tashi daga kwance da yaji zata wuce gona da iri yace "Kinga karki batawa yarinyar mutane suna, ba wata daban da baki sani ba Zan aura, ai kinsan Rahima maman Abdul ko,Allah yai nufin ita Zan aura " Taji dum amma hakan bai hanata yin shewa ba "Ahayye girma ya Fadi, su Yaya babba anji kunya, to daman kace ka gani ka kyasa tuni ba damar yi masa snatching ne da ransa, yo Ashe duk shan mur da kau da Kai na munafunci ne ana so ana kaiwa kasuwa, to me yasa tun farko bka aureta ka barshi ta aureta. Gaske naga danta ya zama dan lelenka sabida son uwa ke sa na d"a. Amma wallahi ka ban mamaki ka bani kunya, ka rasa matar da zaka aura sai matar kaninka Haseeb, wannan abun kunya dame ye kama?" Maimakon yaji haushin magsnganunta dariya suka bashi yace "Zuwaira wane irin kunya Kan abinda addininmu ya halasta bayan kinsan ance babu kunya a addini? Abinda ya halasta ne mu mutane muke haramtawa kanmu sabida jahilci, to in ba tsintsar jahilci ba Ubangiji ya halasta abu Kai bawa ka kawo al'ada da wasu shirme ka gindaya? So ki fahimci akwai aure tsakanin wa da matar kaninsa idan ya rasu za Kuma ayi shine na sanar dake don shi Alhajinku ma rokona yayi ayi da wuri Kar a dauki lokaci, to na bi shawararsa sai kije kiyi tunanin me kike bukata inyi miki ma fadar kishiya? Ta tabe baki "Idan duk jikina kunnuwane ba Zan taba yarda cewan Alhajinmu da kanshi zai goyi bayan ka yiwa diyarsa kishiya ba. "Me zai hana tunda diyar bata neman albarka bata faranta ran iyayenta?" Ta balla masa harara "Don zaka auro wannan yarinyar ce kake fada min magana?" Yace "Ke Kika ja yai nisa, and ki bar tunani cewan yarinya karama zan auro shekaru nawa kika bata?" Ta gatsina hanci "Yo Ashe ma tsohuwa ce kake wannan rawar jikin da dimirgishi Wai dafa kauri ba da." "Nima ai tsohon ne tinda na na Kai 41 yes Kinga za mu yiwa juna daidai kenan." Ta kallesa ta watsar "Kaji dashi Wai ciwon ajali a Dan yatsa." Ya dagi ya kalleta "Please shiga ciki ki kwanta kin dameni da surutu sai da safe." Tayi kwata "Surutu yanzun na bude chapter sai dai Kuma idan dinke bakina za kayi tunda baka da tausayi a zucci ka yanka ka dinke, Kuma gobe gidanmu za ni." Ya amsa "Allah ya Kai mana rai suma nemanki suke kije kije ki kwaso yaran da kika zube a can tamkar basu da gata." Yana fadin haka ya gyara kwanciyar sa nan alamun ba zai ma shiga bedroom din ba balle taci gaba da bala'in. Ta gaji da zama taja jiki ta nufi ciki tana Kun kunai kamar wata yarinya karama. 10/09/2020, 12:29 - Anty saliha: ...RAHIMA..doc by jami 24 Gari na wayewa ko wanka bata yi ba tana idar da sallah ta nufi gidansu, Kai tsaye ta wuce dakin mahaifiyarta, Hajiyar na zaune tana lazumi don al'adarta kenan. Ta dago taga Zuwaira ce taci gaba da karatunta ba tare da sake kallon inda take ba, ita kuwa ta haye bisa gadon uwar ta kwanta. Ba a jima ba taji muryar mahaifinta ya shigo yadda yake yi duk safe ya zagaya dakin kowacce mata yaga yadda ta kwana tareda iyalinta yaji ko tana da wata matsala su tattauna hanyar da zasu bullowa al'amarin. Ya zauna falon uwargidansa Hjy Lami yana jiran ta kare adduointa, Zuwaira taji muryarsa ta taso ta fito ta durkusa ta gaishe shi. Ya kalleta cike da mamaki "Ba dau Zuwaira nike gani yanzun ba, tun yaushe kika shigo gidan Nan?" Ta sunkuyar da kai tace "Ban dade da shigiwa ba, ina kwana?" Ya kalli agogon hannunsa yaga ko karfe takwas bata cika ba cikin tsawa yace "Wace irin sakayyar yarinya ce, ki baro gidan mijinki tun sassafe ki zo me zaki dauka?" Ta marairaice "Karansa na kawo Baba, wallahi duk ya canza, yanzun ma wai aure zai yi, da karya ma har yana cewa ka bashi goyon baya?" Uwar ta shafa adduarta ta fito ta durkusa gaban mijinta ta gaisheshi ya amsa kana cikin bacin rai yace "Ya akayi kika Kyaleta a zauna har tana kwanciya miki a dak?" Hjy Lami ta kada Kai "Yadda ka ganta hakan na ganta ko gaisawa ba muyi ba." Yace "Mutumiyar banza kina nufin kin kwaso kafafunki ne kinzo muyi miki mene, mu hana sa aure? Wallahi Mamana (haka yake kiranta saboda sunan mahaifiyarsa yasa mata) kin ban kunya, ban taba tunanin ba zaki zauna gidan aureki cikin mutunci ba,yarinya kin zama sai kace goyon arna?" Hjy Lami tace "Ya za ayi mijinki ya kalleki da mutunci bayan kin zama tamkar maras mafadi?" Ta saka kuka "Wallahi Mama Haseeb kazafi yake mini." Alh Muhd ya sake daka mata tsawa "Rufa min baki ko in tashi in tattakaki, wallahi muddin baki canza dabi''unki ba daga yau mun sa kafar wando daya ni dake, bar ganin na sake miki ina ksunarki, zata koma kiyayya tsakaninmu Kuma kin sanni sarai kamar yunwar cikinki, wallahi ko ke kadai na haifa ina iya yafeki har abada don banga amfaninki ba." Hjy Lami ta kalleta cikin bacin rai tace "Dubeki yarinyarki dake kin bata rayuwarki da kanki ga kinan duk kin jeme kin lalace, Kuma da kike cewa kazafi likitan ke miki su mutanen duniya da kike mu'amala da kawayen banzan da kike hulda dasu duk kazafin ne? Duk inda kika shiga ana ga 'yar wance da wane." Alh Muhd yace "Dalili kenan da muka bashi goyon bayan ya auro mai mutunci tunda ke kin zubar da naki, idan kinga ba Zaki iya zama dashi ba ga hanya nan bude to banga amfanin zama da igigiyar aurensa a kanki ba, sai kije kiji da zunubi daya." Uwar ta fashe sa kuka "Alhaji kalli yarinyar nan ka gani ba abinda ta sawa gaba sai burin duniya da kyale-kyale, dan rayuwar da take takaitatta. Wai don Allah wane irin gata ne ba a nuna miki ba? Me kika nema kika rasa a gidanku ko na mijinki? Allah ya hore dukiyar da ake taimakawa wasu ma, to me kike nema ne?" Maimakon ta nuna alamun nadama sai ta dauko wani zancen da bai danganci fadar da ake Mata "Mama ni gaskiya ba Zan zauna da kishiya ba, kishiyar ma yarinyar data san sirrina, bayan duk wata takama da Haseeb ke yi da wani ji da kai, mahaifina ne silar duk abinda ya samu, duk abinda yake takama dashi Kai dinnan Baba kaine sanadin, ko yana nufin anci moriyar ganga ne za a yarda kaurenta, to gaskiya Baba da sake... Bata ga mikewarsa ba, ji tayi kawai an dauketa da tafi ta kifa kasa, ya bita ya taka yana zagi, uwar ma ta rufeta da duka, Nan ta fara kwarma ihu sauran matan gidan suka taru don cetonta.. Da kyar da rarrashi aka kwaceta, ko kafin ayi haka fuska ta kumbura jiki ya murzu da duka. Alh Muhd ya fara haki, jiri ya kwashe shi, matan suka tareshi, akayi hanzarin dauko masa maganin hawan jininsa aka bashi yasha kana suka kamashi ya koma daki ya kwanta. Hjy Lami ta dawo dakinta ta cimma 'yar nata kuka tace "Ya jikin Baban?" Ta kalleta ta watsar "Tashi ki bace min da gani, ina ruwanki da jikinsa? Ai kinsan yanada hawan jinin don kece sanadi, to ki dage ki zama kece ajalinsa." Ta Kara fashewa da kuka "Don Allah Mama ku yafe min, Allah zan daina komi, bacin raine yasa Ni fadin wannan maganar." "Da gangar kika yi tunda an Sha gargadinki kan furucin da kike yi, yau kika yiwa mijinki gorin? Maras tunani, da kike fadin ubanki ne silar arzikinsa yanzun hidimar da yake mana ya zama ke Kika sa shi? Yarone dan halas da yasan darajar iyayensa da naki." Ta daga kai "To Ni Mama so kuke in zura masa ido Kan batun aurensa?" "Ah ah kike kiyi abinda zaki iya kinji zabin da muka baki ai. Ni tashi ki fita min a daki, ki Kuma dauki yaranki ki maida gidan ubansu tunda baki San ciwon kanki ba, albasa bata yi halin ruwa ba." 10/09/2020, 18:03 - Anty saliha: ....RAHIMA...doc by jami 25 Zuwaira ta tabbatar wa kanta ba zata sami yadda take so wajen iyayenta ba, saita canza shawara ta tuntubi Husaina daya daga cikin kawayenta a tunaninta ita din ce kadai zata iya taimaka mata warware matsalarta. Tafiya mikakkiya ta isa gidan Husaina dake gadon albasa, Sha daya saura na safe ta matsa kararrawa, saurayin dake mata wanki da guga ne ya bude mata kofar ta shiga yana gaisheta ta tambayesa "Ina Hajiyar?' "Tana ciki." Ya amsa. Kai tsaye ta wuce bedroom din Husaina ta taras da ita a kwance "Lalle kina jin dadinki, ni ina ga time din barcin safe?" Tayi Mika tace "Zuwaira Wai Ina kika shigane tun safe nike neman wayarki?" Zuwaira ta zauna bakin gado "Kinga ni yunwa nike ji bari in ci abinci tukunna kisha newa." Husaina ta dago ta kalli yanayin fuskarta ta saka salati ,"Ke ya aka yi haka?" Tace "Labarine mai tsawo bari in koshi jikina har rawa yake, rabona da abinci tun jiya wajen bukin nan." Cikin hanzari ta kira yaron gidanta ta umurcesa yaje ya hado musu breakfast, ya fita da sauri." Zuwaira ta kalleta sama da kasa "Haba Husaina dubi shigarki fa sannan kika yaron gidanki har cikin bedroom dinki?" "Look Zuwaira nu dake duk kanwar ja ce fa, jirgi daya ya kwaso mu, ya saba shigowa sai me?" Ta gyada Kai "No duk rashin da'ata ba zan bar wani kato ya shigo min cikin dakin barcinmu ba don na dauke shi matsayin *sacred secret place* "Hhhmmm ba dai kin koshi ba? Mu bar zancen mu koma na dalilin nemanki, shin ina Alhajin da yaso like miki wajen bukin nan, ya dameni in bashi lambar wayarki, ya isheni da naci that's why na kiraki tunda safe, me ye ra'ayinki?" Tayi saurin girgiza Kai "Raba da wuya kinji, in don kayan da muka ce muna so ne zamu sara ya taimaka mana ya bar abinsa, irinsu sun cika mita kawai ya hana min sikit.. Ni dai yanzun Kinga fuskata ko? Wallahi aikin Baba da Mama ne suka taru sukai min sukuwar Sallah don nace ban amince Haseeb yai aure ba." Ta furzar da ruwan da sanyin data kurba ta bugi kirji cikin tsoro "Dr Haseeb zai yi aure? Wonderful... "Kin ganni nan fa cikin tashi hankali nike, that's na garzayo bidan shawarki don iyayena sun bashi go ahead." "Yo inya sakeki ba kin huta ba, ga masu sonki ido rufe?" Tace "Sakin bai dameni ba, hakan nike so Amma wallahi ba zan bar gidansa kafin aurensa ba wannan yarinyar ta dauka ta isa ta koreni, sai tazo ta zauna na nuna mata ruwa ba sa'an kwando bane, wutsiyar rakumi tayi nisa da kasa." Husaina tace "A ina ya samu matar ne?" Ta amsa "Matar kaninsa daya rasu dinnan nan, shine iyayenta suka cusa mata ita don sun ga da maiko." "Tashin hankali inji Husaina ta Fadi cikin karaji "Yarinyar dake teaching makarantar kurame?" "Yes ita, wani abu ne?" Ta kada Kai "Yadda nike ji yarinyar nada kamun Kai da rike addininta, Kinga ko nan an samu difference. "Wannan lalurar tace Husaina ta Fadi tana daga kafada irin bai dameta ba dinnan, fada min meye shawara yanzun? Tayi shiru tukunna kafin tace " yanzun Kam kwantar bauna za muyi mu jira ta tare sai ki bullo da kissa da munafunci hade da karfar baka Wanda yafi asiri aiki mu gama da ita. Da dai baki da niyyar barin gidan ne da mun hadata da malam Mai gobe da nisa." Zuwaira tayi hamma tace "Shikenan sai mun sake haduwa, bari in koma gida don yau harda su Khalifa su Mama sunce in kwashesu, na baro an kaisu makaranta ne." Tayi tagumi "Oh in banda abin Dakta meye na hadaki da iyaye Kuma, ya barki kiji da jinyar kololon bakin cikin daya mulmula ya saka miki a kahon zucci don kishi cuta ce." Ta mike tsaye" Ki barsa kawai zan bashi mamaki, ni kam na tafi." "Zan iskoki har gida ba sai kinyi wahalar dawowa ba, yi jinyar tsamin jikinki." Yau kwana biyu kenan da taji labarin Hjy Kaltume na fama da zazzabi,tayi niyyar ta share ko ta aika kawai a dubota, Umma da Maryam sunce bai dace ba, ciwo ya kore komi Kuma tafi gaban sharewa a wajenta, ita tasan hakan illa dalilan da suka taso suka haddasa nisantar junansu. Ba domin batun aurensu da ya taso ba ai Hjy Kaltume uwarta ce mai bata nono tasha ta koshi.Tuni ta daina jin haushinta sai kunya data karu fiye da dauri, ta bi maganar iyaye ta shirya zuwa dubo Hajiyar Karfe takwas daidai ta fito daga gidansu sanye da wata doguwar riga ta yadin Kampala shadda maroon colour, wace ta dora Mata after dress a samanta cream colour. Tafiyar cikin rashin karsashi a natse take yi alamar dole ne yasa ta fito. Iskar dake bugawa a hankali ta rinka kada abayar da lullubinta, tafe take tana jan adduoin neman kariyar Ubangiji daga sharrin mazan dake ta son yi mata magana Yau saita ga gidan Hajiyar yai mata nisa, iya kauda kanta Saida wani Mai motar ya kyala ido ya ganta, ya Kuma bi bayanta har zuwa daidai lungun da zata shiga kwanar gidan Hajiyar, yai parking ya fito ya tsaya jiran fitowarta.... Ta shiga tareda sallama, Mairo ta amsa cikin murna "Marhabin maman Abdul sai yau, idonki kenan?" Tayi dan dariya "Kinada bakin magana ke sau nawa kika taho wajena?". "Ai kuwa sai dai ki zargeni na kanje in duba Umma mana" Mairo ta kare kanta... "To ai shikenan ya jikin Hajiya?" "Da sauki kin San halinta ai bata son a ga gazawarta." Rahima tace "In shiga in ganta, Allah ya sauwake. Hjy Kaltume na kwance bisa katuwar katifar da aka fito mata da ita falo, ta dago kai, tunda taga bakuwarta ta tashi ta zauna "Ni fa naji kamar muryarki sai naki amince ke dince tunda kin gujeni Rahima, Ina dan gidan Baba?" Rahima ta zauna kusa da ita daf da katifar ta gaisheta tukunna kana ta ajiye ledar data riko mata lemu da ayaba tace "Allah ban gujeki ba Hajiya hidimomin ne sukayi yawa, Abdul na baro sa gida naga darene yasa bance ya rakoni ba, Su Baffa da Umma na gaidaki da jikin." Tace "Nagode Allah yai albarka Ina amsawa, ita Umma takan lekoni, nima nakan aiki Mairo ta dubota.". Rahima tayi shiru, zuwa can ta tambayeta "Hajiya ko irin rashin lafiyar nan ce da kika taba yi bayan an kawoni ba dadewa?" Ta amsa "Ina tsammanin shine, domin yanayin jikin nawa kasala ce ke rufeni inji ko hannuna ban iya dagawa balle inyi motsi mai karfi, ga rashin samun isashshen barci, dare ya tsala kiga kowa na barci Ni kuwa lokacin nawa idanun zasu bushe in kasa barcin in rasa kuzarin tashi in gabatar da kiyamul lail yadda na saba, shi yafi damuna." "To kin sanar da Yaya kuwa?" Ta kada Kai "Hhmmm wannan Yayan naku hidimomi sunyi masa yawa, baida kwanciyar hankali wallahi har tausayinsa nike ji shiyasa nayi biris da tawa lalurar." "Hajiya ba'a yiwa ciwo haka fa, idan ya fahimci halinda kike ciki ba zaiji dadi ba, to Yaya Hayatu fa?" "Shima bai sanin ba Yana can yana zirga-zirgan Shirin tafiyarsu Hajj." Rahima tayi dan murmushi "Ai kuwa da sauran lokaci ko azumi ba muyi ba." "To Rahima Mai kwarmin ido ba da wuri yake fara kuka ba? Duk da ba karamin kuzuri aka biya musu gara dai su nema su Kara saboda mutum bai San yanayin da zai kasance a kasar da ba tasa ba." "Hakane gaskiya, zuwa Hajj Kam a wannan lokacin said mutum ya shirya, Allah yasa a dace.". Hajiya tace "To ameen, tabarbarewan al'amurran kasarmu sai addua." Rahima ta tuna dare ne ba rana ba, ta yunkura ta mike tace "Hajiya dare nayi bari in isa gida Zan dawo in an kwana biyu.' Ta bita da kallo kawai na ciki na ciki, tana son yi mata maganar Daktan ta kasa, Rahima na jin nauyinta kar ta matsa Mata, taja baki ta tsuke... Kafin suyi sallama amon muryar da kesa gabanta faduwa ce ta tsinkayo yana magana da Mairo... Nan take kirjinta yai mata nauyi sanadiyyar bugawar da zuciyar keyi ba control, tun kafin ya iso kamshin turarensa ya Kara tabbatar mata da shigowarsa. Ta mutu a tsaye, gaga tsara gaga, wannan shine gaba damisa baya siyaki, Ina zata shiga, uwardakin Hajiya ko saurin ficewa? Ta juya kwakwalwarta tayi dim ta tsaya cak! taki aiki balle taba sauran sassan jikinta umurnin next step da zata dauka. Ya kunno kai cikin dakin bayan Hajiya ta amsa sallamarsa, Yana shiga ya doshi gefen katifar uwar ya zauna, ya dago ya kalli Rahima dake tsaye a sandare yace "Ba dai har zaki tafi ba, daga can gida nike Umma tace kina nan." Da za abata zabi da basu ko gaisa ba ta sulale ta gudu that's in tafiyar zata yuwwu mata kenan da gwiwoyin da suka yi sanyi har kafafunta na rawa, nan ta durkushe ta gaisheshi. Amsar da ya bata cikin sakin fuska ya bata mamaki, eh to a gaban Hajiya ai ba zai rinka wannan cin maganin ba a nata tunanin. Cike da farin ciki da jin dadi ta kallesu "Ko zaka rage mata hanya ne tunda tayi shirin tafiya?". Rahima ta girgiza Kai "Hajiya tafiyar guda nawa ce, ba komi nagode yanzun zan Kai gida, mu kwana lafiya, Allah ya Kara sauki." Dr Haseeb yayi dan murmushinsa ba tare da yace komi ba. Hajiya tace "To shikenan Allah ya bamu alkhairi, nagode Allah sa albarka." Da hanzarinta ta fito waje ta saki wata ajiyar zuciya amma me zata gani? Mutumin dake jiranta ya fito daga mota ya karaso wajenta "Salamu Alaikum don Allah Hajiya ina son magana dake." Ta kalleshi a tsorace ta amsa "Nima don Allah kayi hakuri bani da lokacin magana da Kai." Babban mutum ne da ganinsa bata son cin mutuncinsa amma bai fahimci hakan ba ya sake matsawa kusa "Yi hakuri ki bani minti biyar kacal, sunanki da uguwarku nike son sani tunda kina sauri yanzun ki bani time in taho gida ga compliment card dina." "Hajiyar ta gode rike card dinka don bata bukatar sanin sunanka an riga anyi mata miji.". Bata yi aune taji muryar Haseeb na maida jawabi. Mutumin ya kalli Rahima yaji bata musa ba, ya kalli Haseeb duk da yana sanye da bakin glass dinsa fuskar nan ba alamun rahama nan da Nan yace "Don Allah kuyi hakuri sai anjima. Suna kallonsa ya shiga mota ya tafi. Sun dade ba tareda cewa juna kanzil ba, ta tuna gida zata tafi, ta juya tace 'Nagode, ta fara tafiya... Ya bita da kallo "Na yiwa Hajiya alkawarin kai ki so ki shiga mota mu tafi or are you ready for that kind of attention irin Wanda ya faru yanzun?" Cikin siriryar murya tace "Ni bani na kirashi ba.. "Ba zarginki nayi ba, mu tafi ko?" Tare suka shiga motar yaja suka isa cikin minti goma kacal. Motar na tsayawa ta bude kofar ta fito tace "Nagode a gaida su Aunty" Ya waigo "Magana nike dauke da ita ko kina jin barci gobe na dawo?" Ta girgiza Kai "Ba damuwa, mu shiga daga soro ko?" Ya fito ta rufe motar yana biye da ita, suna shiga tace "Zan amso key din dakin baki. Ta wuce cikin gida ta shaidawa Umman tana tareda bakone, Umman cikin farin ciki take wanda bai misaltuwa don ta gane waye ta Rahima ta kira bako. Har zata fita tace "Haka ake tarbon bakon ko ruwa ba zaki Kai masa ba balle lemu? Ban sanki da rowa ba Rahima." Ba tareda da tanka ba ta bude fridge ta dauko gorar ruwa da lemo da cup ta dora bisa faranti ta koma soron, Yana ganinta ya mika hannu ya amshi kayan ta bude kofar tace "Bismillah." Bayan sun shiga ciki ya ajiye farantin ya zauna kan kujera, Saida ta durkusa ta zuba lemun a cup ta ajiye sannan ta zauna gefen tabarma. Ya dan kurbi lemun kadan ya mayar ya ajiye yana kallonta ta cikin dark glasses dinsa yace "Ina Abdul dina ne ko har yayi barci?". Ta daga Kai "Ya riga yayi barci." Yace "Yaron dana san yana kai wajen sha daya bai kwanta ba sai anyi ta fama dashi?" Tace "Ban da yanzun kuwa ko don bai jin dadi ne oho." Ya bude baki cikin mamaki "Ya akayi ban sani ba, baki aiko min ba ko Hajiya?" Can kasa tace "Don naga ba it's not that serious.".. "Ya akayi kika San hakan?" Yai tambayar a fusace. Ta sunkuyar da Kai "An kai shi asibiti sunce malaria ne sun bada treatment shi yasa naga ba sai na aiko ba." Ya gyara zama "Daga yau karki sake min haka, duk abinda ya shafesa wajibi a sanar dani komin kankantarsa do you get me?" Ta daga kai alamar amsa. Ya kalleta sai Kuma ta bashi tausayi, ya sassauta murya yace "Look why not a daura auren nan this week mu ragewa kanmu jidali tunda Allah ya kaddaro mana haka, daman shawarar dana zo mu hadu mu yanke kenan. Mu ba yara bane, mun San ciwon kanmu naga zaifi dacewa ayi abinda iyaye keso zai fi mana sauki... Rahima tayi shiru yaci gaba "Ko Hajiya abinda ke damunta kenan saboda ta sanya abin a ranta." Ta dai kyalesa ya shirya mai yuwwa tana saurarensa yayi ya gama, ya mike zai tafi ya mika mata rafar kudi tareda tsadaddar handset. Cikin kwanaki uku kacal aka gama tsarawa da shirya komi. Daktan ya aika kayan aurensa akwatuna biyar, ya shaida mata ba zai ajiyesu gida daya da Zuwaira ba ya nemi amincewar yazo su tafi taga gidan da ya saya inda zai ajiyeta a dorayi, tace ba sai taje ba. Bata da niyyar yin kowanne irin shiri kan auren, Maryam tayi surutunta ta gaji ta kyale, ba tareda saninta ba sun shirya abinda ya dace game da gyaran gidan amarya sun Kuma nemi angon yasa an kaisu suka tsara shi yadda ya kamata amaryar data hadu a ga gidanta. Ranar da za'a daura aurensu tunda asubah aka nemi Daktan ya taimaka ya nufi Riyadh dubo maras lafiyan Nan, wannan karon ba gardama, aikinsa ceto rayuwar dake neman agajinsa da taimakon Allah in yai nufin patient din ya tashi, in Kuma lokacinsa yayi ba makawa. Yana gab da tashi ya kira Rahima ya bata hakurin rashin samun daman halatar daurin aurensu, tace ba komi Allah ya kai shi lafiya ya dawo dashi cikin amincinsa, tayi masa adduar Ubangiji ya bashi sa'a yayi nasaran shawo Kan ciwon da yai tafiyar dominsa. Karfe bakwai daidai na agogon Nigeria jirginsu ya daga suka nufi kasar Saudiyya kan hanyarsu ta isa babban birnin kasar Saudiyya, Riyadh. 10/09/2020, 22:44 - Anty saliha: ...RAHIMA..doc by jami 26 Abin sha'awa iyaye, 'yanuwa, da abokan arziki ne suka tsaya aka daura auren Abdul-Haseeb da Rahima. Kafin ayi haka labari ya baza gari, jama'a suka shiga fadin albarkaci bakinsu wasu suka ce yaci amanar Rabiu, wasu suce daman can da kulalliya tsakaninsu, surutai dai gasu nan barkatai masu matukar daga hankali musamman ga wadanda abin ta shafa, da yake shi angon yai nisar kiwo sai damuwar ta tattara kan amaryar kadai daman cu cikinta take. Ta yini babu karsashi ba walwala ba wani kwalliya, bata gayyaci kowa ba hatta collegues dinta basu sani ba, to abu ya taras da miskillancin tsiya, ita Sam bata damu tayi kawa ba a tunaninta Maryam ce kawarta, aminiyarta Kuma 'yaruwa rabin jikinta. Umman da Maryam sunce ba za suyi taron buki tamkar ana zaman makoki ba don haka suka gayyaci dimbin jamaa bayan 'yanuwa wajen yinin bukin da suka shirya. Taro yayi kyau, an ci an sha an koshi, bayan azahar masu wa'azi suka dasa tasu nasihohin suka rinka fassara ayar Allah suna fassarawa. Suka fara da fadakarwa kan masu ganin auren wa ta auri matan kani jahilci ne suka yi kaca-kaca da masu kafa tsirku kan fadin Allah, suka dawo suka yiwa amarya nasiha kan hakkokin mijinta da suka rataya a kanta, suka hangaro na tarbiyyar diyanmu kana daga karshe suka rufe da matsalar data fi addaban Mata yanzun 'kishi' Wa'azine masu ratsa zuciya da shiga jiki ga wadanda keda sauran imani sun kudurta gyaran kurakurensu, ga wadanda suka yi nisa Kuma sai ido . Karfe biyar na la'asra Jamila da Haulatu suka jagoranci tawagar sauran matan kannin Daktan suka taho, a nan drama ta tashi Rahima na kiransu Aunty a matsayinki na matan wan mijinta, yau kuwa reshe ya juye da mujiya, ita ta koma Auntyn tasu a sabon matsayin da Allah ya bata matar babban Yaya. A can ainihin gidan Daktan uwargidan amarya ta gayyato kawayenta marasu mutunci sun cika gida makil, hatta 'yanuwanta komawa gefe suka yi suna kallonsu .. Kawayen sun gama zugata da bata shawarwarin da ba zasu amfaneta ba, harda shirya mata abinda zata yiwa amaryar don tasan ba wurin zamanta bane. Shashashar ma ashe bata san ma cewan ba gida daya zasu zauna ba, Saida ta aika gidan Hajiya a dubo ko tana can ne aka fada mata dorayi aka kaita. Ta dakawa Dan sakon tsawa "Dorayi wane gida? Jeka dubo min ka dawo yanzun." Suna ta yi mata famfo tana hauka cewan ai kamarta raunin hankaline ma ace mijinta yai mata kishiya ko wane dabiun kwarai take dasu da zai hana ayi mata oho. 12/09/2020, 13:05 - Anty saliha: 🦈🦈RAHIMA🦈🦈 28 Ta sauki mintoci heart beat bai koma normal ba, watau a takaice so da kaunar Ya Haseeb na neman mamaye mata ruhinta, ta girgiza Kai wannan ma ai shine abin kunyar, hhmmm da zai fahimci haka ya zai dauketa, maras tunani ko maras matunci? In kuwa hakane gara ta yiwa kanta rigafi ta danne zuciyarta zai fi mata alkhairi. Ba sauran barci a idanunta don haka ta fito daga dakinta ta nufi kicin inda ta taras da Uwale harta kama aikin hada breakfast, tana ganin Rahima ta durkusa ta gaisheta "Hajiya barka da fitowa." Ta amsa "Ina kwana Uwale ashe kin tashi tun dazun." Tayi dariya "Ai mun saba, a can kauye ina muka ga lokacin barcin safe, muna alla-allah bayan munyi sallah mun karya kummalo da dumammen turo mu zuba hatsi a turmi mu shiga neman na abincin rana mu da yara.. Rahima tace "Gaskiya kuna kokari,kuna wahala, shiyasa akace mutum ta rinka kallon na kasa da Kai, nan zaka gane ni'imar da Allah yai masa sai Kuma ka gode masa don wasu sun fi kane Kai Kuma kafi wasu, amma gaskiya idan kika duba rayuwar matan karkara sunada matukar tausayi, sai muce mu aljanna muke." Uwale ta nisa "Ina ma ki kasan haka Hajiya, sai Kinga macen kauye a ce miki sa'arki ce ki yita rantsuwar ba haka bane don ta kusa haihuwarki a fuska, ta tsofe ta komade saboda wahala, hakora sun zube, ba isashshen ingantaccen abinci, ba hutu, na kyakkyawar muhali balle wani sutura mai kyau ga rashin samun kulawa daga mazajenmu, yawanci mazanmu fa basu San darajar mace, iyakar ki dashi ki dafa abinci, wata har noman abincin ma da ita za ayi, kiyi surfe da daka, idan ya bukaceki ya sarrafaki kamar yadda yakewa jakarsa da yake kiwo,idan kin dauki ciki ki babu wani kulawa, wajen haihuwar ma wani a rabu kacar sabida yaushe ya barki Kika je wani asibiti don inganta lafiyarki balle na dan cikin ko jariririn da aka haifa, wasu kuwa don su doki mace ba wani aibu bane a garesu, to mazan nawa ne suka san hakkokin matan da ya rataya a kansu?" Dalili kenan koda mijina ya mutu zawarawa suka yo min caa!! Nace bada Uwale ba, anyi daya ba za a kara na biyu ba, da in zauna cikin jahilci da rashin sanin me auren ya kunsa da rashin sanin hakkokin juna gara in taho birni in nemi sana'a." Rahima ta nemi kujera ta zauna tace "Bari in tayaki aikin mu ci gaba da hirar sai mu karu da juna.. Uwale tace "Ai ke Hajiya Allah ta tarfawa garinki nono, da mata na dacen irin mijinki da ba za suyi kukan komi ba, ko su Mairo da suke 'yan aiki sun shaida balle ku, kin kuwa ji ance kyakkyawar safiya tun daga maraice ake fara ganewa, jumma'ar da zata yi kyau tun laraba ake ganeta, wallahi haka nake son namiji yasan mutuncin 'ya mace. Rahima tayi dariya "Ai ko mazan namu ana samun wadanda basu San darajar macen ba, da na dauka jahilci ne yasa wasu mazan ke maida matansu tamkar jakuna ashe ba hakan bane, ko a birnin haka wasu mazan suke, kiga namiji bai san mutunci da darajar matansa ba, mace bata isa yai shawara da ita ba, don a ganinsa shirme ne, ke wani fa ya dau mace tamkar Mai karamar kwanya ce don haka baki Kai matsayin da zai fada miki wasu sirrinsa ba, sai kiji wani na kiran matarsa Wai dabba ko jaka don rashin sanin kimarta da rainin hankali, amma bai hana ya nemi biyan bukatarsa, bayan haka sukan manta mace dai ta haifesu suke mata isgillancinka bayan Allah ya daukaka darajar martabarta, saboda duk inda namiji ya Kai da mukaminsa, sarauta, jin Kai dole macen yake dawowa. Uwale tace ai baki ma san wani abu ba, mijina madokine, kina masa laifi komin kankantarsa sai ya jibgeki, shi bai kyautata yadda Allah yace ba, bai baki isashshen abinci ba, ba suturarsa fa sai an bamu kwance nida yara, ya rinka hura hanci yana tafe yana busar iska da shan kamshi sai kace Wanda aka kadawa tambari, dare nayi yaje gashi nan bisa kanki, kina gardamawa ya kile ki yayi abinda yake so, ya barki da tsamin jiki ga yunwa dake kwakularki tunda ba ki ci abinci ya isheki da daren ba, gari na wayewa ki shiga fafutukar nemawa yara kalaci. Rahima ta kyalkyace da dariya tace "Uwale Kar kisa cikina ciwo don Allah don Allah ki daina maganar mamaci haka, ki yafe masa tunda ma ai kusan lefinki ne, wa yace ki rinka gardama bayan ance idan baki amince ba kuka kwana yana fushi dake mala'ikun rahama tsine miki za suyi, Allah yai fushi dake." "Hhmmm Hajiya na sani amma sai aka ce suma kar su kyautata mana su sauke hakkokinmu a kansu, kullum ko wa'azi aka tashi sai dai kiji ana fadin mu mata mu sauke hakkokin mazajenmu, su Kuma su rinka tinkaho suna gadarar aljannar mu na karkashin duga-duginsu, suna takamar tunda ance matarka gonarka ce ka zo mata duk lokacin daka so, ko a saman rakumi ne." Rahima ta Kara kyalkyacewa da dariya "Shin Uwale zaki bari mu karya mu kimtsa ko sai kinsa cikina ya cika da dariya tukunna?" Uwale ta kece da dariya itama "Da takaici ne Hajiya.". Tace "Kuma na yarda da batunki, ya dace maza su rinka bamu darajarmu da Allah ya bamu su daina raina hankali da tunaninmu, mu ma muna da kaifin hankali da zurfin tunaninmu, mu ba dabbobi bane mun san ciwon kanmu mun san ya kamata, mun san hakkinmu, mun san nasu, ya dace ace yadda muke kokarin kyautata musu suma su kyautata mana don mu kara ingantuwar zamantakewar aurenmu. Uwale tace "Hakane wallahi,idan muna kokartawa zamu rinka ganin canji, Allah ya taimakemu. Bayan sun kammala kalacin safe, Rahima tayi wanka ta tsala kana ta rinka zagaye sabon gidan nata. 12/09/2020, 22:49 - Anty saliha: ˆRAHIMA ..doc by jami 🦈🦈RAHIMA🦈🦈 27 Zuwaira ta gyara zama a tsakiyar kawayenta taci gaba da masifa "Ku barni dashi zai dawo ya sameni, tun kafin aje ko'ina ya fara nuna injustice." Karaf a kunnin Innarta yar mahafiyarta ta kirata gefe ta fara fada "Ni fa ko da ake gaya min kina hulda da kadangarun bariki ban yarda ba sai yau dana gani da idanuna, ashe wayonki ya zan na banza tunda za kiyi sake wadancan shaidanun su rika hure miki kunni bayan duk fushin da iyayenki suka yi dake ko a jikin ki ko?" Ta turo baki kamar na jaba "To ke Inna baki ga rainin hankalin da yai min bane sai nawa za a gani don na nemi hakkina?" "Yi min shuru sakaryar banza, har wani hakki Kika ajiye? Ana tarboki kina fandarewa, to wallahi duk Kika bari iyaye suka juya miki baya sai dai ki nemi na bariki da suke zugaki." Haka al'amarin ya kasance gareta har aka watse. A can gidan amarya mutane sai sha daya suka watse sai Maryam data tsaya suyi sallama sai kuwa matar da Hjy Kaltume ta nemo mata ta rinka tayata aikin gida wace yar uwar Mairo ce. Rahima ta yaba da tsarin gidanta sosai everything looking nice and cute, ta kama hannun 'yaruwata dake tsaye tana niyyar tafiya tace "Nagode sosai Yaruwa Allah ya bar zumunci.... "Haba kanwata tsakanimu ya zarce haka, Kuma da kike ta wani godiyar gida ba fa ni kadai na tsara ba harda angonki don haka shi ta dace ki yiwa godiya." Ta zaro idanu "You don't really mean that.. Maryam tace "What's so hard to believe? Mijinki mutum ne mai saukin Kai, ga wanda ya fahimcesa,Nima dane nike masa muguwar shawar but mu'amalar da muka yi na dan lokacin nan na fahimce sa sosai kema zaki fadi more nan gaba." Tace "Hhmmm ni ba abinda ke damuna illa yadda zan kallesa a matsayin mijina idan ya dawo, gaskiya ban san abinyi ba." Ta kyalkyace da dariya har tana kwalla "Kenan Ni zan fada miki abinda za kiyi? To tunda abin ya zama haka bari ya dawo shi zai sani." Tana gama magana tayi gaba ta barta nan, dole ta rufe kofar falonta tunda maigadi ya rufe gate Maryam na tafiya. Ta leka dakin da Uwale take taga har tayi barci... Ta shiga bedroom dinta ta shige toilet inda ta sake yin wanka ta dauro alwala, ta fito tayi haramar sallar nafila., tayi adduointa ta kare kana ta haye gado da niyyar samun isashshen barci don wartsake gajiya, amma barci ya gagara, har zuwa karfe ukun dare tana juyi dalilin kekashewar da idanunta suka yi, ba alamun barci ko kadan Tunanine ya addabeta, to yanzun ita Rahima ta tabbata matar Yaya Haseeb kenan ko, shin akwai wadanda Allah jarabta irinta kuwa? Anya rayuwarta zata taba komawa normal? Yes ta sani kowacce rayuwa da irin kaddarorin da aka rubuta mata, yau kaga fari gobe baki, yanzun yau kaga abinda kake so gobe ka samu kishiyar hakan, yau murna gobe ko jibi akasin hakan ba don komi ba sai don Mahakiccinmu ya gwada karfin imaninmu da kasancewar bawa bai taba dauwama cikin abu guda. To ita a matsayinta na musulma wace ta yarda da kaddara mai kyau ko maras ya zama wajibi a gareta tasa hannu biyu ta rungume ta duk da kasancewarta mace mai rauni. Tunanin marigayi suka kutso Kai daidai lokacin Wanda ya haddasa gudanar hawayenta suka fara jika pillow, Allahu Akbar! Ta fadi a fili, rahamar Ubangiji ya ni'imta makwancinsa, sunyi rayuwar aure ingantacce duk da sunce zo mu zauna zo mu saba, zamantakewar su abin koyi ne ga ma'aurata, Bata taba tunanin aurensu zai zo karshe da wuri ba, Amma kash! Mai katse dukkan wani hanzarin mutum ta kusanto ta rushe dukkan ginin da suka fara dorawa... To shin yanzun zata iya dora wani tubalin don gina sabon rayuwar aure da Yaya Haseeb? Idan tasan zuciyarta tasa fa? Ya zata iya tarayyan miji da Aunty Zuwaira gashi tun ba a kai ko ina ba ta fara jin sabanun da ya shiga tsakaninsu? Ta juya gefe guda tace Oh Ya Allah gani gareka, kai ka kaddaro min auren nan , Kai kasan dalili, Ina rokon ka tallafa min tafiyar da al'amarin auren nan nan cikin sauki tareda jagorancin ka. Bata samu barci ba sai bayan data idar da sallar asubah, ta sureta kenan aka Kira wayarra dake kusa da itaa Ta dauka ta sallama ido a rufe. Amsarsa tasa ta bude tangaran.."Ba dai na tashe ki daga barci ba ko?" Ya tambaya bayan amsa mata sallamarta. Shock ya shigeta faras daya, zuciyarta ta fara ras-ras... "Are you alright? Ya sake tambayar ta amsa da Kai, nan take ta tuna bai ganinta tace "Komi lafiya." "Ban amince ba, your voice is very low what's wrong." "Wallahi ba komi." Ya amsa "Hakan dai kika ce, anyi sha'ani lafiya ba wani problem ko" Rahima tace "Aljamdulillah." Is the house ok?" Ta sake amsawa a natse. Daga daya bangaren Dr Haseeb ne ke tuhumar me yasa take bashi short answers,wata zuciya tace baka disconnecting wayar ka huta tunda ba hirar ya kirata suyi ba, a nasa tunanin ma gaisawa kawai za suyi but ya kasa aje wayar ya rasa kalmar fadi Kuma sai kame,-kame. Ya nisa ya sake tambaya "Ina Abdul? Yana lafiya ko?" "Yana wajen Unma." Yai shiru yana murzan goshinsa da yatsu biyu, ya rasa dalilin kasa aje wayar, dalili ya wuce matsayinta na matarshi da son cika amanar da ya dauka? Can yaji muryarta tana tambayar "Ya patient?" Ya amsa "Alhamdulillah, he's progressing well, nagode. "Masha Allah Ubangiji ya bashi lafiya." "Ameen bari in barki ku huta zan kiraki gobe Amma idan da abinda kike so ki yiwa Hajiya magana.". Tace "Ba wata damuwa insha Allah may be dai inje in dubosu zuwa jibi." "A ina kika taba ganin amarya na yawo? Ki bari saina dawo mu tafi tare." "Ta amsa shikenan." "A shafa min kansa, nagode. 🦈🦈RAHIMA🦈🦈 28 Ta sauki mintoci heart beat bai koma normal ba, watau a takaice so da kaunar Ya Haseeb na neman mamaye mata ruhinta, ta girgiza Kai wannan ma ai shine abin kunyar, hhmmm da zai fahimci haka ya zai dauketa, maras tunani ko maras matunci? In kuwa hakane gara ta yiwa kanta rigafi ta danne zuciyarta zai fi mata alkhairi. Ba sauran barci a idanunta don haka ta fito daga dakinta ta nufi kicin inda ta taras da Uwale harta kama aikin hada breakfast, tana ganin Rahima ta durkusa ta gaisheta "Hajiya barka da fitowa." Ta amsa "Ina kwana Uwale ashe kin tashi tun dazun." Tayi dariya "Ai mun saba, a can kauye ina muka ga lokacin barcin safe, muna alla-allah bayan munyi sallah mun karya kummalo da dumammen turo mu zuba hatsi a turmi mu shiga neman na abincin rana mu da yara.. Rahima tace "Gaskiya kuna kokari,kuna wahala, shiyasa akace mutum ta rinka kallon na kasa da Kai, nan zaka gane ni'imar da Allah yai masa sai Kuma ka gode masa don wasu sun fi kane Kai Kuma kafi wasu, amma gaskiya idan kika duba rayuwar matan karkara sunada matukar tausayi, sai muce mu aljanna muke." Uwale ta nisa "Ina ma ki kasan haka Hajiya, sai Kinga macen kauye a ce miki sa'arki ce ki yita rantsuwar ba haka bane don ta kusa haihuwarki a fuska, ta tsofe ta komade saboda wahala, hakora sun zube, ba isashshen ingantaccen abinci, ba hutu, na kyakkyawar muhali balle wani sutura mai kyau ga rashin samun kulawa daga mazajenmu, yawanci mazanmu fa basu San darajar mace, iyakar ki dashi ki dafa abinci, wata har noman abincin ma da ita za ayi, kiyi surfe da daka, idan ya bukaceki ya sarrafaki kamar yadda yakewa jakarsa da yake kiwo,idan kin dauki ciki ki babu wani kulawa, wajen haihuwar ma wani a rabu kacar sabida yaushe ya barki Kika je wani asibiti don inganta lafiyarki balle na dan cikin ko jariririn da aka haifa, wasu kuwa don su doki mace ba wani aibu bane a garesu, to mazan nawa ne suka san hakkokin matan da ya rataya a kansu?" Dalili kenan koda mijina ya mutu zawarawa suka yo min caa!! Nace bada Uwale ba, anyi daya ba za a kara na biyu ba, da in zauna cikin jahilci da rashin sanin me auren ya kunsa da rashin sanin hakkokin juna gara in taho birni in nemi sana'a." Rahima ta nemi kujera ta zauna tace "Bari in tayaki aikin mu ci gaba da hirar sai mu karu da juna.. Uwale tace "Ai ke Hajiya Allah ta tarfawa garinki nono, da mata na dacen irin mijinki da ba za suyi kukan komi ba, ko su Mairo da suke 'yan aiki sun shaida balle ku, kin kuwa ji ance kyakkyawar safiya tun daga maraice ake fara ganewa, jumma'ar da zata yi kyau tun laraba ake ganeta, wallahi haka nake son namiji yasan mutuncin 'ya mace. Rahima tayi dariya "Ai ko mazan namu ana samun wadanda basu San darajar macen ba, da na dauka jahilci ne yasa wasu mazan ke maida matansu tamkar jakuna ashe ba hakan bane, ko a birnin haka wasu mazan suke, kiga namiji bai san mutunci da darajar matansa ba, mace bata isa yai shawara da ita ba, don a ganinsa shirme ne, ke wani fa ya dau mace tamkar Mai karamar kwanya ce don haka baki Kai matsayin da zai fada miki wasu sirrinsa ba, sai kiji wani na kiran matarsa Wai dabba ko jaka don rashin sanin kimarta da rainin hankali, amma bai hana ya nemi biyan bukatarsa, bayan haka sukan manta mace dai ta haifesu suke mata isgillancinka bayan Allah ya daukaka darajar martabarta, saboda duk inda namiji ya Kai da mukaminsa, sarauta, jin Kai dole macen yake dawowa. Uwale tace ai baki ma san wani abu ba, mijina madokine, kina masa laifi komin kankantarsa sai ya jibgeki, shi bai kyautata yadda Allah yace ba, bai baki isashshen abinci ba, ba suturarsa fa sai an bamu kwance nida yara, ya rinka hura hanci yana tafe yana busar iska da shan kamshi sai kace Wanda aka kadawa tambari, dare nayi yaje gashi nan bisa kanki, kina gardamawa ya kile ki yayi abinda yake so, ya barki da tsamin jiki ga yunwa dake kwakularki tunda ba ki ci abinci ya isheki da daren ba, gari na wayewa ki shiga fafutukar nemawa yara kalaci. Rahima ta kyalkyace da dariya tace "Uwale Kar kisa cikina ciwo don Allah don Allah ki daina maganar mamaci haka, ki yafe masa tunda ma ai kusan lefinki ne, wa yace ki rinka gardama bayan ance idan baki amince ba kuka kwana yana fushi dake mala'ikun rahama tsine miki za suyi, Allah yai fushi dake." "Hhmmm Hajiya na sani amma sai aka ce suma kar su kyautata mana su sauke hakkokinmu a kansu, kullum ko wa'azi aka tashi sai dai kiji ana fadin mu mata mu sauke hakkokin mazajenmu, su Kuma su rinka tinkaho suna gadarar aljannar mu na karkashin duga-duginsu, suna takamar tunda ance matarka gonarka ce ka zo mata duk lokacin daka so, ko a saman rakumi ne." Rahima ta Kara kyalkyacewa da dariya "Shin Uwale zaki bari mu karya mu kimtsa ko sai kinsa cikina ya cika da dariya tukunna?" Uwale ta kece da dariya itama "Da takaici ne Hajiya.". Tace "Kuma na yarda da batunki, ya dace maza su rinka bamu darajarmu da Allah ya bamu su daina raina hankali da tunaninmu, mu ma muna da kaifin hankali da zurfin tunaninmu, mu ba dabbobi bane mun san ciwon kanmu mun san ya kamata, mun san hakkinmu, mun san nasu, ya dace ace yadda muke kokarin kyautata musu suma su kyautata mana don mu kara ingantuwar zamantakewar aurenmu. Uwale tace "Hakane wallahi,idan muna kokartawa zamu rinka ganin canji, Allah ya taimakemu. Bayan sun kammala kalacin safe, Rahima tayi wanka ta tsala kana ta rinka zagaye sabon gidan nata. 29 Gidan Rahima sashe-sashi biyu ne sai fili daga can gaba, ginin kansa ya tsaru sosai, ga furanni masu fitar da kamshi daban-daban, tun kafin ta tare saida aka yi mata saukar qur'ani da adduoin neman tsari da albarkar zaman baki daya.. Sun gaisa da maigadin Mai suna Mal. Hassan yayinda dansa Haladu ne zai rinka yi musu wanki da guga da share-sharen waje da gyaran shukoki. Sha daya amaryar ta fara baki, zuwa azahar sai ga uwargida Zuwaira da tawagarta sun danno mata baya, suna mata kirari "Sai ke uwargidan likitan likitoci.. Tayi musu maraba cikin ladabi, ta gaishesu suka share, tasa Uwale ta kawo musu kayan motsa baki dasu lemu shima ko kallo balle su dandana sai sakin magana suke. Ba inda Rahima ta burge kowa sai da taki kulasu tayi tamkar bada ita suke maganar ba don ta lura so suke ta tanka su ci mutuncinta, da taga haka maimakon suyi tafiyarsu sai ta mike tace su biyota wai suga cikin gidan, kawayen Zuwaira su bakwai suka bita duu tana gaba suna biye, Saida suka gama zagaye ko'ina kana suka dawo falo ta tsaya a gaban Rahima tace "Miko min key din dakin Dakta sabida Nan ne kadai ban shiga ba." Cikin natsuwa Rahima tace "Kin dai shiga inda suka dace ki gani, inda kike batu yanzun kuwa sai ki jira amincewar mai dakin tukunna in ya dawo." Kawar Zuwaira Hussaina ta girgiza Kai "Lalle yarinyar nan taga gadon barcinki ta rainaki wallahi." Wata cikinsu kuma tace "Ya dace ji nuna mata da gidan da maigidan dyk mallakin kine." Tana wani jijjiga jiki kamar Mai shirin hawa bori tace "Ki kiyayeni wallahi, zaki bani ko sai rayuka sun baci tukunna?" Rahima ta yunkura ta mike tsaye ta bisu da ido tace "Kin ban mamaki Aunty Zuwaira da zaki tsaya kadangarun bariki na hura miki m wuta a gidanki. Da akwai girma da arziki watakila in daure in baki keys that's in ke kadai ce ma, amma yanzun ba Zan iya ba, kiyi iko da naki gidan inyi da nawa, abu na karshe Ina rokon don Allah ki kwashe tarkacenki gayyar na ayya kuyi gaba. Daga yau idan ba girma da arziki zai kawo ki ba please Kar ki sake zuwa min gida, nagode da ziyara, Kuma a rinka taka tsantsan da duniyar nan tamu mai halin Dan mangwaro, sai kana shansa dadi ya fara tsumaka ya subuce maka, hakan nan ita din rawar 'yan mata ce, na gaba Kan koma baya... "Tafdijan! Lalle wuyar yarinyar nan ya isa yanka, to ke Kyaleta za kiyi Zuwaira ta rainaki a gabanmu?" "Zuwaira ta cika tayi fam tace "Wai ita 'yar gani lasheni.. Daya kawar tace "Ba ki sharara mata mari ta gane banbancin aya da tsakuwa?" Kamar go ahead kawai take jira ta daga hannu zata kaiwa Rahima mati, tayi wuf ta rike hannun cikin sa'a tana girgiza kai "No Aunty Zuwaira Kar ki fara, duk haukar da za kiyi zan kyale but Kar kiyi mistake din hannunki ya Kai ga jikina, don ni din Dan hakin daka raina ne, Ina iya tsone idanunki." Zuwaira tayi kokarin kwace hannunta ta kasa, kawayen nata na ganin haka suka tasowa Rahima haikan, ta kallesu a wulakance tace "Duk wace ta matso kusa dani sai buzunta." Suna cikin haka tawagar iyalan gidansu Haseeb dana bangaren su Haj. Kaltume suka shigo, kanwar Hjy Kaltume mai suna Hjy Iya ta rafka salati sauran jama'aa suka dauka suma "Me zan gani Rahima? Ta saki hannun Zuwaira tace "Tambayi Aunty Zuwaira... Ta juya wajen Zuwairan tace "Ya kike son zubar da girmanki, anyi bukin nan an watse lafiya, meye na tayar da husuma, tunda Allah ya hadaku zaman tare ba sai kuyi hakuri da juna ba, mijinku na can na nema muku abin rufin asiri, ku kuna nan gaban jama'a kuna zubda mutuncinku, ina amfaninsa. Zuwaira ta figi gyalenta ba tareda Kara cewa komi tace wa mutanenta "Mu tafi, ai zamu sake dawowa." Suna fita mutane suka shiga tseguminsu, Rahima ta katse su "Ni dai ku daina cin namansu din Allah, kuyi musu adduar shiriya idan zaku iya, idan ba zaku iya ba kuyi shiru." Da dare ne Maryam ta kwaso su Umma, da goggo Lauratu matar mahaifin Rahima din dasu Abdul suka taho gidan amarya. Bayan sun gama gaisawa iyayenta suka ci gaba da yi mata nasihohi domin ko da yake ita din ba yarinya bace, ba aurenta na farko bane iya yar Adam ce ajiza, wani da gangar yakan kauce hanya ya bi son zuciyarsa, dalili kenan da yasa ake son manya su rinka nasihohi da fadakarwa tareda jan hankali domin gyara. Maryam ce ta dauko batun su Zuwaira, Umma tace ke dai bari duk magana ta karade a Yakasai Wai tayi hayar yan daba su taho su baki Kashi." Rahima tayi murmushi "Gaskiya surutun mutane ne 'yan sa ido da tsegumi, ko ba ayi abu a gabansu ba zasu ce sunji sun gani." Maryam taja tsaki "To ai ita Zuwairan tasan haka, yau mitum ake kiwo ba dabba ba, me yasa ta kwaso 'yan bariki ta kawo gidanki har suci miki mutunci, hhmmm Allah ya tsare da nice wallahi da anyi kare jini biri jini, gobe ko anzo ance ta taho sai tayi fargabar dumfarata." Umma ta harareta ta kalli goggo "Kinji fa, maimakon taba 'yaruwarta hakuri sai Kara tunzura take, ni ban San ranar da za kiyi hankali ba, haihuwa uku." Goggo ta bushe da dariya "Ai ba rashin hankali bane, koni da tsufana ba zan kyalesu irin yadda Rahimar tayi ba, ai ko bata mareni ba sauna sharara mata tafi don kunyar jin maras kunya asara ce." Maryam tace "Musamman ga wadanda basu san mutuncin kansu ba balle na wani." Umma ta kada Kai " Yadda tayi yayi daidai Kuma nagode, baku see ba a biyewa mahaukaci ba, ka Kan koma gefe ne kayita kallonsa yana shirmensa idan ka biye masa kuwa sai ku haukace gaba daya... Rahima tace "Nima shiyasa naki biye mata muyi fadan Kuma ta gane ba zan dauki rainin wayo ba kowacce tasan matsayinta." "Nagode hakan Nike so ki ci gaba da hakuri komi mai wucewa ne " Cewar Ummansu . Maryam taja Rahima daki tace "Yaya ya kira waya? "Tunda safe." Ta amsa a takaice.. Maryam tace "Da kyau Daman shi na kosa inji." Rahima ta tabe baki "Da baki ji ba fa sai Yaya?" "Sai yaya kuwa illa nasan kanwar tawa zata damu ance an daura aure ango na can wata usa duniya, amarya ta kwana ta yini cikin gidansa ace ba kiji muryarsa ba, fita hayyacinki za kiyi sabida mutumin nan ne fa.... Ta harareta "Bari don Allah ban son kuna tuna min wancan zancen ya wuce." "Ni kuwa nace yanzun aka fara Amma na bar maganar." Sai tafiyarsu wajen goma na dare suka sami hutu ita da Uwale wace ta fara gyangyadi, Rahima tace taje ta kwanta, ita Kuma ta shiga toilet ta watsa ruwa, ta gabatar da nafilolin data saba kana ta haye gado, tana kwanciya aka Kira m waya, ta dauka cikin dariya "Haba Maryam nace miki zancen nan ya wuce ko .. "Wane zance kenan? Muryar Daktan ke tambayarta.Duk da cewa ba ganin fuskarsa take ba kunyarsa ta rufeta ta kasa magana for some seconds. Jin tayi shiru yace "Ko kin kife wayar ce?" Ta girgiza kai "Ah ah, da kace sai gobe zaka Kira... Yayi dan murmushinsa "Just want to say goodnight, ko nayi laifi?" Tayi saurin fadin "Ah ah ba haka bane." Wayar tasu kamar ta safe, babu wani kwakwkwaran magans, itama sai inda-inda sai kace saurayi da budurwar da suka kamu da son juna bayyana yai musu wuya. Suka aje wayat kowa da tunanin danuwa. 13/09/2020, 13:28 - Anty saliha:¦ˆRAHIMA..doc by jami 30 Kwanan Dakta biyar a kasar Riyadh ya kira waya cewan yana kan hanyar dawowa. Cikin kwanakin Rahima zata kira sarakuwarta su gaisa kana wajibi ne taci duk kalar abincin da ta girka don sanin muhimmancin ta. An kawo Abdul ya kwana biyu yaki zama aka maida shi inda ya saba, baki na ci gaba da zuwa ganin amarya, wasu collegues dinta, wasu 'yanuwanta dana angon, Hayatu ma zuwansa uku, yace wai yana debe mata kewar Yayansa ne, ya maisheta aunty Rahima yanzun duk da ta nuna bata so yace ina ai mukaminta yanzun yafi gaban a kira sunanta gaba gadi. Wani lokacin idan Hayatu ya zauna yana abubuwansa yakan rinka tuno mata da marigayi, saboda suna kama sosai, barkwanci yanayin son jama'arsu daya ba irin Yaya Haseeb ba. Taf! Shi wa yaga fuskar ma balle hakoransa da sunan dariya, gaskiya ko da take miskila, nashi ginshirar ya shafe nata. A ranar ta shidda da likitan zai dawo tunda suka idar da sallar asubah suka fara shirin tarbon ango. Sun shirya abinci da drinks (natural) kala-kala. Suna cikin aiki Uwale ta tsaya tace "Wai shin Hajiya in tambayeki mana, Kuma ba shishshigi nike son yi miki ba, kin kuwa shirya tarbon maigidan? Ta kalleta "Ban da wannan hidimar da muke yi, akwai nau'in abincin karkara da zaki nuna min a dafa masa ne?" Tace "Hajiya nifa ba abinci nike nufi ba, ina batun gyarane?" Rahima ta sake fadin "Kinada Mai ko turare mai kamshi ne ki bani?" Uwale ta dafe kai "Wai ni Allah Hajiya duk basu nike nufi ba, Sai dai Ina jin kunyarki amma tunda ya zama dole bari inyi miki bayani.. Shin kina ci ko shan 'yan abubuwan nan masu gyara mace? Misali mu mutanen kauye muna cin furen zogale, shan kindirmo, madara, kankana, aya rake da gwanda, to Kuma naga matan birnin ma suna irin nasu" Rahima tace "Me yasa kika yi min tambayar nan?" "Kaji Hajiya! Maigida irin Alhaji? Ni dai ga gudumuwata can na aika an kawo miki, sauran bayanin gaskiya da 'yar kunya tsakaninmu." "Hhmmm inda da kunyar da baki yi min zancen nan ba Uwale, amma nagode da kokari, mu ci gaba da aiki duk da bai Fadi lokacin isowarsa ba." Sai da suka gama gyara dakinta da cikin gidan tsaf sannan ta shiga dakin da aka shiryawa Daktan ta share ko'ina ta kara gogewa duk da daman ba datti a dakin tunda komi sabo ne. Air freshners kala-uku ta fesa a dakin bayan turaren wuta, dakin ya dau kamshi, ta koma falonsa nan ma hakan tayi, gidan gaba daya ya dau kamshi mai sa natsuwa da kwanciyar hankali. Zuwa la'asar tana zaune a falonta ta barbaje littafan da Maryam ta kawo Mata, iya kwakwan son karatunta ta kasa karanta ko da shafi dayane cikin kowanne littafi dalili da ta kasa natsuwa, sai wani fargaba da tsoro da taji motsi, har karar waya ta rinka imagining tana ji a kunnenta. Hhmmm! Kar dai Ya Haseeb ya sata zautuwa... Shiru bai iso ba bai Kira waya ba har bayan la'asar don haka ta sakankance ya fasa dawowa a ranar. Ta tashi ta canza doguwar rigar data sanya a jikinta ta saka wani simple sky blue, dinkin buba, ta saka silver earrings da chain dinsu hadi da bracelet da wrist watch water proof hade da zobenda data sanya a yatsunta na dama, yatsun hannu hagunta ta saka gold rings guda biyu madaidaita. Banda kamshin man enchanteur (stick deodarant) data shafa a armpits dinta, ta kara anti- perspirant deodarant, ta kara fesa perfume (Adorable) sai kamshi duk inda ta gilma. Dr Haseeb Junaid ya kalli rolex din dake daure a hannunsa da lallausar suma suka bi suka kwanta ya gama shirunsa tsaf ya juya ya kalli Zuwaira dake zaune gefen gado yace "Ni zan tafi ba wani abu?" Ta kallesa ta watsar bata tanka ba. Yai ajiyar zuciya ya mike tsam ya nufi kofa kafin ya isa ta rigashi ta taresa "Kana nufin can Dorayi zaka tafi yanzun ka kwana can?" Ya kura mata ido ta cikin glass dinsa yace "Me kike so inyi miki ne Zuwaira,tunda na shigo gidan nan kike neman ffitina, me kike so?" Ta Kara tare kofa "Me nake so? Ya za kayi min wannan shegiyar tambayar bayan wani gida kayi niyyar tafiya ka kwana, bani da right da zan tuhumeka?" Ya girgiza Kai "Ki tuhumeni for what reason? Look Zuwaira ki gane addini yaba magidanci damar sauka duk inda yaso in ya dawo daga tafiya in har ya mallaki mace fiye da daya, amma ga mai son kyautatawa sai ya sauka wajen uwargidansa ko wace take da girki a ranar, a al'adance. To ke na kyautata miki, na dawo na sauka a nan,tsawon lokacin dana dauka tare dake kika nuna tamkar baki san daga inda na fito ba, babu maraban arziki balle nuna jin dadi da hamdallah ga Allah cewan naje na dawo lafiya, banyi fushi ba na zauna tare dake har zuwa yanzun duba time karfe nawa ne, sai kuma zan fita ki taso ki dasa min wasu tambayoyin da basu dace ba? Me ma kike nufin da wai can zan kwana? To yes can zan kwana, idan kin manta ne in tuna miki yanzu ku biyu na mallaka matsayin mata ne, hakkin Rahima ma ya rayata a kaina yadda naki hakkin yake a kaina, wajibi ne in sauke nauyin da Allsh ya dora min nata, tunda an daura ba na Nan, kwana uku zanyi a gidanta, kana in dawo ku ci gaba da raba kwana yadda kuke so wace ban kwana gidanta ba wajibi in lekata da safe don ganin lafiyarta, Ina fatar kin fahimceni, bani hanya in wuce." Wai saita saka kukan kissa ta kama shi gam ta rike "Sabida Allah nu kadai zaka barni in kwana cikin katon gidan nan?" Ya girgiza Kai "Yau aka fara hakan? Idan ban barki kin kwana ke kadai ba ai ke kya barni ki tafi balaguronki ko, to meye na damuwa yau keda kike alla-alla ki samu kafar yawo?" Taci gaba da kuka wanda a zahiri tana yine don bata masa lokaci, ya dago manufarta, ya yakiceta ya raba daga gefenta ya fita, ta bisa har waje yayinda direbansa ya taso ya bude masa mota, yace Mata "Saida safe." Ya shige mota abinsa suka tafi. 13/09/2020, 23:21 - Anty saliha: ...ˆRAHIMA..doc by jami 31 Mal. Hassan ya dagewa direba murfin gate ya wuce harabar da aka tanada domin aje motocin. Uwale ce ta fara hango Maigidan ta tagar kicin yana gaisawa dasu Mal. Hassan bayan fitowarsa daga mota, direban ya bude boot yana fito da kayan dake ciki suka fara shiga dasu cikin gida. Rahima na can cikin bedroom dinta bata San bidirin da ake yi ba, kwance take rigingine ta kifa littafin da tsananin tunani ya hana mata karantawa a fuskarta kamar tana barci, zurfin tunanin da take yi ya hana jin sallamar da Dr Haseeb yayi. Ya dauka barci take ya Kara sallama har sau uku bata motsa ba, ya matsa ya shiga cikin dakin, taushin rug din ya hana mata jin takunsa, saida ya kai daf da gadon da take kwance, yaji sautin wata waka dake fita a wayarta, ta wasu samari da su Kai masa suna *I don't care who you're* Ya tsaya bisa kanta yai mata kallon tsaf cikin dakikoki...... Jikinta ya bata lalle ana kallonta, daidai lokacin ya duka ya kai hannunsa ya cire book din data kare fuskarta, daidai lokacin suka shaki kamshin juna, Rahima ta kai hannunta zata cire book din, already nasa hannun ya sauka a kafadarta. Ganin wanda yake tsaye kanta ta yunkuro ta tashi zaune a tsorace. Ba tareda yayi magana ba ya maidata kwance ganin yadda ta razana, tana ta kokarin fahimtar what's happening is real ba mafarki ne ba, tayi kokarin magana but shock ya hanata, shima a kidime yake don da za a auna jininsa a lokacin za a ga ya hau saboda bugun da zuciyarsa keyi very fast. Ya gyara muryar da zama very low yace "Sorry I didn't mean to scare you.' Ta saki ajiyar zuciya yayinda ta sake yunkurin tashi ta zamo kafafunta yaja da baya kadan still yana kallonta, ta cije tace "Sannu da zuwa, afwaan ban ji shigowarka ba, ya hanya?" Ya amsa "Alhamdulillah ya gida? Idanuwansa na kanta ya lura da kananan kitson da aka tsarawa sumanta da suka sauka har bayan keyarta kafin ta lalubi dankwalinta ta rufe kanta. Yana tsaye yana ci gaba da yi mata kallon kurilla harta mike ta gyara rigarta ta lalubi mayafi ta rufa kana ta fara kame-kame tace "Abinci na can dining ko sai kayi Sallah ka huta tukunna?" Ya bi da kallo ya share tambayar bai amsa ba saboda ya fahimci so tayi ya juya ya bar badroom din shi Kuma kamshin dake fita a hankali ya haifar masa da wani irin natsuwar da yasa yaji yana son zama cikinsa. Amma tunda yaga a rude take, bari ya hakura har ta samu natsuwa. Ya kalleta "Zan shiga dakina for now inada wasu calls before magrib." Rahima ta nufi kicin ta taradda Uwale da Haladu nata shirya kayayakin da ya taho dasu, sun aje komi a mazaunin da ya dace, suna gamawa Uwalen tace "Hajiya zamu sake dafa wani abincin ne?" Ta kada Kai "Ah wadanda muka yi suna cikin warmers ai ba abinda suka yi." "To ke fa? Naga kina son tuwo har na dora ruwan zafi?" Ta girgiza Kai "Ba Zan ci ba gaskiya sai dai ko ke, amma nagode da kokari." Uwale ta dafa cikinta "Ai nima din a koshen nike alhamdulillah." Rahima tace Shikenan "Zan shiga inyi sallar magrib sai anjima kenan." Ta bude baki "Saida safe dai Hajiya, maigida ya dawo wane hira za muyi yau?" Ta girgiza Kai "Uwale kina son shige mun hanci amma zan fyato ki." Tayi saurin durkusawa "Wace Ni uwar dakina, yafe min, amma kinsan gaskiya na Fadi." Ta shiga tana dariya "Hhhmm naso in ganki da kuriyarki Uwale, kin cika ban dariya. Wasu masu shigowa gidan Rahima suna korafin wai tana sakewa da 'yar aikinta da yawa, ita kuwa mace ce mai ba kowanne irin mutum darajarsa, ta Kan dauki kanta ita ba wata tsiya bace, bata wulakanta na kasa da ita saboda sanin kowacce halitta da irin darajar da Allah yai Mata, tsakaninta da masu aikin gidanta,, mutunci ne da girmama juna. Ta dade da idar da sallar isha'i amma ta kasa tashi daga sallayarta. Kamar yadda yaji kamshin dakinta hakan ya cika nashi dakin tun daga falonsa zuwa bedroom, komi ya Burgesa, tsarin yai masa daidai. Hhhmmm ya kasa zama sai tunani, shi bai ma san yadda zai bullowa wannan auren nasu ba duk da ya rungumi auren nan da hannu biyu. To ai ba nan gizo ke sakar ba, ganin irin dari-darin da ta fara yi dashi, to ai shi din ma bai saki jiki da ita ba although ya tabbatar da zasu gina rayuwar aurensu kan kyakkyawan kudiri saboda ya amince da ita duk da babu wata akaka ta soyayya tsakaninsu. Ya ji shuru bata fito ba, ya dau waya ya kirata cewan yana son ganinta a falonsa, kafin ta fito ya kagu da son sake ganinta da tsarin kwalliyarta, tayi masa kwarjini kwarai a fuskarsa. Bata fito ba saida ta saka hijab, ta isko shi tsaye gaban aquarium ya gama baiwa kifayen dake ciki abinci, ta danyi murmushi, ashe ra'ayinsu ma dayane wajen kaunar kiwon kifaye.. Bayan ya amsa sallamarta ba tare daya dago ya kalleta ba yace "Zauna mana." A natse ta zauna a takure tana kara yaba tsarin falon likitan, idanunta suka Kai kan babban hotonsa dake manne a bango da hoton tsohon shugaban kasa Sani Abacha. Shima din yazo ya zauna kujerar dake fuskantar ta yana kallonta ta kauda Kai, ya sauke ajiyar zuciya "Kin san illar tunani kuwa?" Ya tambayeta "Tunani yin kansa ya keyi ai balle Kuma idan mutum nada reason na yi din." Yace "Hakane, but na Kira kine muci abinci." "Ni na koshi gaskiya." Ya ci gaba da kallonta kanta a kasa dai ya ce "Ya za muyi kenan, bana cin abinci Ni kadai Kuma Ina jin yunwa ke Kuma kin koshi a cewarki, in hakura kenan?" Tana jin haka ta dago suka hada ido, zuciyarta ta buga da karfi saboda tun saninta dashi bata taba ganinsa ba glass ba, da ya cire sai ta fahimci yafi kyau da kwarjini, his gazing eyes sai haske suke yayinda yake kallonta.... Ta lumshe nata idanun ta budesu da kyar tamkar Mai shirin yin barci, Daktan yaji tsigar jikinsa ya tashi, shawa'awar amaryarsa ya diran masa a kahon zucci Wanda yasa ya manta da matsayinta na da can sai matsayin matarsa. Cikin rashin kuzari dalilin kasalar data taso ta lullubeta ta mike a hankali ta nufi dining table ta kwaso warmers din data jera ta maido su gabansa ta ajiye a bisa carpet kana tace "Ina rokon arziki ka sauko kaci komi kankantarsa. karka kwana da yunwa." "Bana magana biyu Rahima, as long as ba za muci tare ba na hakura." Ba yadda zata yi dole ta sauka ta zuba musu abincin a plate guda bisa umurninsa. Tafdijan ita bata taba cin abinci da namiji plate daya ba, ko Rabiu kuwa, dole haka ta daure cikin jin nauyi ta rinka tsakalar abincin, shima ba wani ci yayi ba sai uban nacin kallonta da yake duk ta tsargu kamar ta tashi da gudu ta bar falon. 14/09/2020, 17:50 - Anty saliha: ...RAHIMA..doc by jami 32. A takaice tare suka ci abincin suka gama ya tayata kwashe kayan zuwa kicin, niyyarta ta shige daki ta kwanta yace yana son magana da ita.. Suka koma falon suka zauna, tsawon lokaci bai ce komi ba, shi fa problem dinsa kenan, banbancin su day Rabiu karara ne yaushe shi zai tsaya yana jan aji kafin yai magana? Duk kokakarinta na avoiding tunanin Rabiu yaci tura. To wai me zai gaya mata nema yake wani shan kamshi kafin ya furta? Ta rinka motsi da kafafunta don ya gane ta matsu bai kula ba. Ita bata taba ganin mai kyuyar magana kamarsa ba, ashe kuwa za ayi zaman kurame, don idan takamarsa miskillanci gidan ya taras. Shin ko nauyin abinda zai fadin yake? Zuciyarta ta bada dam! Ba dai yana tunanin irin kusancinta da marigayi ya kasance tsakaninsu ba. Tafdijan! Aiki jawur!! Tunanin hakan ya haifar mata da damuwa maras misali, hawayen data rinka kokarin dannewa suka kubce suka fara gangarowa,sheshshekar kukanta ya zaburar da shi daga duniyar tunanin da ya tafi, nan take zuciyarsa ta shiga kuna don ya fahimci zubar hawayenta bai rasa nasaba da halinda suka tsinci kansu a ciki na *Mata* da *Miji* wanda iya dakewan mutum sai ya bara. Sai dai shi ya daukarwa kansa alkawarin rike Rahima da danta bisa amanar da kaninsa ya damka masa, yayi saurin ciro white hankerchief cikin aljihunsa ya share kwallar da suka ciko masa, ya zabura ya mike ya nufi fridge ya bude ya dauko fresh milk ya tsiyaya a 2 cups ya matsa kusa da ita ya mike mata 1cup "Sha madara ya sanyaya miki zuciya." Ta karba ta kurba sanyin ya ratsa makoshi ya shiga cikinta, ta rumtse ido ta bude sannan ta sake kurba kadan ta rike sauran a hannunta... "Rahima ya kira so, softly,. kamar ta cikin kunninta ya rada mata sunan har tsigar jikinta na tashi, ta kasa amsawa, ya sake Kira ta daga masa Kai alamun tana jinsa...tausayinta ya kamashi yayinda yaci gaba da magana kamar yanayi da karamar yarinya "Don Allah ki daina kukan nan, i hate to see a woman crying. Ina rokon ki kwantar da hankalinki kan al'amarin nan da Allah ya kaddaro mana, ba da yin mu bane, rubutaccen al'amarine Ubangiji ya kutso da hikimarsa ta wajen Hajiya, mu Kuma muka yi mata biyayya don bamu isa mu kauce abinda yai nufi a garemu ba, don haka hakuri da tawal'u ya dace muyi da duk wani tunani da ba zai haifar mana da komi ba illa damuwa. Nasihar sa ya shigeta sosai ya haifar mata da karin fitar hawayenta, ya kalleta "Oh my God! Ya furta cike da damuwa yayinda ya taso da hanzari ya iso gareta, ya mika hannu tamkar zai rugumota, ya taka burki yayi reverse tareda girgiza kai ya shiga yawo a falon yana ci gaba da rarrashin ta. Kamar yana Kara mata volume, cikin kukan tace "Nasan kaddara ce amma wallahi na kasa daurewa... Yayi saurin dakatar da ita "Karki bari bacin rai yasa ki kauce hanya ki kai ga sabo please, tunda har kin amince a barta a haka mu ci gaba da adduoin Allah ya yaye mana kuncin dake tattare damu, ya karemu daga dukkan sharri ya kuma tabbatar mana da alkhairin dake cikin aurenmu." "Ameen ya Hayyu ya Qayyum." Ta amsa murya can kasa Yayi dan murmushi yace "Nagode and in Sha Allah nayi miki alkawarin you'll never regret this marriage, yanzun kije ki kwanta ki huta kin sha aiki yau, gobe in Sha Allah zan daukeki muje gidan Zuwaira mu dauketa muje wajen Hajiya, in lokaci bai kure ba mu wuce har wajen su Umma da rijiyar Lemu da Galadanci." Tace "Duk yadda ka tsara hakan za ayi." Yace "Ki dai yi tunani, oh sorry na hanani dukkan wani tunanin da zai saki kuka, no more tears." Ta amsa "Zanyi kokarin daukar shawararka, nagode." "Ni ne da godiya ai, sai da safe kenan." Ya amsa mata wannan karon fuska a sake. Tace "Allah ya tashemu lafiya. Nan ta barshi tsaye ta wuce dakinta. Maimakon su kwanta kamar sun hada baki, kowanne daura alwala yayi cikin daki suka fara jera nafiloli da adduoin samun ingantacciyar rayuwar auren da tsabtatacciyar soyayya, kowanne yaiwa marigayi adduar samun rahamar Ubangiji sannan kowa ya kwanta barci. 14/09/2020, 17:51 - Anty saliha: ...RAHIMA..doc by jami 33. Sun tashi cikin farin ciki da annashuwa tamkar basu suka kwanta cikin kunci da damuwa daren jiya ba. Bayan ta gama azkhar dinta ne ta nufi kicin domin hadawa maigida abincin kalacinsa da hannunta musamman da ya kasance tun suna gida ita mai sha'awar girke,-girke ce har sukanyi gardama da Maryam da ta kance Mai aiki zata rinka barin wa aikin komi saboda mene amfanin ajiyeta to in ba domin mace ta huta ba? Ta Kan cewa Maryam mene amfanina idan ba zan shiga kicin in dafawa rabin raina abincinsa ba bayan ko turawa na fadin the way to a man's heart is through his stomach? Can Kuma ta tambayi kanta to ita so take ta shiga zuciyar Ya Haseeb ko kuwa shine rabin ran nata? Kafin ta shiga laluben amsa Uwale ta shigo ta rike baki"Me kuma zan gani Hajiya, don Allah ki fito ki barni inyi aikina." Ta juyo "Mun tashi lafiya Uwale? Ina hadawa Dakta abincinsa ne, ke sai kici gaba da namu dana baki." Tayi kasake alamun bata ji dadi ba. Rahima tayi dariya "Saki fuskarki Uwale, ba fa na shiga aikin ki bane, bana Raina kokarinki bane, ladan nike kwadayi, bayan haka ban son in zama irinsu Mamin Sahabi na cikin littafin Anti Bilki Mai suna 'yayan hutu' Kinga dole in zage damtse in kwato zuciyar mijina hanyar da addininmu ya yarda dashi. Uwale ta gyada Kai "Yanzun na fahimceki Hajiya, watau dai zaki Kar tsuntsu biyu da dutse daya, ga ladar da zaki samu wajen Allah don faranta ran maigida ga Kara samun matsayi a zuciyarsa, hakika iya girki na daya daga cikin abinda ke karawa mace martaba a idon maigidanta." "Yauwa kin gande kenan. Ai da kinji labarin yarinyar nan sai takaici ya kamaki kinyi Allah wadarai, bata iya dafa komi ba sai ruwan dumi, miji ya jibgo cefane amma ba katabus, ko da yake sakayar uwa aka samu da bata dage wajen nunawa diyarta yadda ake hidimar gidan aure ba.".. Uwale ta marairaice "Kaico an kuwa tafka asara, to Ni yaushe zan fahimci labarin nan, sai dai ko in Zaki taimaka ki karanta min Hajiya." Rahima tace "Ba damuwa.... "Amma Ina fatan ba yau ko gobe za ayi wannan karatun ba ko Uwale?" Muryar Haseeb da suka ji ba tsammani yasa suka yi tsit, sannan Uwale tayi karfin halin durkusawa ta gaisheshi cikin ladabi, ya amsa yana murmushi kana ya kalli Rahima "Me ake girkawane gidan ya cika da kamshi gashi har na kasa daurewa na biyo?" Cikin jin nauyi tace "Yi hakuri, Uwale ce ta tsareni da surutu amma gani nan na kusa hadawa." Ya juyo wajen Uwale "Haka za muyi dake? Ashe kina Shirin komawa kauye." Duk da tasan wasa yake tayi saurin durkusawa "Tuba nike ranka ya dade ayi min afwaa." Ya kalli Rahima yana murmushin da ya kashe mata jiki "Sai in uwar dakinki ta amince." Tace "Na amince." Tana kallon Uwale tana dariya a fakaice. Ya juya ciki "Ba komi, but kuyi ku kare kinsan zamu fita." Yana wucewa Uwale ta dafe kirji ta nisa "Allah ya tsare, yau da mutanen kauye sunyi bakuwa." Rahima tace " Wasa ce yake kin sani ai kinzo kenan shiga sojar baddakare, gashi naga alamun Mal. Hassan ya shiga cikin zauwarawa." Ta kama baki "Lah! Inji wa?" Tace ," In jini Mana, kinsan yanzun mutum ake kiwo ba dabba ba, Kuma kuna karkashina wajibi a gareni in sa ido inga yadda kuke gudanar da harkokinku inda yake da gyara a gyara ko da duk Kun girmeni, amma ku din amana ne a karkashinmu." Uwale ta jinjina "Tabbas a Kan Sami karamin da yafi wani babban kaifin hankali da hangen nesa, kina daya daga cikinsu Hajiya, gaskiya kika Fadi ya nuna ra'ayi nace sai nayi nazari shiyasa ban Kai ka shaida miki ba Uwardakina." Rahima tace "To ai auren shine darajarmu Uwale, Allah ya tabbatar da alkhairi." Karfe tara daidai na safe sun gama shiryawa. Dakta Haseeb ya fito cikin wata rantsatstsiyar shadda yar ubansu wace ake kira senators shadda amma Kuma an rinata ta fito kala biyu, ruwan danyen haki ne da gwaiduwar kwai, dinkin tazarce kamar ko yaushe sai maski take tana shining, ga wani kamshin turaren manya irin na kasaitattun mazan da suka amsa sunansu.. Rahima ta fito ta kallesa sai guda ta sadda kanta kasa saboda duk da ta saba ganinsa cikin irin yanayin, shigar yau ya Kara kwarjini da muhibba, a daya bangaren shima kallonta yake yana yaba tsarin shigarta, babban abinda ya burgesa ta bashi sha'awa shine les din data saka kalar gwaiduwar kwai ne, lapayya data nannade jikinta combination ne na deep green and yolk colours again, sai ya zama tamkar anko suka yi, takalman data saka kafafunta basu cika tsawo ba kuma ba flat bane, hade da yar karamar jakarsu an rubuta musu suna *sweet heart* Bai iya tantance sauran accessories din data saka saboda jikinta rufe yake ruf, gashi duk da bata fesa turare a jikinta ba, tana matsawa kusa dashi yaji wani mayataccen kamshi na fita daga jikinta. Murya a dushe yace "Mu je ko?" Suka yi sallama dasu Uwale suka fita. Motar da ya dauko yau jeep ce, Rahima ta kame a gaba yana tuki a hankali suna hira jefi-jefi har suka isa Galadanci. Bayan sun gaisa da maigadinsa again suka shiga ciki, kofar falon Zuwaira a garkame yake, ya tsaya ya danna karaurawa, shiru har ya koma buga kofar ba a zo an bude ba, yasan kuma tana gidan don ga motarta nan a harabar aje motocin,moreover ma tasan da zuwansa din, takaici ya cika yasa hannu ya fara dukan kofar kamar zai balleta da karfin tsiya sannan aka bude. Kishi! Kishi!! Ya turnuko Zuwaira ganin Haseeb da Rahima. Wani kololon bakin ciki ya tokare mata wuya, bata taba zaton irin haka zata ji idan taga mijinta da wata ba, ashe fa aiki na baya she made a big mistake data bari akayi auren Nan( kunji jahila sai kace ita keda ikon sawa ayi ko hanawa) Kuma har a da tana ganin zata iya rabuwa da miji irin nata ba tareda abin ya dameta ba, amma Ina! Ta canza salon rawar domin kidar ma ta canza. Tana son mijinta ba Kuma zata iya hakura ta barwa wannan Mai auren cin amanar shi ba? To wane mataki zata dauka yanzun? Sai dammarar kwato sa da karfin tsiya ko da masifa da bala'i, don Allah dubi abin takaici har yana wani dressing kala daya da ita,taja wani dogon tsaki ta juya bata amsa sallamarsu ba balle tayi musu maraba har ma ace ga wurin zama. Ya bita da kallo yace "Zuwaira haka Allah yace ki yiwa bakin ka?" Ta juyo a fusace "Yanzu Kai ko kunya ma baka ji na ka taso tsohuwar matar kaninka da sunan Wai matarka" Ya amsa "Ai ba wai matata ce saboda ba ke kadai zaki bada shaidan hakan ba har dimbin jama'ar da suka halarci daurin aurenmu, zaki zauna ku gaisa ko ah ah?" Ta sake buga wata shegiyar tsaki tana harare-harare, ta zauna kan hannun kujera tana kada kafa. Rahima sai kallonta take, a da can inda aka fito ta rinka girmamata a matsayinta na matar wan mijinta duk da cewan ba ta girmeta da wasu shekaru ne sosai ba sai girman jiki data fita sosai. A yanzun ma dole ta ci gaba da girmamata a matsayinta na uwargidan mijinta. Yes dole ne Aunty Zuwaira taji ciwon auren nan, dole tayi kishin mijinta, dole ta tsaneta to amma ita ya ta iya da ikon Rabbana? Da itace Zuwaira ba zata yi wani shirme da zai kawo raini tsakaninsu ba, idan ma kishin ne za tayi na 'yan birni irin kishin matan da suka san kansu. Ta zamo daga kan kujera ta rusuna "Aunty barka da kwana, ya kwanan su Khalifa?" Ta galla mata harara tace "Ke Kinga idan kina son kanki da arziki karki sake yi min magana saboda kin zama baka Mai bakar aniya, ki auri kani ki dawo ki aure was ko kunya ba kiji ba. Yanzun ke kinyi abinda ya dace kenan? Idan namiji bai san yakamata ba ke baki san ciwon kanki bane da kika amince masa kuna raba abin Fadi a gari?" Rahima ta dake "Aunty kina da damar fadin abinda kika ga dama don anyi miki laifi, Ni Kuma da kika gani na dauki kaddarar da bani na shiryowa kaina ba, tunda haka Allah ya tsara, haka yake son ganinmu, mun bi umurninsa, na rungumi mijina da hannu biyu, sai dai kiyi hakuri kema ki rungumi kaddarar." "Ba laifinki bane inji Zuwaira da take ta sakar mata harara, duk cin mutuncin da kika yi min sayo min aka yi aka zube cikin gidana, sai dai Ina gargadinki da abu days karki sake ki shiga harkata kota yarana, idan kika yi min shishshigin da kike yiwa danginsu Dakta ranki zai baci ki gwammace ba ki amince kinyi tarayyar miji dani Zuwaira ba." Haseeb ya gyara murya da yaga zata wuce gona da iri yace "Ba surutu ya kawo mu ba, idan keep n shirya ki taho mu tafi Yakasai." Ta kallesa a wulakance "Ban shirya ba, kaje na iskoka can." Ya fusata ya mike yace "Yanzun nan nayi niyyar mu tafi tare ko kin shirya ko baki shirya ba, karki maisheni mutumin banza, inace gudun haka yasa na kiraki a waya na shaida miki tun jiya?" Ta tashi fuu ta wuce cikin bedroom yai kamar ya kyale sai Kuma ya kalli Rahima yace "Excuse me." Ya bita ciki. Tsaye ya iskota tana wani jijjiga tana tsuma wai ita masifa na cinta, yai sallama ya shiga duk da bata amsa ba. Ya tsaya a bayanta cikin wata masifaffiyar sansanyar murya yace "Zuwaira kiyi hankali dani, duk abubuwan da kike yi ba za suyi komi dani ba, kin san Ni, kin San halina, idan Kika sake Kika kureni ke za kiyi dana sanin da baida amfani, na kawo yarinyar nan ki zauna ku gaisa ku fahimci juna abu ya gagara, Rahimar wata ce da baki sani ba? Kina ganin shirmenki zaisa ta ga kimarki ta girmamaki? ke ganinki wannan haukar da kike wace bata da maganin daya wuce hakuri ne mafita a gareki? To ki sani idan muka fita muka je gidan Hajiya, ko gidanku ko nasu Rahima kika kika ki kama kanki za kiyi mamakin matakin da zan dauka a kanki, and yanzun na baki only 5minutes ki shirya ki fito ko ranki ya baci." Yana gama maganganunsa ya fita. Ta tsaya tayi shiru na yan dakikoki kafin ta zabura ta fara Shirin dole domin tabbas tasan halinsa, zai iya Kyaleta tayi masa duk cin kashin da zata yi amma duk ranar data kai shi makura sai ya juye mata ta rasa gane kansa, duk iya kissa da dabarar ta bs zata ciwo kansa ba sai ya gaji ya sauka don kansa. Sannan wani abin takaici sannu cikin ruwan sanyi yake gasata, ita tunda take dashi bai taba daga muryarsa da sunan fada ba, sai dai ya kara zama cool. Tayi kwata, wallahi Haseeb green snake ne. Duk caba adon da tayi da wani jan material Mai sulbu yana shaking a jikinta bai burgesa ba, tana fitowa ya mike Rahima ta bi sahu, har zasu fita ya tsaya ya kalli Zuwairan "Su Khalifa school suka je ko Ina kika tura su?" Ta sassauta murya "Suna school, daga can zasu wuce gida." Yasa Kai suka bi shi. Hhmmm su Zuwaira ashe wargi wuri yaka samu. 14/09/2020, 22:44 - Anty saliha: ..ˆRAHIMA..doc by jami 34 Uwargida ta zauna gaba, amarya na baya, angon na tuki a sukuni, babu mai magana cikinsu duka har saida ya furta cewan akwai tsararbar da ya taho dasu a boot na Mahaifiyarsa da iyayensu kowanne da ledarsa. Rahima ta saurara taji Zuwaira tayi godiya bata yi ba, ta bude baki tace"Mun gode Allah ya Kara budi." Adduar ta yiwa maigidan dadi saboda bai taba yiwa matarsa ko iyayenta wani alkhairi tayi godiya ba, infact ita kullum gani take tunda yana aurenta wajibi ne yayin, idan yayi Kuma ba wani gwaninta ne a gareta ba balle har tayi godiya ta dora da addua irin yadda Rahima tayi masa ba, dadin da yaji yasa ya kallota ta mirror yace "Ameen nagode da addua. Cikin sakin fuska. Hakan ya Kara sa Zuwaira tsuke fuska. Suka Yakasai Hjy Kaltume ta tarbesu da murna da farin ciki, abin gwanin shaawa, suna gama gaisawa ta fara yi musu nasiha, ta fara da Uban gayyar cewan ya rike matansa da zuciya daya tsakani da Allah, yayi kokarin kwatanta adalci tsakaninsu, yaji tsoron Allah, ya tuna da mata da 'y'yansa amana ce a gareshi, yasan Allah ba zai barsa ba muddin yaci amana ko zaluntar wata. Ta juyo kansu tace "Ku Kuma kin zauna lafiya, ku rike mijinku fisabilillah, kuyi biyayyar aure yadda Allah ya umurceku dayi, ku sani aure ibada ne don haka ku tafiyar da rayuwarku da bin dokokinsa. Ke Zuwaira ki Kara hakuri, ki rike girmanki karki sake a rainaki, ki daure ki sanyawa zuciyarki salama, ci gaba bai samuwa sai inda aka yi hakuri.. idan ma an zalunceki ki kayi hakuri Allah zai saka miki .. "Dole a bani hakuri Mana tunda an riga sn zalunce ni, in gaskiya ne me yasa aka rasa wace za a hadashi da ita sai matar Rabiu?" Zuwaira ce ta katse maganar sarakuwarta... Hajiya da Rahima suka bude baki cikin mamaki.. Shi Kuma ya juya a hankali ya kalleta "Kinsan nayi warning dinki ko? Saboda nasan hakan zai faru, to wallahi idan Kika sake ce tak na nuna rashin mutuncin Mahaifiyata na gama aurenki tun a nan ba sai mun matsa ko Ina ba." "Innalillahi wa Inna ilaihirrajiun to ba a gabana ba, ba gidana ba, Kuma ban amince ka karya kadarin aurenku ba." A fusace yace "Hajiya zan yi mata hakurin komi a duniyar nan amma banda wulakanta min ke, sam ba zan taba yarda da wannan rainin wayon ba, idan ba rashin kunyar banza ba ta kalli kwarar idonki tana fada miki wadanan surutan, yau na Kara tabbatar da baki San mutunci ba, baki San darajar na gaba dake ba." Hjy Kaltume tace "Wallahi in don Ni na yafe kaima Kuma kayi hakuri, kasan bacin rai ne." "Bacin rai da akayi mata mene? Aure ne nayi duk abinda za kice kin dade, na auri matar kanina, aurene muke yi ba zaman banza ko?" Sai anan Rahima ta tanka "Don Allah kayi hakuri a bar mahanar." Ya gyara zama "Daga yau kowaccenku ta sani ban hada Mahaifiyata da kowa ba a duniya, haka ina kaunar 'yan uwana kaf fiye da zaton kowa saboda haka duk wace taga ba zata iya kaunarsu ko girmamasu ba zama dani ba dole bane.". Hjy Kaltume ta nisa "Ka cika mita, batun ya wuce ai, ina Kara horonka da kayi hakuri a matsayin Wanda ya tara, muna tayaku addua kullum Allah ya albarkaci rayuwarku." Har zuwa lokacin Zuwaira bata ce ayi hakuri ba, to bashi cikin policy dinta sam sabida a ganinta laifin me tayi? Daga fadar gaskiya kawai a dake ka a hana maka kuka a kan me? Sun baiwa Hajiyar tsarabarta wadanda suka kunshi duk abubuwan da yasan tana so ne ya karo mata kasancewar daman bata rasa komi ba. Daga nan gidansu Rahima suka nufa, Umma ta kasa rufe baki don murna, nau'ikan abinci ne aka jera musu na tarbonsu, gefe kayan sanyi ne da ababen motsa Baki, Umma akwai iya tarbon baki... Alh. Mamman na gida don haka bayan ya tsaya sun gaisa dasu Zuwaira yaja Haseeb suka koma soro suka shimfida tabarma ana gaisawa. Suna Nan har aka dauko Abdul daga makaranta yaga babansa ya daka tsalle ya haye jikinsa yana murna. A cikin gida Zuwaira tayi kasake tana kallon yadda ake nunawa Rahima so da kauna irinta tsakanin da da iyaye, ita Kuma tana basu girmansu, ta kanta domin da ita gani take ai 'gata ce a gidansu ashe gatancin Rahima shine gata Kuma ya dama nata ya shanye don ko ba komi gatan bai zamar mata wauta ba balle cuta. Tun tana daure fuska har ta gaji ta saki, to Umma macece mai harka ga iya zama da mutane, ta nunawa Zuwaira su basu iya hauka ba. Suma sunyi murna da tsarabar bakin sunyi godiya sosai. A rijiyar Lemu aininhin Mahaifin Rahima ya nuna Haseeb ba surukinsa bane, Lauratu ce tace ita kam surukutat za tayi da likitan, daga karshe duk da kunyar Rahima da yake ji bai hanata kebewa yai mata nasihohi ba kana ya hadasu yai musu addua, da kyar suka amshi tasu tsarabar suna sa albarka A gidansu Zuwaira kuwa sai ta canza, basu dade da shiga gidan ba ta nunawa Rahima cewan gidan ubanta ne ta wuce gaba ta barta, Rahima ta saki fuska tamkar ta taba zuwa, suma iyayen Zuwaira da 'yanuwanta sun mata kyakkyawar tarbo, suka karramata.Tayi mamakin ganin ingantattar tarbiyyar sauran yaran gidan, kenan kan Zuwaira aka samu zakka. Ganin irin yadda iyayenta suka amsheta da hannu biyu yasa tayi kudurin zama lafiya da diyarsu duk iya fitinar da zata tayar don sunyi mata halacci, sunyi musu nasihohi da adduoin suma.Abdul ya lakewa yan uwansa da suke gidan, suma din kakansu yace su bi iyayensu gida. Zuwaira tayi kwatakyas data ga irun tsarabar da mijinta ya jibgowwa nata family din, duk inda suka fito nasu bai Kai na gidansu yawa ba, yayi hakan ne sabida yawan da suke dashi amma ba dominta ba... Sai karfe goma na dare suka koma gidansa na Galadanci inda ya mikawa kowa nata tsarabar dana Yara. Sun tashi tafiya Uwargida ta hade rai, Rahima tayi mata sallama ta amsa a ciki bata kula ba ta rike hannun Abdul su tafu yaron ya cije shi wajen su Khalifa zai kwana, suma suka ce ki dai a barsa wurinsu, ko su bishi dorayi su kwana can, Rahima tace a tarkato mata su tafi can gaba daya. Zuwaira najin haka tace "Gaskiya ba inda zasu." Yaran suka sa kuka, uban ya wuce cikin bedroom dinsu ya kwaso kayansu ya tasa su a gaba su ukun ya saka a mota kana ya cewa "Rahima ki tafi ku shiga mota Ina zuwa. Taja hannayensu suka fita waje. Tana fita ta fara yarfa ruwan bala',in don me za'a kwashe mata yara ya kai gidan wata, Kuma ba'a tambayeta izni ba. Ya kalleta " "Gidan watan da kike ikrari gidana ne, yarana ne akwai wanda ya isa ya hanani daukarsu ne tunda can naso su kwana?" Ya barta baki bude yai gaba, su kuwa Yara sai murna suke. 15/09/2020, 12:01 - Anty saliha: ..RAHIMA...doc by jami 35 Suna shiga gida Uwale ta taimaka mata suka yiwa yaran wanka tayi musu Shirin kwanciya sannan ta kaisu dakin da aka kebewa Abdul ta shafe kowannansu da azkhar din kwanciyar barci, suka kwanta, ta sakayo musu kofa ta koma dakinta ta fada wanka itama. Tana gama wanka ta dauro alwala, Rahima ko yaushe cikin alwala take dare da rana, ko ya karye zata sake wata saboda malaminsu ya fada musu muhimmancin yin hakan, Wanda ke kwana da alwala mala'ikun rahama Kan bi kowacce kafar gashinsa suna yi mada addua da neman gafara, sannan duk wani shaidanin maridin aljani ba zai kusance shi ba, haka shaidan la'ananne zai nisance shi. Tsaye take a tsakiyar dakinta daure da katon towel bayan ta fito daga toilet, ta dauko man shafawarta data hade da turaren miski ta fara shafawa tana maming wakar nan ta back street boys *I don't care who you're , where you're from, what you do, as long as you love meee* Kamshin dake fitowa daga cikin dakin ya fa fara dukan hancinsa, Yana isa daf da kofar yaji 'yar karamar muryarta na maming wakar da yake son shima, ya kara kutsa kai Yana sallama amma bata ji ba sabida ta shafa'a tunanin maigidan fa na iya shigowa ya ganta ba sutura a jikinta, idan ya ganki fa, ba mijinki bane wata zuciyar ta bata amsa.. Bata ankara ba kawai taga mutum a gabanta, taja da baya a firgice ta bude baki zata buga ihu.. Tafin hannunsa yai saurin sawa ya rufe bakinta tareda yi mata magana a hankali"Me yasa kika cika tsoron tsiya ne?" Ta saki numfashi jikinta ba inda bai rawa, ganin haka yasa ya janyota garesa ta langabar da Kai, kafafunta sunyi sanyi da ace bai riketa ba zata iya kaiwa kasa. Haseeb ya kara mannata a jikinsa har tana jin bugun zuciyarsa, ta dago a hankali tana kokarin kubcewa Amma baiyi niyyar rabuwa da ita ba, wani abu take ji Wanda bata taba experiencing ba... Ya tallabo gemunta don ta kallesa, hasken da taga kwarar idanunsa na fitarwa yasa tayi saurin rufe nata idanun, yayi mumushi "Wai wace irin kunya ce haka da taki karewa?" Tayi shiru ta Kara rumtse idanun. "Rahima bude idanunki ki kalleni." Ta girgiza Kai ta Kara cusa kan nata cikin jikinsa tana shakar kamshinsa. Ya sumbaci tsakiyar kanta, warm lips dinsa suka haifar mata da kasala, ya sassauta rikon da yai mata da niyyar kissing dinta... Wayarsa dake cikin aljihunsa ta fara sound na alamun an kirasa, ya share bai daga ba harta tsinke, aka sake kira, kamar ba zai daga ba again, ya tuna matsayinsa da irin aikinsa na ceton rayukan al'umma, nan da nan ya fiddo wayar ya daga yana sauraren mai kiran, kusan minti biyar kana ya aje ya tsaya yana kallon Rahima data koma gefen gado ta zauna, ya matso ya tsugunna a gabanta.. "Ina fatan lafiya.'. Ta furta da taga yanayin damuwarsa. Ya dafa gwiwarta "Dr Kabir ne ya Kira cewan mun Sami wata patient daga Maiduguri tun dazun Kuma yayi iya nasa kokarin babu canji so zanje mu gani may be sai anyi mata surgery don jini ne ya shiga kwanyarta sanadiyyar accident da tayi." "Subhanallah Ubangiji ya bata lafiya, me zan taimaka maka yanzun don ka hanzarta shiryawa ka tafi?" Rahima ta Fadi cike da tausayin matar da bata sani ba Ya mike tsaye cikin zafin naman nan nasa "Ki dai tayamu addua please, sai na dawo." Zuwa karfe 12: am Dr Haseeb da sauran likitoci hudun da yake jagoranta sunyi nisa da binciken kwakwalwar patient din, sun Kara daukar awa uku cur kafin su ciwo kan problem din a inda ya yanke shawarar ba sai yayi mata surgery ba, abubuwan da suka yi mata zai taimaka jinin ya rinka gangarowa ta hancinta ana zukewa har yayi clearing. Bayan nurses sun Kai patient din dakin jinyar kuma ya shiga ya dafa kanta ya dade yana karanto adduoin samun shifaa gareta, wannan al'adarsa ce ga patients din sa Kuma Ubangiji na amsar adduoinsa yasa a samu waraka ko da an yanke teammanin samun waraka. Mijin maras lafiyar ya rasa irin godiyar da zai yiwa Dr Haseeb tunda ya shaida masa she's out of danger. Kwarai Alh.Ahmad Sharif ya yaba da kwazon gwarzon likitan musamman ganin irin dedication dinsa kan aikinsa, gaskiya he's very committed to his job.Dr Haseeb ya maida kansa bawa wajen geagwarmaryar ceton rai ko neman lafiyar duk maras lafiyar da aka kawo asibitinsa. Wata damuwa da Alh Shatif ya gabatarwa Daktan shine cewan basu San kowa a garin Kano ba labarin asibitin kawai suka ji ya dauko matarsa suka yo gaba, tunda satinta biyu da yin hadarin, bayan kukkujewa da tayi nan da can ne sai ta fara sumbatu Kuma, barci yai kaura daga idanunta, sai anga sauki abu ya dawo, so wasu ne suka basu shawarar su kawota wajensa. Daktan yace ksr ta Sami damuwa harkar accommodation, asibitin sunyi tanadin guest house dab da asibitin saboda irin hakan.Batun hidimar abinci kuma zaisa matarsa ta aiko. Alh Ahmad Shariff ya fara zuba godiya Daktan ya katse shi cewan musulmi duk inda yake danuwan musulmi ne, Kuma shima an taba taimakonsa. 15/09/2020, 18:50 - Anty saliha: ...RAHIMA..doc by jami 36 Rahima ta kalli agogon dake manne a bangon dakinta, dare ya fara tsalawa, karfe daya harda wasu mintoci amma shiru maigidan bai dawo ba.Ta saki ajiyar zuciya auren likitan kenan, wata rana ma can zai kwana that's why ake son matansu su kasance masu hakuri da dangana. Ta juya gefe, ita ta rasa dalilin da idanunta suka kekashe ta kasa barci bayan na tattare da gajiya. To me ya hanata barci kuwa illa tunanin da ace maigidan bai fita da yanzun suna tare watakila ma a shimfidarta? Oh ni Rahima, shin Ina kunyar Ya Haseeb ya tafi ne har nike irin wannan tunanin?Anya kaunar da nike masa zata boyu kuwa? Barci ya fara fisgarta tana kokarin bude idanu amma ina! Sarkin karfin ya dauketa... Har ya shigo cikin gidan ya shiga dakinta bata sani ba, barcinta yai nisa, yayi kamar ya tasheta ya fasa. Duk da barci take ta Kara yi masa kyau da kwarjini, bai iya tantance tsananin bugawar da zuciyarsa keyi, shin dalilin matsanancin sha'awarta ce ko kuwa so ne ya fara surfafar zuciyar? Tunda baida amsa a lokacin, ya matsa kusa yasa hannu ya gyara mata hannunta data lankwashe tareda shafa kanta a hankali. Jikinta yai dumi amma ba na rashin lafiya ba, duk yadda yaso ya daure abu ya faskara ya duka yai kissing chicks dinta, ta dan motsa kadan taci gaba da barcinta kan dole ya cije ya nufi dakinsa ya kwanta. Qira'ar qur'anin da take yi ya bashi tabbacin ta jima da tashi, shima sai da ya kare nasa ya nufo dakinta yai zaune bakin gadonta yana jiran har ta kammala ta shafa adduointa sannan ta mike cikin natsuwa ta isa dab dashi ta tsugunna. "Ina kwana, ya kaga mai jinyar?" Ta fadi a hankali. "Lafiya lau, jiya ban dawo ba sai muka tabbatar bata cikin wani hadari, insha Allahu zata sami sauki." "Ubangiji ya amince ya bata lafiya, nima da har na tsaya jiran dawowarka unfortunately, barci barawo ya dauke Ni ban farka ba sai asubah." "Yes ai ma shigo na samu kinyi nisa sai na kasa tashinki saboda you were sleeping like a baby, looking so beautiful and innocent, naji kamar in zauna kawai in yita kallonki." Kunya ya kamata "Lah daka sani ka tashe Ni... Ba wani jin kunya ya kalleta yace "Kinsan abinda zai faru da na tashe ki?" Ta mutu a zaune.. Wai me ke damun Ya Haseeb ne yake zaro zancen da bai dace ba? Nauyin jin kalamansa yasa ta kasa dagowa. Ya girgiza Kai yana murmushi yace "Ba ni da amsar maganata kenan?" Ta daga kai alamun amsar sa. Yace "Hhmmm ashe zan zo in fara adduar Allah ya rage miki jin kunyar saboda idan baki saki jikinki dani ba ya za muyi zaman auren kenan?, I mean if you're not free with me ya Zaki lakanci halina, in san naki Kuma?" Tace "I will try my best." "Yauwa haka ya kamata, yanzun taimakonki nike nema kan patient din da aka kawo jiya.... Ya zayyane Mata halinda suke ciki da irin taimakon da yake son yi musu." Rahima tace "Ba damuwa Allah na taimakon Wanda ya taimaki wani. Bari inje mu shirya musu breakfast sai in shirya mu tafi tare?". Ya amsa "Okay, godiya nike." Sun isa asibitin kenan Allah ya nufi Hjy Fatima da farkowa daga barci daidai maigidanta Alh. Ahmad ya shigo cikin asibitin suka hadu da babban likita a nurses station, ya mikawa likitan hannu suka gaisa, Daktan ya tambayesa "Ya kwanan patient din tamu?" Alh. Ahmad ya washe baki yace "Ai naga abin mamaki jiya kamar wani magic wallahi tunda kuka gama dubata baiwar Allah nan ta samu natsuwa tayi barcinta lafiya, ba buge,-buge, ba wasu 'yan surutai da take yi a can inda aka fara dubata. Dr Haseeb yace "Alhamdulillah, yanzun tunda mun samu tayi barcin fiye da awa shidda, brain din ta zama relaxed, yau zamu sake sakata cikin na'ura mu bincika sosai ko da wata matsala a San matakin da zamu dauka, idan iyakar problem din da muka riga muka gani jiyane kawai, mun shawo kanta tun jiya din ma said mu jira karin samun sauki, Allah yasa mu dace." Ya amsa "Ameen Dakta, muna fa godiya sosai Allah ya Kara hasken ilmi." Yana magana ya kalli Rahima yace "Ikon Allah ga wata kamar 'yaruwa." Dr Haseeb ya kalli matarsa, ba shakka irin shigar nata ce tayi ta nannada lapayya, tayi kama da bare-barin, shi ko bata saka shi ba takan yi masa kama da matar kasar Chad. Ya sake bin ta da ido, ya juya yaga yadda Alh.Ahmad ke wani washe baki, kishi ya turnukoshi har yaji mamakin kansa, ya gyara murya yace "Wannan amaryata ce Alhaji ta shigo wajen ita patient din ce at least taji ko akwai abinda suke so tunda ku baki ne." Alhajin ya gintse dariyarsa har dai daya lura da canjin fuskar Daktan, ya gyara tsayuwarsa yace "Masha Allah, Allah ya sanya alkhairi da albarka cikin auren, sannu Hajiya." Ta amsa a darare saboda itama taga yadda mijin nata ya hade gira, miskillancin ya taso kenan ta fadi a zucci. "Ina dakin da pateint din take?" Ta tambaya aka nuna mata. Soyayya gamon jini, haka Allah shi ke hada mutaneya sanya kauna tsakaninsu. Mintoci kalilan da shiga Rahima wajen Hjy Fatima Allah ya hada jininsu,bayan sun gaisa suka Dan fara hira a hankali kafin su saki jiki tamkar sun taba haduwa. Rahima ta zuba mata abincin kalacin data kawo musu ta rinka bata a hankali tana ci bayan ta taimaka ta jingina mata pillow ta zauna. Hjy Fatima farar mace ce doguwa Mai jiki, kyakkyawa ce, tana da tsagen bare-barin a fuskarta sunyi mata kyau.. A haka mazajen suka tarad dasu suna hira. Hjy Fatima ta kalli mijinta dauke da murmushi a fuskarta "Alhaji kaga matar Dakta ta zama kanwata ko, me zamu cewa wadannan bayin Allah, da miji da matan kirkinsu ya Kai!" Alh Ahmad yace "Ki bari kawai, wallahi na rasa irin godiyar da zanyi, wannan dawainiyar sai dai Allah ya biya." Ta gyada Kai a hankali "Sai Kam addua garesu kawai.". Dakta Haseb ya matsa kusa da gadon patient din ya dau file dinta dake sargafe yace "So Hajiya ya jikin naki, da kika farka akwai jiri ko ciwon kai?" Ta amsa "Alhamdulillah tunda na farka banji komi ba gaskiya, sai dai dan nauyi kadan da naji kan yayi min." Ya gyada Kai "Yes is expected, shima zai bari a hankali don haka kar kice za kiyi garaje a bi a hankali ko? " "Toh Dakta mun gode sosai, na Kuma gode da ka hadani da kanwa ta muamman." Ya kalli Rahima yai murmushi sannan yace to za kuyi min afwaa ku tsahirta mu duba patient please. Rahima kije office dina ki jirani." Ta yaba kwarai da tsarin office dinsa, komi tsaf-tsaf, ya kawata office din da hoton shugaban kasa Dana gwamna masu ci yanzun, sai hoton marigayi Sani Abacha again, still da karamin *Aquarium* dauke da wasu kananan kifaye kala uku Kuma kwara ukun tal kyawawa dasu suna ta yawo cikin ruwa. Bisa tebur dinsa frames ne guda 4 kanana masu dauke da pictures din Hjy Kaltume, su Khalifa da Abdul dinta, Bata yi mamakin ganin hoton Abdul ba don irin shakuwarsa da yaron. Ta gaji da zama ta mike taje gaban aquarium din Nan ta dibi abincin kifayen nan ta rinkka zuba musu tana musu magana. Ya bude office din a hankali ya shigo, bai tsaya ba sai a bayanta yace "Sorry though naga kin samu abokan hira." Ba damar ta juya saboda yayi kusa da ita sosai, ta amsa "Tace yes na samu friends, sunada sunaye kuwa?" Ya Kara matsawa har kafadarsa na gogan kanta yace "No na bar miki wannan aikin.' Ta girgiza Kai "Ni dai a bar min wadancan na gida, ka rike wadannan." " Toh naji, idan na kirasu da sunan colours dinsu, yellow, red and green ba laifi ko?" Ta daga kafada "Okay, idan sunyi maka, Zan Kira nawa *piece, blessing& comport* Yace " Gaskiya ban yarda ba ai wayo kikai min." Tayi murmushi kawai. Yace" Shikenan sai me, Ina zamu yau?" Tace "Kace gidan su googo da Malam zamu, na rokeka ka ajiyeni gidan Maryam har ka manta?" Ya sauke numfashi "Na tuna hakan za ayi but ya zaki yi da sabuwar Auntyn ki?" Tace "Maryam zata kawo ni asibitin daga nan ta ganta sai in sameka a nan mu koma gidan, ba zaka je gidan Aunty Zuwaira ba?" "Yes na kirata ma bata jin dadi." Tace "Subhallah, Allah ya bata lafiya,don Allah ka gaida min ita." Yace "Je ki sallami kawarki ki taho mu tafi." Rahima ta koma wajen Hjy Fatima ta Bata hakurin cewan zata tafi ta dawo zuwa dare." Tace "Ba komi zuwa lokacin ma insha Allah yanuwanta sun iso don suna hanya." Suka Kara yi Mata godiya itada mijinta ta fito ta isko Daktan suka shiga mota suka fito daga asibitin. 15/09/2020, 22:31 - Anty saliha: ..RAHIMA,..doc by jami 37 Daktan da Rahima sun kewaya gidajen da suka ce zasu tafi daga karshe ya ajiyeta gidan 'yar uwarta ya wuce gidan Zuwaira. Alh. Abbas ta fara karo dashi a kofar gida kafin ta shiga ciki, bayan sun gaisa ya fara mata barkwanci "Daman kuwa Ina Shirin tahowa gidanku amsowa abokina magani.". Tayi dariya "Kai dai baka rabo da ban dariya, Daktan ne ma zai bashi magani?" Yace "Yes idan anyi masa ai an rage masa zafi." Tace "Ko dai a Kara masa." A cikin gida sun jima suna hira da Suwaiba da Maryam, inda Rahima ta basu sha'awa sam taki amincewa suyi hirar Zuwaira, duk inda suka bullo saita kauce, to ribar me zata ci idan taci naman 'yaruwarta musulma a cewarta. Saida suka kebe, Maryam ta tabota "Ke ina labari, ya canza kuwa?" Rahima ta nisa "Sosai ni har tsoro yake bani, ya canza ya rage daure fuskar, sai dai na kasa sakin jikina dashi gaskiya." Taja tsuki "Ai tsiyarki kenan, don me ba zaki saki jiki ki sakata ki wala da mijinki ba alhalin yana sonki tun kafin a daura aurenku na fahimci kuna son juna, amma kuna abu kamar wasan yara? Anyway kuka sani." "Ni kuwa dadi dake wutan ciki, Ina amfanin garaje? Sannu bata hana zuwa ai." Maryam ta zaburo "Amma a dade ba a Kai ba kuwa a rinka kallo ana hadiyar miyau, look Rahima nasan rawar jiki da saurin bada Kai na ragewa mace kima a idon namiji, inda yawancin maza ma Kan fassara hakan da rashin kamun Kai ga ita macen. Idan nace kamun kai Ina nufin natsuwa a gaban masoyi cikin kowanne hali da kuma cikin jama'a, rashin natsuwa na zubar da mutuncin mace, natsuwa kuwa kara mata daraja yake yi a idon jama'a da masoyinka. Duk da ya kasance wannan muhimmin al'amarin ne a rayuwar Mata, ba a son mace ta kasance miskilan gaske kar kuma ki zama mai sakin fuska, ba a son mace ta zama mai yawan washe baki tana dariya ba natsuwa a yayinda ta zama ba mai daure fuska ko da yaushe ba, ta dai zama tsaka-tsaki. Rahima ba nace kiyi masa shishshigi bane din hakan nasa kiyi saurin gundurarsa, dole ki rinka kina ja da baya amma ba kowanne lokaci ba, lokacin da kika lura miskillancin sa ya tashi sai kin kebe sai ya warware. Karki zama mai tsananta kwalliya fitar hankali, Kar Kuma ki kasance kazamiya. Ki tabbatar da kina faranta masa rai, kina bashi shawarwari na gari, ki zama Mai danne fushinki idan ranki ya baci, ki yawaita bashi hakuri idan ya nuna kinyi masa laifi koda kuwa kece da gaskiya. Ki zama Mai lura da hidimomin da suka shafi hakkokinsa na gida da waje, ban ce ksr kija masa aji ba don mace kike amma aja a hankali sannu sannu don namiji tamkar yaro yake ko da suka Raina mu sai dai bamu so juya su ba, ba boka ba mallam, ah ah ko alama, so da kauna, ladabi da biyayya, hakuri, yi nayi bari na bari sai su mallaka miki mijinki a tafin hannunki don duk namijin da yai dace da macen da take tsare masa wadannan dabiun y dace ya kyautata mata shima ya guji bacin ranta yadda take gudun nasa don yasan ya ajiye matar kwarai cikin gidansa unless ya zama butulu wannan Kuma Allah ba zai barsa haka ba zai fitar miki da hakkin ki. Ke din karki zama Mai danne hakkinsa, idan ma wani laifi ne gara ya fito daga garesa. Idan kin daure Allsh SWA zai daukaka darajarki." Raf-raf-raf! Rahima ta tafawa Maryam "Yanzun Kam babu mai kama ki da laifin karatu ba amfani cikin marubutanmu naji sai gaba yake yi, nagode 'yaruwa, zanyi iya kokarina da taimakon Allah." "Oho na dai fita hakkinki, ni yanzun ma Dakta nafi baiwa laifi.' Ta bude baki "Wane laifi Kuma?" Ta muskuta "Ah to ba namiji yake ba sai yace kule ace masa cas! Ko sai zuciyoyinku sunyi bursting?" Rahima ta jinjina "Wane irin bursting Kuma?" "To in baku ba ya za ayi ina so Ina kaiwa kasuwa?" "Allah ya shiryeki a bar batun Ni dai." A nan suka hadu suka dafa abincin da zasu Kai asibiti, Maryam ma tace tana neman ladan. Karfe takwas na dare suka koma asibiti harda Alh. Abbas inda suka taras da 'yanuwan Haj.Fatima sun iso lafiya. Matafiyan uncles dinta ne su biyu da kanwarta Falmata wace zata zauna tareda ita har ayi sallama. Lokaci kankani matan suka zama tamkar 'yanuwa, Falmata sun sarke da Maryam, ita din zawarci take kuma bata taba haihuwa ba a inda ta fiton, Hjy Fatima kuwa yaranta hudu, maza uku mace guda, bata da kishiya, sai ma dalilin wannan hadarin ne da yaso ya zama kamar ta samu tabuwar kwakwalwa dangin miji suka fara batun ya nemi wata matar, bai dai saurari kowa ba a lokacin hankalinsa tashe yake yana neman wa matarsa uwar 'ya'yansa hanyar da zata samu waraka, bisa dukkan alamu Kuma an dace. Sai karfe goma saura Alh Abbas da Ahmad Shariff suka shiga cikin ward din, Abbas yacevwa Maryam ta taso su tafu gida akwai alamun hadari ana walkiyya. Da jin hakan Rahima ta mike itama tace zata bisu su ajeta kawai tunda har zuwa lokacin Daktan bai dawo ba. Koda suka ajeta basu tsaya ba saboda hadari na shirin tasowa, Maryam ta leko kai ta windo tace "Ya za kiyi yanzun na sanki da tsoron ruwan sama." Rahima tace "Kin cika tonon silili saida safenku." Ta shige gida Kai tsaye dakin Uwale ta wuce ta sameta har ta kwanta, ta tashi zaune "Oh a gaisheki Hajiya sai yanzun?" Tace "Ke dai bari, yau ma zirga-zirgan muka sha duk na gaji, wanka kawai zanyi in kwanta." Uwale tace "Ga garin ma da alamar ruwa za ai Mana." Ta wuce tana fadin "Allah ya bamu Mai albarka, mu kwana lafiya." Kasancewar ta gabatar da sallolinta cire kayan jikinta kawai tayi ta fada wanka, inda Saida ta cika bath din taf da ruwan dumi, ta zazzaga bath salt a ciki, ruwan ya dau kamshi da kumfa Mai sulbu, ta shige ciki tayi wanka ta fito ta gabatar da alwala ta fito. Ta goge jikin da yayi smooth, bata shafa mai ba balle wani make up, just turare ta mutstsuka a jikinta ta saka cotton night dress tana tunanin may be weather din yai sanyi a dalilin ruwan saman da taji yana shirin saukowa. Tayi adduointa ta kwanta, ta dauki wani novel ta bude ta fara karanta shafi guda ta rufe, hirarsu da Maryam ne ke mata yawo a kai. Ba shakka gaskiya ta fada mata hakika son mijinta ya mamaye zuciyarta ba karya, yanzun ne ta Kara fahimtar maanar so da kaunar wani, watau da shirme take, to Allah yasa ba tana abin nan da hausawa ke Kira *son ma so wani ne* ba. Ai da kuwa wahala ta ganta, oh oh Allah Mai yin yadda ya so, ya dauke kani ya hadata da wa to Amma a wane babi take cikin zuciyarsa? Ta zabura ta tashi, tunda ba amsar zata samu ba is better ta tashi ta gabatar da sallah ta Kara addua. Ta shafa kenan taji dawowar Haseeb. 16/09/2020, 06:08 - Anty saliha: RAHIMA...doc by jami 38 Ya shigo ya sameta kan sallaya, mamaki ya nuna a fuskarsa amma yace "Kin ganni sai yanzun ko? Kiyi hakuri." Ta kada Kai "Ya Mai jikin?" Ya amsa "Da sauki malaria ce ke damunta." "Allah ya saukaka, ba wani abinda kake so don kwanciya zanyi?" Yace "Akwai, but kiyi min hakuri inyi wanka please.". Ya fita yana tunanin why ta daure fuskarta tamau haka, ba dai kishi ke damunta ba itama, idan hakane zaiyi farn ciki don alama kenan na kamu da son sa kamar yadda yake jinta a zuciyarsa. Bayan fitarsa tayi kasake! Lalle ma namiji sai a barsa kawai, ji yadda ya shigo yana mata wani shan kamshi sai kace in laifinne bashi yayi mata ba ya dawo Yana tabarmar kunya. . That's why fa Ubangiji yace ba zasu iya adalci ba sai dai su kwatanta. Hhmmm Kar shaidan ta xugata tana zargin abinda bata gani ba ance ko zato zunubi. Tausayin Zuwaira ma ya tsirga mata dole fa ne baiwar Allah Nan tayi kishin mijinta... Ya sake dawowa ya ganta zaune inda ya barta "Har yanzun adduar ake ne?" "Ah ah". Ta amsa a takaice. Yace "Allah ya karba mana amma da kin matso nan ko haka zan rinka maganar kina can Ina Nan?" Ta mike cikin rashin karsashi ta dawo dab da gadon da yake zaune a kai ta zauna. 16/09/2020, 22:25 - Anty saliha: ...RAHIMA..doc by jami 39 Ya kalli yadda ta wani takure a gefensa ya girgiza kai yace "Rahima ya dace ki fahimci matsayinmu na ma'aurata, meye kike dari-dari?" Tayi shiru bata amsa ba, yaja numfashi yace "Gobe idan Allah ya kaimu kwanaki ukun da aka tanadar mana zasu kare sabanin kwanaki bakwai na auren budurwa. Wadannan kwanaki Kuma ba an kebe sune kawai don ango da amarya su hole ba kadai, ah ah ana son miji ya koyar da matansa abubuwan da ya lura bata sani ba dangane da addini ko zamantakewar auren ma gaba daya. To alhamdulillah! a 'yan kwanakin da muka yi tare nasa ido kan yanayin ibadarki abinda na gani abin yabo ne sosai, sai dai duk da haka wajibi ne gareni in miki wasu tambayoyin kan addinin don sauke nauyin dake kaina, kin fahimce ni?" Ta dago kai ta amsa "Na fahimta, me kake son sani?" Ya gyara zama "Ki karanta min suratul fatihatul kitaab, ki fada min farillan alwala, sallah da sunnonin su." Ta nisa tukunna kafin ta da basmalla ta kare karatun kana taci gaba da jero wadanda ya bukaci sanin." " Masha Allah Rahima, na godewa Allah da ya nufeni da aurenki, Allah yasa diyanmu su amfana da ilmin da ya bamu." Ta amsa "Amin ya Hayyu ya Qayyum, nagode da yabawa." Daktan yayi dan murmushinsa kafin yaci gaba "To bayan wadannan akwai 'yan abubuwan da nike son in Kara miki kwarin gwiwar ci gaba da aikatawa, alal misali na lura kina yawaita alwala ko yaushe, yana da kyau matuka, ko kina cikin tsarki ko jinin haila domin Manzon Allah SAW yai Mana nuni cewan duk Wanda ya kwanta da alwala ya gabatar da azkhar din kwanciyar barci akwai mala'ikan dake bin kafofin gashinsa jiki yana kwance a karkashi da duk ka motsa ya roka maka gafarar Allah, abu na biyu ki kiyaye salar kiyamul lail, ki rinka raya dare da ibada sabida mafi yawanci jahilai masu sihiri cikin duhun dare suke aikata surkullensu, to su can suna shirmensu ke kuma kina bautar Ubangijinki. Na lura ke mai yawan addua ce, to idan zaki roki Allah ki rinka masa fadanci kina masa kirari da tsarkakakkun sunayensu mafi soyuwa a garesa, wadanda idan aka kirayesa dasu zai amsa, idan aka nemi jin kansa dasu zai yi jin Kan, idan aka nemi yayewar tsanani zai yaye.. Ki tabbatar da kafin ki fara kowcce adduar kin fara gabatar da shimfida, watau istigfari da salatin Manzon Tsira, idan kin kare kuma ki sake rufewa da salatin. Idan zaki yi addua ki rinka girmama rokon, ki daukesa da muhimmanci, ki rinka na ci, sannan ki dunkule bukatarki ki roki Allah Kai tsaye, ki yawaita tuba da yin adduat tare da sauran jama'ar musulmi Kar kiyi ta rokon ke kadai. Babban muhimmin abu game da addua shine tawali'u da rage aikata sabo da tarar lokuttan da aka yi nuni ana amsar addu'ar. Misali idan cikin dare ne tsakiya da karshensa don ance a wannan lokacin ne Ubangiji ke tashi da kansa yana Kiran Ina me neman biyan bukata in biya masa.. Kinga Wanda duk ya dace da wannan lokaci yayi kyakkyawar sa'a.. Akwai farkon asubah da karshenta, sai lokacin da mutum ya fuskanci abokin gaba wajen yaki, lokacin saukar ruwan sama, bayan kiran sallah da tsakanin kiran sallar da tada ikama, ko ki fuskanci alkibla ki rokesa, amma inda Ubangiji yafi amsar addua shine yayin da bawa ya kaskantar da kai cikin sujada ya roki Mai dukan zai amsa. Saboda haka yanzun ma ki tashi mu gabatar da sallar nafilar da ma'aurata keyi mu nuna godiyarmu ga Ubangijinmu da ya kaddaremu yin wannan aure, mu rokesa ya tabbatar mana da dukkan alkhairinsa ya kade mana kiwanne irin sharri. Ta mike tsaye ta saka hijab dinta suka natsu, ya shiga gaba ta bi bayansa suka gabatar da nafilar, bayan sun idar ya juya gareta ya dafa kanta ya sake rokan Ubangijinsa alkhairinta da neman tsari daga sharrinta, daga nan ya umurceta da suka karanta suratul Ikhlas kafa 3 ko11 suyi taswili zuwa kabarin Rabiu, iyayensu da dukkan musulmi da suka rigamu gidan gaskiya. Duk hakurinta ta kasa danne zuciyarta tunanin Rabi'u da mahaifiyarta da bata taba sani ba a rayuwarta. Kuka take Mai tsuma zuciyar Mai saurare, hankalinsa yai dubu ya baci, ya fara rarrashinta "Rahima kiyi hakuri Allah ya gafarta musu, meye na zubda hawaye bayan munyi musu addua shi suke matukar bukata daga garemu" Hawaye ya rinka kwaranya daga idanunta, ya mike tsaye cikin damuwa ya kamata suka shiga toilet "Ki Yi hakuri ki daina kukan nan haka, wanke fuskarki." Ya umurceta. Tayi abinda yace, suka dawo dakin, ya zaunar da ita a bakin gadon ta zuba tagumi, ya fita dakin, zuwa can ya dawo dauke da babban tray dauke da warmer da plates da kwalin mango juice dana fresh milk da cups ya dire a gabanta yace "Kinga ni yunwa nike ji tun rabuwarmu ban ci komi ba, sauko mu ci abincin." Bata musa ba saboda itama yunwar take ji, cikinta kamar an washe mata tas! Ta bude warmer din, gasashshen nama ne irin Wanda ba'a bari ruwan jikinsa ya kafe dinnan, sai kamshin kayan yaji, ga tumatur da albasa an yanka kanana, miyaunta ya tsinke tun kafin ta saka yanka daya baki,, ai tana taunawa Saida ta lumshe ido saboda dadin naman, Maggi da gishi sun kama radam... Kallon reaction dinta yake yana murmushin nan nasa, sai da yaga ta sake taunawa ta hadiye yace "Yaya, yayi dadi?" Ta gyada Kai "Don Allah a ina aka samo ne?" Ya girgiza Kai "Sai mun cinye za kiji." Ta zage taci naman nan har ta fi shi, ya zuba mata madarar ta shanye tayi gyatsa tayu hamdallah harda sude hannu. Suna karewa ta yunkura zata kwashe kayan, ya dakatar da ita da "No yau aikina ne, bari in Kai in dawo in baki labarin inda na samo naman." Ya fita ta bi bayansa da kallo tayi zugum. 'Anya wannan rawar jikin da Ya Haseeb keyi yau baids wata manufa can karkashin zuciyarsa kuwa? Ah to ta gane mana, cin nama banza ne da dare balle ga ango da amarya?" Ba'a jima ba aka dauke wutar lantarki sakamakon kakkarfar iskar data taso hade da saukar ruwa mai karfin gaske hade da tsawa mai firgitarwa, ga walkiya na gilmowa har ta cikin window dakinta.. Rahima ta tsorata ba shiri ta haye bisa gado ta kudundune kanta cikin pillow tana salati. Dakta ya dawo dauke da wata 'yar torchlight a hannu yana haskawa, yana shigowa ya maida kofa ya rufe, ya Kara tabbatar da duk windows ma rufe suke sai yan ragar da iska ke shigowa tunda ba kura, yace "Yanzun Malam Hassan zai kunna gen gidan yayi duhu ko?" Ba amsa, ya haska ya ganta a kudundune, ya karisa yace "Rahima mene kuma ke damunki yanzun?" Bata dago ba ta amsa "Wallahi Allah ya hakicce ni da tsoron tsawa sa wal .. bata karisa ba, aka buga wata tsawar ratsa--tsa-tsa...walkiyar ta gilmo cikin dakin, ta saki pillow ta cakumeshi ta rike gam tana makyarkyata... Dariya ta kama shi "Ni ban taba ganin matsoraciya irinki ba, maimakon ki rinka karanto adduoi sai ki rinka boye fuska?" Ta Kara cusa kanta a kirjinsa tace "Me zan karanta?" "Ya kwantar da ita tukunna ya fara rada mata "Cewa za kiyi *tsarki ya tabbata ga Allah Wanda tsawa take tsarkake shi da yabonsa da mala'iku don jin tsoronsa* A hankali ta rinka maimaitawa har taji tsoron ya gushe, to sai Kuma me? Sai fahimtar halinda take ciki, gaba daya jikinsu manne suke, kunya ta rufeta, ta nemi juyawa ya rada mata *Kin San hukuncin matar data juyawa miji baya ko* Bakinta ya mutu, magana ta gagara sabida yanayin data tsinci kanta ciki, jikinta yayi likis, kasala ta rufeta, tunda ya gane ta bada kai bori ya hau, daman ya riga ya hau tudu, gangara kawai yake nema, sun hade su n manne da juna, sun shiga rudani, gaba daya ji sukai tamkar basu taba wani rayuwar aure da kowa ba sai yanzun. Suna cikin yanayin ana ci gaba da zabga ruwan sama, tuni Rahima ta manta tsoron tsawa da walkiya, shi kuwa addua yake yana kara godewa Allah daya nufesa da auren daya daga cikin matan da ake Kira *SA'IDA* Lokacin da ruwan ya tsagaita barci ya rinka fisgarta ta rinka mashalo ita ba barci Mai nauyi na ita ba a farke ba yayinda ya rinka kallonta cike da so da kauna maras misaltuwa. Cikin dan barcin daya sure ta tayi mafarkin tana tsaye bisa wani tsauni tareda Haseeb da Rabi,'u, zuciyarta ta cika da murna da farin cikin ganinsa, ta matsa da hanzari domin ta kamo shi amma tana isa kusa yaja da baya, ta sake bin sa, ya tsaya ya riko hannunta ya matsa kusa da Haseeb shima ya rike hannunsa ya hada da nata ya manne yace "nagode daka rike amanar dana baka, ka rike matarka da kyau...ya juya gareta yace 'Ke Kuma ki bi mijinki zaku kasance cikin amintattun masoya da suka samu ingancin aure.. Mamaki ya hanata magana sai kokarin riko shi take yana ja baya har ya bace daga nan wani mashahurin haske ya lullubesu ita da Haseeb .. Ta farka babu inda jikinta bai kyarma saboda gigita, tunda ya rasu bata yi mafarkinsa ba sai yau, ta rumtse ido ta karanto *Allahumma innee a'uzu bika min sharri maa ra'ayta fee manaamee wala yadhuru nee fee deeni wa dunyayaa* Nan take yasa hannayensa ya rungumota in a warm hug, cikin matukar kulawa yake son jin me ya tsorata ta, ta fada masa mafarkin da tayi, yayi shiru tukunna yaja numfashi ya saki kana yace "Ki daure ki sanyawa zuciyarki salama kan marigayi, nima Dan uwanane Rahima, amma ba zan so ace duk lokacin da muke tare zaki rinka kawo batunsa ba." Taf! A takaice yai misunderstanding dinta kenan, to a ganinsa da gangar take yi ko me yake nufi? Nan take ta cika, ta zare jikinta ta zuro kafafunta zata sauka daga kan gadon ya dago "Ina zaki?" Ta ci gaba da daure igiyar night dress dinta "I just want to be alone." Ta mayar. "Okay zo amshi key don na rufe kofar." Ta juyo da niyyar amsa, ya janyota ta fada jikinsa ya riketa gam ya lakace hancinta "A takaice ba kiji wa'azi ba kenan, don ke ba juya bayan ma za kiyi ba, guduwa za kiyi, Rahima baki da kirki. Ni bada wata manufa nayi miki nasiha ba, kiyi tunanin idan da bani Kika aura ba wane namiji ne zai yarda kuna tare kina maganar tsohon mijinki ko a mace ko a raye.?" Ta langabar da Kai "Ya kayi min muguwar fassara baka fahimceni bane in dai Kuma ba kishi ne ba." Ta karisa tana boye fuskarta. "Hhmmm kunyarki ai na karyane in har zaki iya min Zuciya daga na fada miki gaskiya, in Kuma kishin ne Ni ya dace ma inyi fushin dake Rahima amma sai kika bugeni kika hana min kuka." Ta saki sa sanyar ajiyar zuciya "Kayi hakuri danu Yaya ba zan sake bata maka rai ba, but you should understand me Nima tun farko kace min auren nan dole a gareka to ya za kayi expecting barin tunani bayan nasan banda wani matsayi a zuciyarka data wuce "yar amana?" Yayi shiruu! Lalle baki shi kan yanka wuya, yasan abinda zai fadi amma bai San illar da furucin zai haifar ba. Rahima ta iya ramuwar gayya, shi tun ranar daya Fadi kalmar ma ta manta bai yi tunanin kalmar *dole* zata ja masa problem ba, gashi magana zaran bunu ce data riga ta fito ba a maidata ciki.Ya muskuta yace "Yes na tuna na furta hakan but wallahi is a mistake, i was under pressure at the time ba hakane cikin zuciyata ba, kinsan duk muutum ajizi ne ki yafe min." Tace "Matsayin nawa kawai nike son sani saboda ina cikin duhu." Ya kada Kai " Wannan akwai ki da kure amma ba komi gidan kika taras tunda na lura halayyar mu daya." Tayi murmushi "Wace ni da irin halin manya?" "Hhmmm tsokanace ma abin? To tashi muyi wanka asubah ta karato tunda kin hanamu barci." Kinji namiji wai nice na hana masa barci, ta Fadi a zucci.. Bata yi aune ba taji an sureta an yi cikin toilet da ita, ya direta cikin bath, yai tsaye yace "to bismillah ki inyi miki ne?" Ta rufe ido "No nagode." "Dube ta da anyi magana kice kunya alhalin baki da dama." Bayan ya dawo masallaci ya zauna suka yi karatun quranin tare suka yi azkhar dinsu suka shafa adduoinsu.. Ya rinka mata wani irin kallo yana nazarinta, ya tabbatar wannan lallasausar jikin nata mai kama da jikin mage yai mata tsami ko'ina... Ta dago taga yanayin kallon da yake mata, suka hada ido tayi saurin saurin sauke nata kasa, ita dai wani bala'in nauyinsa take ji. Hhmmm har ga Allah ta gwammace yayi magana komin kankantarta da yin shurun nasa da Allah kadai yasan abinda wannan kwakwalwar tasa mai kamar computer take kirfa masa. Ta sake satar kallonsa har zuwa lokacin ita yake kallon, ya nutsar da idanunsa alamun cikin zurfin tunani yake, da yaga shi take kallon itama yai mata signal, idanunsa sun koma tamkar na mai jin barci, nata sukayi luuu ... Da za a tona zuciyar kowanen su tsantsan so da kaunar junansu ne suka mamaye ko'ina amma sun kasa furtawa juna, hhmmm zuciya na so baki yaki fada kenan inji Aunty Hadiza Bungudu. Da baki zai daure ya taimaki zuciya ta amayo cutar data addabeta da sun sami saukin kuna da tafarfasar da take musu a daidai lokacin. Amma tunda dukkansu kowa naji da kansa sai a rinka kallon-kallo a jira har zuciyoyin su cika su tumbatsa.... Tare suka sauke sansanyar ajiyar zuciya, kasancewarsa namiji yai ta maza ya danne tukukin hayakin soyayyar da ya nemi fitowa waje ya koma kirjinsa ya cika yaci gaba da radadi, ya Kira "Rahima?" Ta dago ido da kyar domin ita kadai tasan abinda take ji, jiransa kawai take ya furta wani Abu yaji sirrin zuciyarta amma tunda bai shirya ba ta dake, ko ba komi a matsayinta na mace ta rike martaba da darajarta har sai ranar da ya gaji ya bara. Ta kanne tace "Ka kirani kuma kayi shiru.. Ya sake yin shiru sannan yace "Kin San anjima zan koma gidan Zuwaira ko?" Bata yi tsammanin kalmar da zai fadi ba kenan, da taji ba warning kishi ya taso ya lullubeta ta shiga jan innalillahi wa Inna ilaihirrajiun domin kishi masifa ce, sannan ta amsa "Yes na san ka"idar ai." Ya kura mata ido don ya lakanci wani abu yace "Ni fa dadi na dake kenan iya zance.". "To me nace daban?" Ya naji a bar zancen, batun asibiti ki bari Saida azahar ki tafi sabida ki kwanta ki sami hutu, batun breakfast ma ba zan ci komi ba for now." Ta kallesa "Wai don me?" "You ve filled my apetite, na Kuma gode Allah ya saka miki yai miki albarka." Ta juya baya don kunyar jin kalamansa, yai murmushi, Nima kwanciyar zanje inyi amma in my bedroom muddin Ina son ki huta din." 16/09/2020, 23:42 - Anty saliha: ...RAHIMA..doc by jami 40 Bata farka ba saida akayi kiran sallar azahar cike da mamaki, rabonta da samun lafiyayyen barci haka ta manta. Saida ta gama kimtsawa tsaf ta nufo kicin wajen Uwale, bayan sun gaisa take tambayarta Yaya ya tafi asibiti ne ban ganshi ba." Uwale tace "Ya jima da fita ai Hajiya, shine ya ban umurnin Kar na sake na tasheki sai kin farka don kanki." "Ikon Allah ta Fadi, to ya batun abincin su Hjy Fatima?" Uwale tace "Tuni an gama aikin sabida tun jiya Alhaji yace in kwana da shirin hada musu abincin Karin kumallo, to har na ranar ma na gama an kai tun dazun, wannan zaman ma da kika ga nayi jiran fitowarki nike in damka miki sakonki in tabbatar da kin ci.".. Rahima ta kalleta "Ban gane ba, anyi yamma da kare,meye na wani tilastani cin abinci gaskiya ban jin yunwa." "Ai kuwa zaki daure kici ko dan kadan ne, na dau alkawarin tabbatar da hakan." "Abincin baida suna ne wai?" Inji Rahima cikin curiousity. Uwale ta duka ta duka ta bude oven ta fiddo sauran naman da suka ci tareda Dakta daten jiya ta aje mata a gaba, kana ta dauko warmer dauke da soyayyen dankali da plantain ta hada mata, ga flask cike da ruwan shayi, ta koma ta jingine." Ta dago "Wadannan abincin duk zan zubawa cikina? Tirkashi, to miko plate in zuba miki naman.". Ta wani zaro ido ta daki kirji tace "Wa Ni? Don Allah rufan asiri Hajajju wace ni da cin abincin da Alhaji yayyi da hannunsa?" Rahima ta zaro ido "Da gaske?" Ta gyada Kai "Wallahi shi ya gasa naman nan jiya, don ma Kar in ga abin banbarakwai tafiya yayi can sashensa sai kamshi naji kawai yana tashi, da ya fito yai min kashedin Kar in fara in fada miki, na kame bakina... Rahima ta jinjina, wane irin mutum ne shi wannan Ya Haseeb? Bata taba ganin namiji kamarsa ya wani tube ya shiga kicin ba talkless of ace ya bata lokacinsa dafa abinci especially idan yanada mukami ko kudi, Ya Haseeb ya nuna mata yana da difference da wasu mazan, shin sai yaushe zata fahimci hatsabinin mijinta? Sai bayan azahar direba ya sauketa a asibitin, bata ga motar sa so bai cikin office dinsa kenan, ta wuce ward din su Hjy Fatima, suna ganinta suka yi mata caa suna tsokanarta ya gajiya? Tace "Ta me Kuma?" Falmata tayi dariya "Kunji fa wai mu zaki maida kifin rijiya, alhalin Dakta da kanshi yace ayi hakuri za kiyi lattin zuwa saboda kina hutawa, to in ba hutun gajiya ba na menene?" Hjy. Fatima ta riko hannunta tace "Kyale Falmata kinji, na lura ita da Maryam basu da wani zance sai irin wannan." Rahima tayi murmushi "Ai su experts ne." Sun ci gaba da hirar gida Maiduguri, Rahima na sha'awar culture dinsu sosai, taji yadda suke hada turaruka na jiki dana tufafi na daki na tsugunno, daga karshe dai sunce ta bari a sallamesu Daktan ya amince suje ta gano garin Tasha mamaki... Suna idar da sallar la"ar ta dauko wayarta ta Kira Aunty Zuwaira. Bugun farko ta daga wayar,tana jin Rahima ce ta buga tsuki zata kashe. . Tace "Don Allah karki kashe just na kira in miki sannu da jiki ne." A can bangaren Zuwaira ta amsa "Kin dai Kira kiji ko muna tareda Dakta, to gani nan bisa cinyarsa." Tana jin haka ta aje wayar tayi zugum cikin zurfin tunani. Suka lura da yadda ranta ya baci, suka tambayeta dalili ta fada musu, Falmata tace "Kina wasa da kissar mata kenan kin yarda da hasashenta? Hjy Fatima tace "Da alamu ai, wallahi idan baki tsaida hankali da tunaninki ba zata rinka kulla miki makirci tana hadaki da mijinki a banza." Rahima tace "Gaskiyarki, hhmmm ni da har kuri Nike yiwa Maryam cewan zan iya zama da kowacce kishiya." "Ko yanzun ma karki canza ra'ayinki, ki tsaya Kan akidarki duk rumtsi, ki rabu da ita tayi irin nata." Tace "Insha Allah, sai dai fa kishin nan dana fara ji shi zai wahalsheni, ko mijina na farko nan taba jin matsiyacin kishinsa haka ba.". "So ke haifar da kishi kanwata, Don da kike yiwa Dakta yafi wanda Kika yiwa dan uwansa so dole kishinsa ya rinka bijiro miki amma Kar ki bari kishin ya raunana yarda da amincin da kuke yiwa juna ke dashi balle ya samu daman ruguje ingantaccen ginin tubalin soyayyar juna da kuka aza." Rahima tace Insha Allahu zanyi yaki da shaidan don Allah kadai yasan kudurina Kan Aunty Zuwaira." Suka ce to Allah ya cika miki burunki na alkhairi." 17/09/2020, 16:21 - Anty saliha: ...RAHIMA..doc by jami 41 Sai karfe biyar ta bar asibiti ta koma gida ta fara Shirin abincin dare, ba a dade ba Daktan ya dawo ya zarce falonsa, ta bishi can ta gaishe shi. Ya dago daga latsar wayar dake yace "Kiyi hakuri tunda na fita ban kiraki , Ina tareda wasu friends dina ne." Tayi dan murmushi "You dont have to explain yourself to me, ba komi. Tayi shiru zuwa can ta kallesa "Uwale ta bani sakonka na ci nagode, but don Allah karka shagwabani, ni ya dace in rinka shiga ina yi maka ." Yayi dariya a takaice "Anya! Zamu shirya da Uwale kenan, ita da nace sirrine." "Hhmmm! Kana ta ja min aji Ya Haseeb, I am puzzled.. Yace "Ba dai kin yaba ba?" Ta gyada kai "Sosai kuwa, just yadda aka yi hakan nike son ji." Yace "Karki damu kanki kan wai na shiga kicin, na saba tun Ina karami, Hajiya ce sila, kasancewa na namiji bai hana ta koya min hidimomin cikin gida ba, musamman aikin kicin, to ni kadai ta mallaka,ina tausayinta sosai, kaunar da nike mata yasa bana iya zama inga tana kai kawo ita kadai ban taimaketa ba, no, Ina kwadayin zama da nagari, abin alfahari gareta, don haka komin kankantarsa lokacin dana samu bana karatu muna tare a kicin, tare muke girki, na iya gyaran gado, wanke-wanke dasu shara tunda ni nike mata, ta nuna min cewa ba mace kadai take da hakkin kula da cikin gida ba, akwai lalurar rashin lafiya, wata macen ma ko ka aureta bata iya girkin ba, kinga a nan ba sai mutum yaita bacin rai ko yawon zuwa sayen abinci ba. Ta nuna min hanyoyin dogaro da kaina, na amfana sosai Rahima. Gani da kyan-kyani in kin lura sam bana iya cin abincin sayarwa, a jami'a ma da kaina nike girka abincihar friends dina suka ce da catering na karanta, to ba wannan ne burina ba, sha'awa ce kawai da yanzun na zama Hotel manager. Yanzun haka akwai friends dina da suke managing manyan hotels din kasar nan. Tunda nike ban taba cin abincin da yai min dadi Kuma na gamsu ba kamar na Hajiya ba, to sai naki wanda na ci hankalina kwance cikin jin dadi, shine nace bari a ramawa kura aniyarta." Ta jinjina "Lalle Allah ya sakawa Hajiya da alkhairi, ya kara maka jin kai da tausayinta, kaima yasa ka samu masu yi maka biyayyar." Ya bita da kallo cikin jin dadi, shi dai a ko yaushe yana jin dadin adduoin da take masa, ya sakar mata murmushinsa mai kashe mata jiki yace "Thanks so much my dear Allah ya saka miki da alkhairi." Ji tay kamar an zare mata lakka, ita har fargaban irin kallon nan nasa take saboda ya fara takan zama tamkar wata *zombie* ce. amma tasan maganin abin, ta daga Kai ta kalli agogo tace "Naga shidda saura kwata ba yanzun zaka wuce gidan Aunty ba?" Ya Kara nutsewa cikin kujera "Korata kike?" Ta girgiza Kai "Wai Kar a shiga hakkinta." "Naji zan tafi but ban tashi tafiyar ba." Tace "Allsh ya baka hakuri, ya batun Abdul, ina son inje in dauko shi." Ya gyada Kai "Yes nima nayi tunanin a dauko shi ya dawo nan ya natsu wuri daya, a rinka kaishi Yakasai din during weekends." "Idan kayi min izni in tafi in dauko shi anjima." Ya bata rai "Sai dai direba ya kaiki bana son kiyi driving da dare, ku tafi da Uwale ta gaida Hajiya da Mairo daga can ku shiga asibiti." "Tayi shiru "To laifin me Kuma tayi yake ta wani magana fada-fada, hhmmm miskili kafi mahaukaci ban haushi, yanzun zai saki fuska, anjima ya daure tamkar bai taba yin dariya ba. "Amshi wadannan." Ta dago taga yana mika mata wata 'yar jaka. Ta sauka daga kan kujerar ta durkusa tasa hannu biyu ta amsa "Nagode." Ya kalli rolex dinsa ya mike "Ni zan tafu Kar a sake korata.". Tayi murmushin karfin hali "Haka dai kake gani, bari in dauko sakon su Khalifa." Ta ruga ta dauko wata jakar leda ta mika masa, Ina gaida yaran da Auntyn da jiki.". "Sai na kira." Ya fadi a takaice "Karka damu kanka Yaya in don Ni, mu kwana lafiya." Ya tsaya kawai yana kallonts, shi a ganinsa ma alla-alla take ya bar mata gidan tana korarsa don rashin damuwa da al'amarinsa, bai san daurewa take ba, na ciki na ciki." Har ya saka kafa daya a kofa zai fita ya fasa ya juyo gareta "Zo amshi nayi mantuwa.".. Ta tako ta iso gabansa, ji kawai tayi ya rungumeta yai mata kyakkyawar kiss da numfashinsu ya balaguro na dakikoki kafin ya saketa, ya fita ya barta a tsaye. Ta girgiza kai da yai mata dum ta taka a hankali ta koma kujera ta zauna tayi jum har saida ta daina ganin jiri-jirin da bugawar zuciyarta ta haddasa mata, hankalinta ya dawo jikinta, cikin natsuwa ta dauki gift din da ya bata ta fara ciro wasu kananan cards da wani sansanyar daddadan kamshi ke fitowa daga garesu, ta ajiyesu gefe, ta dauki wani gift din da aka yi wrapping ta bude tacu karo da wani karamin box mai kyaun gaske na glass, to ba dan akwatin ba abinda ke cikine ya burgeta, cike yake da ruwa taf, kasansa kananan kifaye ne da mami wota a tsakiyar ruwan, ta kurawa gift dinshi ido cikin tambayar why zai bata kyautar Nan, meya hadata da *Mermaid* Kuma?, Ga Kuma wani key holder da aka yiwa design na wasu kifaye biyun manne da juna jikinsu nata walkiyar ruwan ruwan azurfa, daga jikinsu aka rubuta sunanta wanda sai an kura ido za a gani. Ta ajiye wadannan bisa cinyarta ta dauki cards din ta bude tana karantasu daya bayan daya, kalaman da aka tsaro cikin na karshen yafi daukar hankalinta, ta sake karantaea a fili *I enjoyed your company so much, that I will like to enjoy it again, I never knew that you could give so much fun... I used to think that you're always shy* Kamshin turaren *Impression* ya cika mata hanci, jatta hannayenta kamshin turaren Ya Haseeb suke, ta mike ta adana cards din kana ta yiwa dan box dinta na fishes mazauni kan bedside drawer dinta. 17/09/2020, 16:22 - Anty saliha: ...ˆRAHIMA..doc by jami 42 Yana shiga gidan da sallamarsa ta doka tsaki ba amsawa ba sannu da zuwa balle yaji sanyi a kokon ransa. Bai kula ba Kai tsaye ya wuce sashensa ya gama abinda zaiyi ya sake fitowa, yaransa na zaune a falo suka rugo ya rungumesu "Dama kuna cikin gidan Nan?" Abdul ya nuna uwar "Mummy ce ta hanamu fitowa." Yace "Ba komi, baku tambayi Dan uwanku Abdul ba " Nan da nan suka ce "Ka taho mana dashi ne Baba?" Ya girgiza Kai "Ah ah amma ga sakonku inji Aunty Rahima." Har suna rige-rigen karba, suka zazzage kayan kwalam din da ta ciko musu leda dashi suka baje kowanne ya dauki abinda yake so ya fara ci, Zuwa ta mike ta fisge na hannun kowanne ta zubar tasa kafa ta tattake sauran tana tsiya " Aikin banza da wofi, ni za a nunawa yarana iya hila, Kai ka gaya mata 'ya'yanka basu cin irin wannan da za a kwaso tarkacen banza kayan zawo a kawo musu?" Yaran suka fashe da kuka, ta bisu zata bubbugesu ya kamasu ya rungume, bai ce da ita komi ba sai rarrashinsu yake "Me kuke son ci yanzun?" Khalifa yace *Ice cream?* Yace "Okay ku zo mu tafi a sawo. Tana ganin sun fita ta biyo bayansa "Ni ban yarda wani ice cream za a sayowa ba, can din dai zaka koma.". Tankawa yabawa, ya saka yaransa a mota yaja suka sake fita gidan. Tana ganin haka ta ruga cikin gida ta dau waya ta dannawa aminiyarta Husaina kira, tana dauka ta fara "Ke ni fa nayi yadda kika ce banga alamar zai canza ba, wallahi ko a jikinsa bai kulani ba, ya mai sheni wata mahaukaciya." Husaina tace "Tunda hakan bai tasiri ba, ba zamu ciwo kansa ta hanyar tsiya ba kenan, yanzun ki kwantar da hankalinki itama ki nemi shiryawa da ita Amma ba farad daya ba don karta dago manufarmu, data saki jikinta dake sai mu far mata." Zuwaira tace "Nima naga hakan zai fi gaskiya don a kyaleka kayi ta haushi kai kadai kamar wata karya da takaici sosai." "Ai ke Zuwaira na rasa abinda yasa kika lakewa namiji kwara daya tal yana wulakanta ki sai kace shine autan maza, yana sonki zai miki kishiya kuma ma matar kaninsa?" "Hhmmm zaki gane bane Husaina, sai wata zuciya tace in rabu dashi wata ta rinka kwadaita min irin dacen da nayi dana sami miji irinsa, ke wallahi Dakta fa gwarzon namiji ne, duk macen data dandani zumarsa ba zata iya rabuwa dashi ba ( kunji sakarcin banza, ahir dinku mata wajen tona sirrin aurenku. Tuni ya dace Zuwaira ta fahimci manufar kawarta a kan mijinta ko don yadda ta kan rinka kyaun likitan ko yabon halinsa da sauransu, sakarcinta ya hana, to gashi tana Kara kwadaita mata shi, Allah ya ganar da ita) my To gashi dai ta bata shawara kamar kullum ko zata dauka oho. Kafin Daktan ya dawo da yaranta tayi wanka ta kalelaita jiki ko'ina ta zauna jiransa... Yana tuki yana dan waigen yaran nasa guda biyu da Allah ya bashi, duk sunyi barci, tausayinsu ya kamashi, su dai kam ba suyi dacen uwa ba, gaba daya ya sabo su ya shigo cikin gidan ta wuce dasu dakin barcinsu ya shimfide, ya tofa musu adduoi ya rufi musu kofa ya wuce bedroom dinsa yai kwance ya rufe ido yana nazarin al'amurran rayuwarsa da irin destiny dake playing role hanya daban-daban. Ya kalli agogo, karfe sha daya saura na dare, tasan zaiyi wuya ace Rahima tayi barci by now don macece mai son raya dare da ibada, son jin muryarta ya tsananta a garesa ya kasa daurewa, nan take ya zaro wayarsa ya kirata. Tana dagawa ya fara tambayarta "Ya kin taho da Abdul din?" Tace "Eh ya biyoni da kyar may be don bai ganka bane, Ni na rasa dalilin da yasa bai son zama a wajena." "Karki damu kanki kinsan Dorayumi is a new place a gareshi, zai saba a hankali, be patient with him.' Daga nan duk sukayi shiru, ba abinda ke bakanta masa rai da ita irin miskillancin ta, ko shi kadai take yiwa hakan? At least he has done his best ta bangarensa wajen kokarin sakin mata fuska ya aje nasa miskillancin but taking ta warware, me take son yai mata Kuma? Wani dogon tsaki ya fito daga bakinsa, Mata ko!! Idan mutum ya biye musu sai hallakar dashi wallahi, but shi din ya riga ya amincewa zuciyarsa yana son matarsa, son da ya kebe a wani bangaren na zuciyarsa, may be idan taji hakan ta dan rangwanta masa... Zuwaira ta sallama ta shigo,bai daga ido ya kalleta ba har ta zauna, ta dauki 'yan mintoci ba tace komin ba itama, shi Kuma yaci gaba da maganarsa "Mu kwana lafiya, I will call you again." Ya ajiye wayar ya juyo kan Zuwaira yace "Kinga idan ba maganar arziki ta kawoki ba don Allah ki sarara min ga hanya ki fita ki ban wuri kaina ya dau zafi already." Ta sadda kanta kasa "Zuwa nayi in baka hakuri, don Allah da Annabinsa ka yafe min." Yace "Idan nayi hakurin na yau, sai kuma na yaushe, anjima, gobe ko jibi? Kuma ma hakurin me kike bani, mun riga mun saba, zaman auren kawai muke tamkar wasu jahilai." Ta muskutta "Ni dai nace ka yafe min ba don halina ba." "Me Kika yi da kike neman yafiyata, Ni a was Nike a rayuwarki don ban san matsayin da kika ajeni ba." Ta dago cikin hanzari "Ya zaka ce haka, matsayin mijina mana." Yace "To su Kuma abokan da kike dasu na waje matsayin me suke a gareki?" Ta fara kuka" Ni fa wallahi tallahi ban taba tarayya da kowanne namiji ba, wadanda muke huldar business dinmu kadai ne muke communicating dasu." "Ni ban tambayeki kuka ba, to su din kuma muharramanki ne? Zuwaira ki ji tsoron Allah, ki sani komin dadewarki a duniya Zaki tafi lahira, Allah zai tuhumeki abubuwan da kika aikata a duniya. To wai tsaya ma tun farkon aurenmu nasan ke din mace harija, duk kokarin sauke hakkinki ki kan nuna ke ba a gamsar dake ba, tun a nan na fara tausayinki, bayan wannan ke din nan fa ban aureki cikakkiyar mace ba, for whatever reason hakan ya kasance gareki ban sani ba, that's why ganin yadda kike huladarki da abokan naki yasa ni zargin. A wancan lokacin mutuncin dake tsakanina da mahaifinki yasa na share, na danne zuciyata har addua na rinka yi kar Allah yasa in rinka ganin bakinki ko rashin martabarki, ba don haka ba da tuni mutuncinki ya gama zubewa a idona, ke kinsan *virginity* darajar diya mace ce amma na ci gaba da zama dake da halayenki na rashin da'a amma kawaicina da hakuri bai sa kin gyara ba, sai kika kara shiga harkar kawaye masu zugaki kina shiririta, kina zaton ba don su Khalifa sunyi kama dani ba Zan karbesu ne a matsayin 'ya'yana? Nace idan ma halink ne yau da gobe bata bar komi ba ai. Daga nan saboda daurewa yawon gindi kika je kika daure mahaifa wai ke karki haihu ki tsufa da wuri, kika kara samun lasisin yawon. Kullum cikin nasiha nike a gareki amma ko a jikinki, Zuwaira ban rageki da komi ba, ba rashin abinci ba sutura, ba rashin kudin kashewa, iyayenki na kokarinsu a kanki to ashe duk ba muyi miki gwaninta ba, kince kina son ki nemi na kanki na mara miki baya don nima ban son tauye hakkinki, kuma no matter how much muke baki, is good ki nemi na kanki din saboda halin yau da gobe, but sai kika zake in the process, ke kinsan wanene ni, ni ba mazinaci ba ne, Allah ya kaddaro min auren Rahima kin kasa kwantar da hankalinki sai shirme da hauka kike wadanda ba zasu hanani komi ba balle su sani illa ma ki Kara zubda mutuncinki a idona. But ki sani kin kaini makura, saura kiris in dau matakin da zai baki mamaki." Tayi kasake tana saurarensa, to me ya fadi Wanda ba gaskiya ba? Babu, tayi tsumi ta muzanta, to ai shi daman komi kake aikatawa Allah na ganinka da lokacin da zai kama ka a hannu... Amma Allah ya sani da zuciya daya ta auri mijinta don tana matukar son abinta, amma ba a a nan gizo ke sakar ba, tun kafin ta auri Haseeb kawarta a boarding school ta fara bata ta in the process of lesbianism, ta saba a haka har suka gama school, sai kuma wani tsinannan saurayinta ya nemeta ba tare da sanin kowa ba, har iyayenta, tun kafin taga Haseeb. A gaskiya tafi danganta lalacewarta da wadannan mutum biyun da suka taka rawa wajen gurbacewar tarbiyyarta duk ta taso da shagwabar nata, iyayenta sunyi kokarin gyara tarbiyyarta ta fandare ita ala dole yar gata, kuma yan uwanta kaf ba haka suke ba.. Ta kalli mijinta da wutsiyar ido taga latsar wayarsa kawai tunda ya gama mata magana, in banda sharrin shaidan wace mace ce zata sami miji irinsa tayi mishi rikon sakainar kashi? Wallahi ko personality dinsa kadai ya ishi mace jin sha'awarsa balle a Kai ga kyawawan halayensa, ba domin shawarwarin da Husaina ke bata ba da tuni ta daina abubuwan da take yi ta rungumi mijinta, to amma ko yanzun lokaci bai kure ba, but Kashi! Inda zata sami cikas dayane, wannan auren da dauko. Sai dai kuwa ta kadata tayi gaba ta bar mata mijinta idan kuma taking fita za taga sharri kala-kala, ba zuwa wajen boka balle Malam, Zuwaira bata bin malamai duk iya shegenta, wannan sai Husaina. Tasa hanni ta shafi lallausar suman kansa "Kayi barci ne?" Ya wani dago kamar wace ta cije shi, "Menene Kuma?" "Na rokeka gafara ne banji kace ka yafe min ba ." Na yafe miki Zuwaira Allah ya yafe mana gaba daya amma ki roki gafarar Ubanginki kan zunuban da kika dauka da niyyar ba zaki sake aikata kwatankwacin su ba, idan kuwa kinsan ba zaki bari ba, no need ma kiyi istigfarin don Allah ba abokin wasan kowa bane, ai kin gane?" Tace "Wallahi har ga Allah ba zan sake ba, don Allah ka tayani addu'a. Yace "Kullum cikinta muke, muma ajizai ne Allah ya yafe mana dukkan kurakurenmu." Tace "Ameen.' Ya juya baya domin turaren data fesa hawa kansa yake, karfinsa yai yawa har ji yake kamat zaiyi amai." Ba da son ransa ba ya rinka tuna sansanyar kamshin turaren Rahima Wanda ya kama jikinta radam, turarenta har wani kashe jiki yake...bai gajiya da shakarsa.. Ta matsa kusa dashi ta shafa bayansa ta kira sunansa "Dakta? Ya amsa "Ni kuwa haihuwa nike so." Wata sabuwa inji yan caca! Ba tareda ya waigo ba yace ",To Ni ke bada haihuwar, da can Kuma nina hanaki? Ai kin fini sanin abinyi sai ki hada da addua.". Ta kwantar da kanta a jikinsa ta sassauta murya "Ka taba ganin mace ta haihu ita kadai, yaushe rabon daka kusance Ni?" Haseeb ya dafe Kai! Allah wadaran naka ya lalace, shi bai taba ganin mace maras kunya irin zuwaira ba, duk da ya saba da halinta na rashin iya danne maitarta, yau abin yai masa wani iri, ko don 'yan kwanakin da yayi da Rahima ne, yana son mace mai kunya, yana jin dadin yadda take jin nauyinsa, mace mace mai kunya abin so ce, duk yadda taso da bukata sai an kai ga rarrashinta ta bar mijin da rawar jikin, Kai Allah ya shiryi Zuwaira, abinda akace kunya na daga cikin yankin imani. Da taji ya Kyaleta ta kuma Kara rungumarsa tace "Kasan dai hakkina na kanka ba mai sauke min shi sai kai, kuma zaka rantse da Allah kwanaki ukun da kayi a wancan gidan haka kayi salin alin ba abinda ya wakana tsakaninku sai Ni don na nemi hakkina ka ja min rai?" Cikin deadly voice yace "Nayi warning dinki daga yau idan zaki magana karki sake kawo min batun Rahima.. Ta marairaice ta narke a jikinsa "Afwaan ba zan sake ba. " Ya dago ya kalleta tun daga sama har kasa yaji shi kansa kyamar kansa yake ji but wajibi sauke nauyinta da Allah ya dora a kansa, ya tashi zaune yace "Ji nan please je kiyi wanka, Kuma idan domina kike shafa wannan turaren don Allah ki canza bana so, ki tabbatar da kin teafe kitson attachement din nan, ki yanke wadannan akaifar da kika bari kamar ta masu cikin kare idan ba haka kuwa sai dai mu hakura da juna." Nan da nan ta amince "Wallahi dyk zanyi abinda kake so, amma ban dade da yin wanka ba sai na sake wani yanzun? Ya gyada Kai "Manufata kenan, idan ba zai tuwwu ba okay my kwana lafiya.". Ta zabura ta duro daga Kan gadon ta fada toilet..... Haseeb ya bita da kallo ya mike tsaye ya fuskanci alkibla ya daga hannayensa sama ya fara jero addua "YA Allah kasa yau ya zama mafarin shiriyar wannan baiwar taka saboda kai ka halasta saki amma kana kyamar yinsa, ya Ubangiji kar ka kaddareni aikata abinda idan nayi Al'arshinka zai girgiza, Allah ka karamin hakuri da juriyar zama da ita, ka bani ikon yin adalci tsakanin matana, Ya Allah ka shirya Mana zuriyyarmu idan zaka Kara Mana ka bamu masu albarka shiryayyu salihai masu shiryarwa, ka gafarta mana dimbin zunubanmu, ka yafe Mana baki daya." Ameen. Ya shafa kenan ta fito ta ganshi a tsaye, ta dauka ita yake jira, da sauri ta isa garesa ta kwantar da kanta bisa kirjinsa, yasa hannu ya rungumeta, ko adduar da yayi ne yasa zuciyarsa ta rage radadin tsanarta? 18/09/2020, 00:18 - Anty saliha: ...RAHIMA..doc by jami 43 Kiran sallar farko ya zame jikinsa ya shiga yai wanka tareda alwala ya fito yai shirin zuwa masallaci, tashim duniya Zuwaira bata motsa ba hakan ya fita ya barta, ya nufi dakin yaransu ya tashesu suka yi akwala ya tafi dasu masallacin.. Har suka isar suka dawo bata farka ba sai juyi take a gado, yai mata tsaye saida yaga ta sauka ta shiga wankan ya Kyaleta, a gurguje ta gabatar da sallar ta koma gado taci gaba da barcinta, ya kalleta yace "Allah ya shiryeki." Bai tsaya jiran wata Mai aiki ba da kansa ya hadawa su Khalifa breakfast suka ci tare dashi, ya shiryasu ya kuma kaisu makarantar ya ajiye ya dawo gidan bai sake bi ta kanta ba ya koma falo yai zamansa. Ya dauki 'yar redio ya kunna, but sauraren kowanne programme ya gagara saboda daidai lokacin tunanin Rahima ya kutso masa, al'amurranta suka rinka masa yawo cikin kwakwalwa, ya saki wani dan murmushi, kasa daurewa yayi ya zaro wayar ya danna mata kira. Ta rufe Qur'aninta kenan Kiran ya shigo ta daga ta sallama ta gaisheshi har da dan rusunawa kamar tana ganinsa. "Ya kwanan su Aunty da Yara?" Ta tambaya . "Lafiya kalau Ina Abdul?" "An kaishi school." Ta amsa a takaice ta kuma yi shiru.. Hhmmm bai san dalilin da yasa da yaji muryarta yake daburcewa ya kasa furta kalaman da ya shirya zai fada mata ba, and she's not helping matters sai tayi shiru ta barsa yana kame- kame. A nata bangaren kwarjinsa ke haddasa masa increased na heart beat wanda hakan ke sa ta kasa magana. Yaji shirun zaiyi yawa ya gyara murya yace "Jiya bamu gama zancen mu ba." "Wane zance kenan?" "Zan tuna miki on one condition, kin yarda zaki bani abinda nike so?" Ta gyada Kai "In dai bai fi karfina ba insha Allah." "To baki ce komi ba, Kinga kifayen?" Ta sake amsawa da "Na gani sunyi kyau nagode sosai but still Ina cikin duhu, rashin fahimtar ma'anarsu." "Zan miki bayani idan na shigo anjima kadan." "Ina ce a asibiti zamu hadu kawai.". Takaici ya kamashi, Lalle yarinyar nan bata kaunarsa, dubi yadda ya kwanta ya tashi da tunaninta a rai amma ji irin reaction dinta da ya kirata." Yace "Okay mu hadu a can din ba problem." Sai karfe hudun bayan la'asar ya kirata suna cikin hira dasu Hjy Fatima." Kamshinta kawai ya isar masa da sakon ta shigo office din nasa, ya juyo yana kallonta, taku daya ana biyu yaja ya tsaya a gabanta, yai niyyar embracing dinta, ko me ya tuna ya fasa, daidai lokacin aka kira wayarsa ta office, ya juya ya dauka ya fara magana. Tsawon mintoci Yana ta magana daga harshen turanci ya koma larabci, *Hal anta bi khair?* Ya tambaya ashe patient dinsa ne daga Riyadh yaji sauki ya murmure, Daktan ya ci gaba da magana taga zasu dauki lokaci, ta fita ta basu wuri, tana fita ta shiga ta yiwa su Hjy Fatima sallama ta koma gida. A ranar kuwa Zuwaira ta kasa gane kansa, yayi zamansa a falo shida Yara har suka yi barci ya maishesu ciki ya dawo falon yaci gaba da latsar wayarsa.. Ba wani abu ke cinsa ba illa tunanin Rahima, zuciyarsa kamar ta fashe , wannan wane irin bala'ine? Ya dace ya shareta dalilin abinda tayi masa tayi tafiyarta ta barsa but ya kasa daurewa why? Ya yanke shawarar tura masa sako but muddin ta gani bata yi responding ba bayan ya tona mata sirrin zuciyarsa zai kyaleta sai ta ne me sa don kanta. Nan take ya rubuta mata *Lokacin da zaki karanta sms dinnan, ki tabbatar tunaninki ne ya addabeni, may be in kasance cikin murmishin da na kanyi duk lokacin da tunaninki ya bijiro min cikin kowanne yanayi a ko'ina nike ko me nike yi Kuma. Bayan kin karanta warannan kalaman, ina fatar zaki fahimci matsayinki a gareni a yanzun da anjima, da har muddin rayuwa even if it's for a blink of an eye. Kiyi murmushi domina yayinda kike ci gaba da hidimominki don zan kasance cikin tunaninki.* Zuciyarta ta cika fak da murna da farin ciki duk da bai furta ainihin kalaman da take son ji ba wadannan ma kadai sun isa Mai hankali ya gane *So da Kauna * aka dunkule waje daya. Fahimtar inda ya dosa yasa ta maida masa martani kamar haka: *Daga awoyin da muka rabu ina fatar ka sakani cikin ruhi da zuciyarka ya kasance ko rufe idanu kayi Ni kake gani cikin tsananin tunaninka da irin wannan ci da zuccin saboda nayi matukar maraicinka, ban ki a ce a yanzun Ina tare dakai cikin raina, zuciya da ruhi ba.* Ya rasa me zai ce da ita don dadi, hakika Rahima ta fahimci manufarsa fiye da zatonsa, ashe daman m shi take jira ya bara kafin ta tona nata sirrin zuciyar, me wayon tsiya ya Fadi a fili yana murmushin farin ciki.. Ba bata lokaci ta sake aika mata *Hakika nayi maraicinki kamar in janyo sauran time din da zamu kasance tare, ashe kewar masoyi ukuba ne.*. Ta maida masa reply *Tawa kewar ta zarce taka Ya Haseeb.* *Karki damu zamu magance su duka, sai ince sai mun hadu.*. Ta rubuta Waiting for you with pleasure. 18/09/2020, 15:48 - Anty saliha:...RAHIMA..doc by jami 44 Ranar d zai koma gidanta Rahima ta kasa zaune ta kasa tsaye ta kara tsabtacce ko'ina cikin gidan ya ci gyara tamkar ranar aka kawo ta, komi yayi fes, ta bangaren abinci ta shirya masa light food ta dafa masa mai suna "Muhammas' abincin larabawa ne yana yanayi da cous-cous, hade da farfesun kaji, a gefe ga dambun kifi, banda drinks na kwali, ta hada masa lemon tatacciyar abarba da gwanda kana ta saka kwalbar favorite drink dinsa 'Blue fruit cikin fridge yai madaidaicin sanyi. Kwanaki biyun da yayi gidan Zuwaira sun bata damar canza tsarin bedroom dinsa ta kawata dakin barcinta da nasa da furanni masu kyau, daga gefen window ma ta aje wasu tukunyar live flower dake fitar da natural kamshi saboda iska da hasken rana dake taimaka musu. Sabon duvet ta baza a saman gadonsa,banda soft blanket din dake gefe koda ana bukatar lullube jiki idan sanyi yai taso, ta feshe gadon da turare Mai suna *seduction* kana ta feshe dakin gaba daya da Natural fresh air (pot pouri), ta kunna Air condition sannan ta koma ga suturar sa da ya saka ya cire kafin barinsa gidan, alreday an wanke su tas an goge, jerasu kawai tayi cikon wardrobe dinsa, da kanta wanke inner wears dinsa ta goge ta feshesu da turare suma ta jera komi a mazauninsa. A gurguje ta leka asibiti ta basu Hjy Fatima hakurin ba zasu ganta da yamma ba ranar, ta koma gida ta ci gaba da hidimarta tsabtacce jikinta, al'adarta ce duk karshen wata bayan ta Kara period ta kanyi shaving pubic hair dinta da na armpit saboda koyi da addininmu da inganta tsabta, to yau ma hakan tayi. Uwale ta rangada mata zanen shuku suka zuba har dokin wuyanta saboda gwargwado tanada yalwar suma ta kame da ribbon,tanada son kumshi sosai, shima Uwalen ta taimaka ta d'afa mata celotape da aka yiwa designs masu kyaun gaske kafa da tafin hannu sannan aka bi da natural lalen da aka kwabashi hade da turarensa tun safe don yai saurin kamawa, a takaice ranar take amaryar zan-zan, ta zama taba ka lashe. Bayan ta ba Abdul abinci yaci ya koshi, sunyi sallah tare tunda baban nasa bai iso balle suje masallaci, hakan take yi duk ranar da yaron bai samu zuwa masallacin ba sai tasa ya rinka binta suyi sallar tare yana gani da koyon yadda ake gabatarwa. Suna idarwa tayi mishi wanka ta saka masa 'yar pyjamas sa ta yara sannan ta shiga tayi wanka ta fito ta kimtsa kanta, moderate kwalliya tayi da wata atampar Holland da aka dinka mata simple gown wanda tayi mata das tayi kyau da kirar jikin nan nata, tayi cas! Ba a batun kamshi a tattare da ita don ita ma'abuciyarsa ce, ya riga ya kama jikinta radam. 'Yar muryar Abdul dake wasa a falo taji yana fadin "Abba oyo-yo." Ta fito daga bedroom dauke da murmushinsa "Barka da isowa." Ta fadi cikin ladabi. Ya mika mata hannun damarsa "Assalamu Alaiki wa rahmatullah wa Barakatuhu." Cikin jin kunya ta mika masa nata hannun kana ta amsa sallamarsa, ya dan matse hannun kadan kana yace "Malamai sun mana koyi da yin hakan bayan yada sallama, yana kara shakuwa tsakanin ma'aurata. So ya gidan?" Ta maida masa sallamar sannan tace "GIda kowa da komi lafiya, ya aka barsu Khalifa?" "They are Okay alhamdulillah." Ya amsa yana wasa da Abdul dake ta zuba surutu.. Sun jima da gama cin abincin amma bai daina santin farfesun kaji da dambun kifin na, ta rinka tsokanarsa tana dariya. Tsaye ta iskoshi cikin bedroom dinsa bayan ta kimtsa falon, ta taka a hankali zuwa bayansa ta kwantar da kanta tace "Menene naji kayi shiru?" Ya juyo ya riko hannayenta yana kallonta, ya girgiza kansa "Kin canza min komi na rayuwata, me zance?" Ta saki ajiyar zuciya "Bana bukatar fitowar wata kalma daga bakinka muddin na faranta ranka, zuciyata cike take da farin ciki." Ya sake girgiza kai "Ba zaki gane bane Rahima, but a bar maganar for now come here... Da kalaman da yayi fada mata, but as long as tana kusa dashi yana kallon yadda tayi kyau ta tsaru tamkar wata 'yar tsana ba zai samu natsuwar wasu surutai ba, ya kama hannunta guda ya rinka kallon desing din lalen da yai ram a tafin hannunta, ya kai hannun bakinsa yai sakar mata kiss, ta lumshe idanunta, bata ankara ba taji ta bisa shimfidarsu, kamshin turaren seduction, da kamshin turaren Haseeb mai suna *Privacy* suka hade da wanda ta shafa *Eternity* suka cakude gaba daya, ya rungumeta tsan-tsan tamkar wani yace zai kwace mishi ita. Kamar a majigi suka rinka iyo cikin kogin so da kaunar juna, sai rada mata yake *Uhibbiki Kaseeran* cikin kunnenta, ta bude idonta da kyar " Me hakan ke nufi? Cikin shauki ya fassara *It means I love you so very much* Rahima, so da kaunarki sun shige min cikin jinina kamar yadda kwayoyin cutar nan da basu da magani kan shiga cikin jinin mutum." "To ni kuma in ce me Ya Haseeb? Saboda yadda nike jinka na rasa yadda zan kwatanta soyayyarka cikin zuciyata sai godiyar Allah nike dare da rana domin kullum adduata ya bani mijn da zan so ya so ni da zuciya daya ashe kaine amsar addu'ar. Nan kishi ya motsa yace "kina nufin baki taba son wani ba harda marigayi?" Ta danyi shiru tukunna kafin ta amsa "Na so Rabiu, irin son 'yanuwa ko kuma ince irin miji da matan da suka tsinci kansu a wannan matsayi kaddara Allah ta gitta amma ban taba jin irin wannan tafasar kunar zuciyar ba sai haduwata da Kai." Ya kara rungumeta "Iam sorry dana bude miki old wound, na kasa daurewa ne.". "Na fahimceki Yaya and iam glad da kayi tambayar coz a karo na farko bayan rasuwarsa nayi maganarsa ba tare da zubda hawaye ba sai deep sad feelings, ko ba komi Uban dana ne, shi ya fara nuna min so da kauna har in mutu ba zan manta dashi ba." Ya nisa "Yes hakane, karki manta nima danuwana ne da muka shaku kwarai, akwai wata irin kauna tsakaninmu da Allah ya dasa Mana, I really missed him, kuma wallahi ban taba tunanin zan auri matar da ya aura ba, but da Allah ya shiryo mana hakan kullum adduata garesa yasa ya huta, Allah ya sanyaya masa, Ina rokon Allah yasa zaki haifa min wani Rabiun bada jimawa ba." Tace "Idan ma ba a samu ba ga Abdul Nan.". "No Abdul -Haseeb dana ne da yaci sunana, yanzun Rabi'u nike so yaci sunan babansa.". Tace "To Allah ya amince ya tabbatar mana da khairan." Saida gari ya waye Rahima tayi maganar kifaye yace "Ya dace ki fahimci dalilin da yasa na baki kyautar kifayen nan Rahima." Tace "Hhmmm ni ban fahimci komi ba Kai dai za kayi min bayani Dakta." "To naji, ya jikin kifi nan tarwada yake?" Cikin rashin fahimtar inda tambayar ta dosa ta amsa "Tarwada ita kullum jikinta tsantsi da damshi ne ko tana cikin ruwa ko akasin hakan." Yace "Yauwa, ya jawota ya zaunar da ita bisa cinyarsa kafin yaci gaba da bayin "To Kinga kamar yadda halittar jikin kifi tarwada take haka Allah ya halicce ki kema exactly, kullum cikin ni'ima, duk namijin da Allah ya nufa da auren irinku to shi fa baida sauran burin wata 'ya mace a duniya, kune irin matan da ake Kira "Sa'ida', ba ruwanku da shaye-shayen magunguna da wasu matan keyi, ko kinsha ko baki sha komi ba mijinki zai matukar gamsu... Kinji reason dina na bada wannan kyauta, kuma daga yau duk gift din da zan baki wajibi ya danganci ruwa.. don nima kina ni'imtani, kin fahimceni, yanzun sai batun kyauta ta." Maganganunsa sun sa kunyarsa ta dawo mata sabuwa ta rufe idanunta, ya banbare da kyar. Cikin shagaba tace "Don Allah ka rabu dani.". Yace "Ai kuwa baki isa ba, alkawari ki kai min wajibi ki cika sa." Tace "To me kake so?" Ya amsa "Sai kin kalleni zan fada miki." Tana kallonsa yace *Yourself* Hhhmmm wai don Allah da gaske ne da mutane ke cewa yawancin Doctors maza basa jin kunyar fadar magana? Saboda ita ga nata likitan nan Yana ta rikita mata kwanya da surutan da ko a mafarki bata yi zaton zai iya Fadi ba. Dr Haseeb da Rahima sun ci gaba da gudanar da rayuwar aurensu gwanin sha'awa, aka bar masu fadin ya za ayi wa ya auri matar kaninsa baki ya mutu sai sha'awar su suke. Sati biyu cif Dakta ya tabbatar da warkewar patient dinsa Hjy Fatima don haka ya rubuta musu sallama. Da kansa ya daukesu zuwa gidansa suka kwana guda sannan suka koma Maiduguri. Ba su tafi ba Saida suka tabbatar zumunci Mai karfi ya kullu tsakaninsu tareda da alkawarin ziyarar su day zaran ya samu sarari inji likitan, sun rabu suna begen junan Hutun da Rahima ta dauka ya kare sai batun komawa aiki, Daktan ya daka tsalle waje guda yace ba zata sabu ba Wai bindiga a ruwa, yadda ta shagwaba shi yana bukatar attention dinta sosai amma yace ta nemi sana'ar da zata yi don bai son ta zauna hannu sake tana jiran kullum sai anyi Mata. Ta nemi shawarar iyayenta suka amince, ita da 'yaruwarta Maryam suka hada jari suka aikawa Hjy Fatima ta fara turo musu turarukan wuta, na jiki, dana tufafi, har dasu lapayya. A sannu Ubangiji yasa musu albarka, kasuwanci ya habaka ya karbu wajen matan manya sai hamdala. Kwatsam Zuwaira ta tada fitinar sai dai a hade su gida daya saboda kullum cikin zargin mijinsu na mata rashin adalci take, kuma wai ma Rahimar bin malamai take a nata tunanin ba haka kawai miji ke rawar jiki da ita ba. 18/09/2020, 19:13 - Anty saliha: ...RAHIMA..doc by jami 45 Tun daga Kan Hjy Kaltume, Maryam da Iyayenta babu wanda ya bata goyon bayan ta amince da bukatar Zuwaira ba balle shi kansa uban gayyar da yace duk abinda zata ce taje ta dade bata ba amma bai yarda tsarin ba sam. Rahima tace a bata kwana bakwai tayi istikhara ta roki Allah zabi tukunna. Sarai yasan halin gimbiyar tasa don haka yace Kar ma ta san ran zai canza ra'ayinsa ya riga ya yanke shawara. Ba Rahima bata amince da shawarwarin da aka bata bane, no bata san abinda gaba zata haifar ba, zaman nasu khairi ne ko sharri Allah kadai yasan gaibu, dalilinta kenan na dagewa tayi adduar saboda zuciyarta ta kasa tsayuwa waje guda. Bayan satin taji ta natsu ta amince da batun hadasu din sai dai ta dage da adduar neman tsari daga dukkan sharri da fitinar dare da rana. Tana tunkarar maigidan da maganar yai tsalle yace ba zai taba hadasu ba, ta kafe kan ra'ayinta ya kafe kan nasa taron taurin kai. Ranar tana zaune taji sallamar su Umma da Hjy Kaltume Daktan na biye dasu ta girgiza Kai ta tabbatar shi ya dauko su kan batun nan da yaki ci yaki cinyewa. Bayan ta gaishesu ta kawo musu abin motsa baki, bata bari sun fara magana ta tambayesu "Yaya karata ya kai ko?" Hajiya Kaltume ta gyada kai "Har yanzun kaina a daure yake Rahima, na rasa dalilin da yasa kike son dauko fitina da hannunki ki kawi cikin gidanki, me ye zafi haka? Ta sunkuyar da kai "Hajiya baku fahimce nu bane shiyasa kuke tunanin hakan." "Ina fa zamu fahimceki tunda ba muyi wayo da hankalinki ba." Ummanta ta fadi a fusace. Ta kalleta a raunane "Afwaan Umma haka nike nufi ba." Hajiya ta kalli Umma "Saurara mata tayi Mana bayani watakila ta fi mu gaskiya.". Sai a nan Haseeb ya tanka yace "In dai itace yanzun zata kashe miki jiki da lafuzanta ki amince da manufarta ko banza ba Kya ganin laifinta." Rahima ta kallesa "Shikenan Yaya bari in musu bayani idan basu amince ba wallahi na hakura, amma kafin nan ka fadu hujjojinka na rashin son hadamu din." Ya gyara zama "Hujjoji?, Halayyen Zuwaira ai ba boye suke ba, kuna nesa da juna ma ban tsira da korafinta na Ina rashin adalci tsakaninku ba, fitinar yau daban ta gobe daban Wanda da ina biye mata da tuni mun rabu." Rahima tace " Kuna jinsa ko? To ai ni abinda ban son ya faru kenan, da can din ai da halinta baka rabu da ita ba sai bayan aurena? Ko Ni ce zanyi zargin dalilin wata ka rabu dani, daga nan Kuma kulalliyar gaba ta kullu tsakanina da yaranka har abada saboda mai zurfin tunani ne zai gane cewan gajiya kayi da halinta ka Kai makura ne silar rabuwarku, batun danne hakkinta da take yi ma zaman mu a tare zai sa ta gani idan ana zaluntarta din, Kai kuma za a rage maka yawan zirga-zirga tunda iyakinka na natse waje daya hankalinka zai fi kwanciya." Umma ta daka mata harara "Ai ba dai iya magana ba 'yar ka iya, shi ba wadannan matsalolin suka dame sa ba." Yace "Ta fa san duk abinda nike gudu Umma." Hajiya tace "Rahima zaki iya zama da Zuwaira da halayyenta?" Ta gyara zama tace "Sai maganar halayye muke Hajiya amma bamu tsaya munyi nazarin shin wane irin hali Aunty Zuwaira ke dashi ba kamar yadda masu ilmin sanin halayyan dan Adam suka kasa halayyen mutum har kashi uku. Na farko akwai halayyen da basu gyaruwa kwata-kwata, misali irin halayyen da mutum ya gada daga iyaye ko aka haifesa dasu, to kowa yasan halayen Aunty Zuwaira ba gado ba ne don kowa ya shaidi martabatar iyayenta da sauran zuriyyarsu, ba kuma wadanda aka haifeta dasu bane. Na biyu shine halayyen mutum da ake iya gyarawa Amma sai an Sha wahala sosai wajen yin gyaran, irin wadannan halayyen mutum kan tsiri yinsu ne a kan da dole ma'ana wani dalili ya tilasta wajen adopting canza original halinda aka san mutum dashi. Misali irin yanzun da yawancin maza kan bar wa mace takakihun hidimar gida, yau da gobe darajar sa na iya zubewa a idonta, ta daina ganin girmansa sabanin yadda take mutuntashi da can. Na uku mutum Kan dauki halayyan da ba nasa ba da rana tsaka ko dalilin hulda da abokan banza, ko haka kawai ya halin wani ya rinka burgesa, irin wadannan gyara kawai suke bukata ba kuma za a wahala wajen gyarawan ba. Ya kada kai yace "To munji mai falsafa cikin wadannan kashin da kika zano da wanne kika danganta Zuwaira dashi har kike shaawar zamanku tare? Kenan kina ganin zaki iya gyara halayyenta? Rahima ta nisa "Sanin gaibu sai Lillahi, Ina adduar sanadiyyar zaman tare ta canza halayen nata." Hjy Kaltume tace "Da kyau Rahima haka ake son musulmin kwarai ya sowa kansa abinda yake so wa kansa, kin burgeni." Umma tace "Hakane Hajiya nima banki naki ba, tashin hankaline nike gudu." Rahima tayi murmushi "Kamar kin manta da halin diyar taki Umma, fitina ta kan kare ne Kan Wanda ya jawota, Ni dai goyon bayanku nike bukata sannan ku tayamu addua." Hjy Kaltume tace "Shikenan Allah yai miki albarka ya cika burunki na alkhairi. Daktan ya wani kalleta yace "Naji duk kun goyi bayanta ne, to ni kam ina nan kan bakana, idan Kuma kun matsa na amince to Kar ayi kuka dani idan wani abu ya taso nan gaba " Mahaifiyarsa tace "Wannan ne baka isa ba, ka tara 'ya'yan mutane kace ba ruwanka.". Rahima tace "Rabu dashi Hajiya naji sharadinsa na dauka Allah ya kama mana." Ya sake kallonta a fusace yace "Yanzun sai ki fadi inda kuke son ku zauna tsakanin Dorayi da Galadancin." Ta girgiza Kai "Ba ni da wannan matsayin, Kai da Aunty Zuwaira kuyi deciding Ni 'yar amshin shata ce.". Ya juya gasu Hajiya "Kunji amsar ta ko?" Hajiya ta gyada Kai "Laifi kake son Dora mata dai amma gaskiya ta fada, tabbas zabi na gareku, ta ba Zuwaira girmanta da Kai kanka." Da yaga ba zai samu goyon bayan da ya zata ba dai ya amince cike da fargaba. Yayi deciding kara gyara gidan da Rahima take saboda akwai filin da za a dora wani ginin sosai. Ba bata lokaci aka fara aikin sake tsara gidan Daktan don zaman iyalinsa. 19/09/2020, 13:57 - Anty saliha: ...ˆRAHIMA..doc by jami 46 An kammala komi na gidan Dakta har gashi Uwargida Zuwaira da tawagarta sun rakata tarewa a nata bangaren. Yanuwanta da suka san mutunci sun shiga sun gaisa da Rahima aka taba barkwanci suka musu addua suka tafi, kawayenta kuwa sai shirmen da suka saba, hatta da falon Zuwaira Saida suka leko yanayin tsarin da Rahima ta yiwa nata suka dawo suka kwatanta irinsa, suna yo suna yar da maganganu don dai neman jidali. Bata kula ba balle tasan Allah yai ruwan tsironsu, to Rahima a banza take miskila? A wannan ranar Zuwairar ke da maigidan yadda ta shirya saboda Wai ta nunawa Rahimar ita ke da gida da maigidan ma gaba daya, to wace take yi dominta bata san arziki na bori ba. To idan ba shiririta da neman zubar da aji irin na Zuwaira ba, kowaccensu sashen daban, sai ma kaso sanin halinda yaruwa ke ciki ne zaka leka inda take, sai kuwa idan sun hadu a general parlour na gidan, kowacce tana da masu aikinta to me ye na hana Kai sukuni? Dawowar su Zuwaira yasa yaranta suka Kara shakuwa sa Rahima saboda tana jansu sosai a jikinta, ta hanyar kulawa da duk bukatocinsu ba gajiyawa, ga kokarin tarbiyyarsu da take yi tareda danta, to jama'a ko yaro yasan mai son shi. Zuwaira bata kaunar kusancin yaranta da Rahima ko miskala zarratin, da taga tayi kokarin rabasu ya faskara sai ta shaidawa abokiyar shawarar nata. Husaina ta buga kirji tace "Zauna ki saki baki galala kamar wata sauna bayan ta mallake miki mijin ta hada da 'ya'yanki kina zaune sokoko ta mallake zuciyar yaranki tas, an fada miki da bakin hura wuta wannan yarinyar ke zaune a gidan Nan?" "Da alamun kamshin gaskiya a batunki Husaina, nima zargina kenan don wallahi ko kaffara ba zanyi ba, ba haka kawai Dakta ke rawar jiki da ita ba, ke baki ga yadda take juyashi ba fa, Daktan da bana ganin tsadadden murmushinsa sai na sha ruwan dala amma ko waya yake da ita haka zaki ga yana wani rausayar da Kai Yana zuba murmushi sai kace wani sick lover boy." Husaina ta kyalkyace da dariya tace "To ai ba murmushinsa kadai ba shi kanshi tsadadden ne Zuwaira, yanzun dai meye shawara?" "Kinji kuma, ke din dai nike saurare." Husaina tace "Ya zanyi dake yanzun,kince ke ba zaki shiga malamai ba, to ki zauna ta saki a tafin hannunta ta murza ta juya son ranta, mu dai idan da malamai da bokaye a duniya mun gi karfin tsara balle irin wancan da aka dauko miki, ke Kika yi sake tun farko amma ai ba ajinki ba ce." Zuwaira taja dogon numfashi "Ai yanzun dole mu san matakin dauka that's why na neme ki." "Karki samu damuwa 'yaruwa, kin yarda ko wane irin taimako na kawo miki zaki yi amfani dashi ko?" "Me zai hana kuwa Husaina shakkun me kike?" Husaina tace "Ai dole in jinjina kar kisa in kashe kudina a banza alhalin kin san samun su da wuya." Zuwaira tasha mur tace "Ke fa problem dinki kenan in dai batun kudi ya taso alhalin ni Ina kashe miki kowacce irin lalura ba tareda jin kyashin komi ba, ke kuwa in dai za ki yi min Abu sai kiji tamkar naman jikinki zaki diba." Nan take Husaina 'yar bariki ta share wannan batun cikin dabara tunda tasan gaskiya aminiyarta ta fadi tace "Wasa fa nike miki, amma da gaske kinsaj business din mu yaja baya Kuma mijina ba irin naki bane da yake sakar miki dala kina fantamawa yadda ranki ke so, nasa Dan banzan makon tsiya, hannun nan nasa a dunkule tamkar na "yan dambe." Zuwaira ta tuntsire da dariya "Oh sharri ma za kiyi masa Kuma? Ai kuwa Yana kokarinsa shima.".. Ta tabe baki. "Me Kika sani game da mugun halinsa, ke ni fa auren ma na gaji har na nemi ya sauwaka min, in gutsire igiyar auren in yi gaba in sami Wanda ya dace dani." Ta zaro idanu "Ke Husaina ki rufaea kanki asiri, Ina ke Ina wani rabuwa da mijinki yanzun, wa zai wani aureki yanzun bayan ga 'yan matan Nan ma suna yawo a titi a mashinshini?" Ta gyada Kai "Ai da kika ganni da agenda ta, na riga na shirya komi jiran lokaci nike in gabatar miki.." "Toh! Al"amarin ba sauki kenan to Allah ya nuna mana alkhairi." Tace Amin "Bari inyi azama Kar Malam ya fita sai kin ganni." Tsakanin matan Daktan biyu zama yaki dadi,ta kowanne bangare Zuwaira bata da dama. Matsalar farko da Rahims ta fara karo da ita daga uwargidan nata itace gasa, Zuwaira irin matan nan masu shegen gasa, duk abinda taga Rahimar tayi sai ta kwaikwaya, ko silifas ta lura Rahima ta canza itama saita saya, balle a kaiga su kayan jiki ko na gyaran gida. Wasan wasa rashin mafadi, gasa idan ba na nuna bajinta wajen bautar Allah bane ya zama shirme. A ka dawo Kan abinci, a kullum mai aikin Zuwaira na yaeon gulma sa sunan tana zuwa wajen Uwale ne amma su sun San yar leken asirin uwardakinta ne, duk abinda yazo taga ana girkawa a sashen Rahima zata nade taje ta fesawa uwardakinta musamman idan Daktan wajensu yake, ita Kuma ranar nata girkin saita wanke tukunya ta kwaiwayi irin Wanda su Rahimar suka yi ta sake dafawa. Sai ayi rashi dace, Wanda akayi dominshi ba zai ci ba, Zuwaira ta fara bala'in hatta abincin ta ya daina ci sai na Rahima. Tunanin bai kawo mata dalilin rashin cin bai rasa nasaba bai dade da cin irin nau'in abincin ba kazaliza method da aka hada ma ba guda ba. Rahima ta gaji ta yanke shawarar aikawa Zuwaira ko me ta dafa. Uwale ta kalleta galala tace "Ni fa kina bani mamaki, yaushe ne Zaki yarda da kishiya har dai wace bata kaunarki har da batun Kai Mata abinci? Kin san ba zata ci na saidai ayta asara kawai. Rahima tace "Uwale kenan Ni ban dauki Aunty Zuwaira kishiya ba, abinci kuwa ko taci ko Kar taci na sauke nauyin da Allah ya dora min matsayinta na makwabciyata." Ta rike haba "Makwabciya kuma Hajiya, ina makwabciyarki itace Hjy Shafa'atu mai shigowa wajenki din nan?" Rahima tace "Makwabta sun kasu kashi uku ne Uwale, akwai mai daraja ta daya, ana nufin musulmi danuwa da kuke da danganta da juna Makwabci Mai daraja ta biyu shine wadanda baku hada komi amma Allah ya hadaku zama unguwa daya, ka zo , na zo kamar ita Hjy Shafa da kike batu.. Mai daraja ta uku shine makwabcinka da ba musulmi ba. To Kinga zan iya Kiran Aunty Zuwaira makwabciyata Mai m daraja ta daya kasancewarta musulma, ga Zumuncin dake tsakanin yaranmu, ga shi muna auren miji daya, muna zaune karkashin mutum guda, ko da a ce ga dakina ga nata ne sunan mu Makwabta Uwale. Tunda hakan ne wajibi a garemu mu kyautatawa juna don gudun fushin Ubangiji mu Kuma tsira daga cikin mutanen da Allah ba zai karbu tuban su ba matukar sun mutu basu gaggawar gyarawa ba, shin kin san cewan an ce daidai da abinci mai kyau makwabci ya dafa ya ba makwabcinsa Kar ya cinye shi kadai?" Uwale ta gyara zama "Oh gaske naga baki damu da wulakancin da take miki ba kullum idan kin shiga gaisheta, har a zuciyata nace ko dai tsoronta kike ne? Kuma ga wannan kwaikwayon naki da take yi kullum.. "Abu Mai kyau mutum keyi har wani ya gani ya yaba ai, inda taga mummunar abu nikeyi ai ba zata yi ba komin gasar ta kuwa. Bayan haka sanin nauyin da Allah ya dora mana a Kan juna yasa nike share wulakancinta, inyi biris da shirmen ta sabida nasan abinda nike kwadayi, itama rashin sanin ko biris da sanin yasa tayi sakaci shaidan yai rinjaye a kanta amma Ina adduar Allah ya ganar da ita, muma ya Kara mana fahimtar. 19/09/2020, 18:21 - Anty saliha: ..ˆRAHIMA..doc by jami 47 Uwale tayi ajiyar zuciya "Ameen Hajiya, gaskiya zama da mai ilmi babban nasara ce a rayuwa saboda karuwar da mutum zai yi, yanzun gashi na karu da sanin abubuwan da tunda nazo duniya ban sani ba, dole in kara himma a makarantar islamiyyar da na shig, amma Hajiya taimaka ki fada min su wanene Allah ba zai amshi tubansu ba idan suka rasu suna aikata sabon da suke yi basu bari ba?" "Uwale nima ilmin nawa cikin cokali ne, amma yanada kyau komin kankantar ilmin mutum ya sanar da wadanda basu sanin ba suma su amfana sai Allah ya baki lada ya kuma kara bude miki kwakwalwar ki kara ilmantuwa don kiji dadin yadawa jama'ar musulmi. Wadannan mutane bakwai da malamai suka yi mana bayani sune na daya shine Mai bata hakkin makwabtaka, na biyu masu yin luwadi, na uku wadanda suke matse al'aurarsu har sai maniyi ya fito musu, na hudu masu saduwa da dabbobi, na biyar namijin dake saduwa da matarsa ta duburarta, na shidda Wanda ya hada diya da uwa yana saduwa dasu, (irin bala'in da yai yawa yanzun cikin al'umma, uba ya rinka neman diyat da ya haifa) na bakwai mai yin zina da matar makwabcinsa." Uwale ta jinjina "Ashe aiki na gaban rago bai zo ba balle ya wuce, wallahi duk ilahirin jikina ya mutu likis, Lalle muna da sauran aiki jawur, in hakane kuwa Allah kadai yasan ladan da kike kwasa kin barmu baki sake sai dai mu take ciki da abinci mu koshi, kwanya ta toshe da miyar kuka da ruwan goro." Rahima ta kyalkyace da dariya "In don wannan karki samu damuwa tunda muna da likitan kwakwalwa, ya bude ya kwashe miyar." Ta kwalo ido "Rufan asiri Hajiya na koya a hankali." Ta mike "Naga idan na biye miki ba zani gidan Shafa'atun da nayi niyya ba, bari in hanzarta kafin maigidan ya dawo yace ya fasa barin fitar." "To a dawo lafiya Hajjaju." Ta saka hijab dinta har kasa ta nufi sashen Zuwaira tukunna, ta tsaya ta rinka sallama shiru Kuma tasan tana ciki tunda ga motar ta nan. Al'adar ta kenan da duk zata fita zata shaidawa Makwabciya, kazalika idan ta dawo don gudun faruwan wani abu ga Kuma sauke hakkin zama tare, ta juya ta tafi abinta. Ko awa guda bata yi ba ta dawo gida saboda sam Daktan bai so ya dawo gida bata nan duk runtsi, tana matukar gudun zuciyarsa. Bata yi fushi ba data dawo gida ma ta sake shiga wajen Zuwairan shima tayi sallamar shiru har ta juya taji an bude kofar falon, ta dawo ta tsaya "Sannu da Aunty, daman fita zanyi na leko mu gaisa in fada miki but har naje na dawo ma." "Oho ai banji knocking ko sallamar naki ba ina cikin toilet ina wanka." Sai a lokacin Rahima ta bita da kallon yadda ta fito ba riga a jikinta sai towel data ratayo a wuyanta, ta jike gashin kanta sharkaf da ruwa har tana wani girgizashi ruwan na fantsamawa Rahima a fuska. Tace "Ayya tunanina bai kawo hakan ba ai.. "To ya na iya ai nima wankan dole ce ta kamani yanzun, ni wannan hidima na Dakta ta fara isata." Rahima ta wani kalleta ta sakar mata matsiyacin murmushinta tace "Ashe daman ke kika koya masa haka Aunty, da na sani ai da tuni na kawo kararsa wajenki don ni din raguwa ce.". Zuwaira ta zuba mata wata uwar harara tare da tsuki gaba daya ta juya ta rufe kofarta garam, ita kuma ta karisa sashenta tana dariyar wautar Zuwaira, a tunaninta don ta nuna tana tare da miji zai daga mata hankali ko da ace gaskiya ce balle tasan ba hakan bane, ko ce mata akayi jima'i kadai ne jigon rayuwar aure oho. Ba wani dadewa Daktan ya dawo, bayan sun dan taba hira take tambayarsa ko ya leka Hajiyarsa? Ya amsa "Sai zuwa dare in Sha Allahu." Tace "Dazun dana kirata a waya naji alamar bata jin dadi ko ta gaya maka?" "No kin san ba zata fadi ba sai dai mutum ya fahimci akwai damuwar." Ta kallesa, fuskar nan a murtuke, maganar da yake yi dai kace tilas sai kawai tayi dif itama, to ta riga ta lakance sa da zaran miskillancin nasa ya taso ko yana cikin bacin rai ta lura mood dinsa ya canza ta kan ja jikinta sai ya nemeta. Shirun da tayi kuma bai masa dadi ba ya kalleta ya kau da kai, ya sake juyowa ya jefo mata tambayar "Rahima me ya faru tsakaninki da Zuwaira take fada min surutun wofi?" Kunji kuma wani daukakkiyar, ba dai mganar da suka yi ne dazun ta zama abin korafi ba.... Da yaji bata tanka ba, ya cire glass dinsa, ta dago ta kasa kallonsa cikin kwarar idanu, ta juyar da Kai gefe yace "Ba ki ce komi ba." Tace "Saboda ban san amsar bane tunda a sanina ba muyi fada ba just magana ce tayi na bata amsa ko ance wani Abu ya faru beside hakan?" "Look Rahima shirmen nan na guda tunda kuka dage zaku zauna tare na amince dole and you know how much I hate the idea amma Kika nace gashi nan yanzun kusan 6 months kuna tare ba zaman lafiya balle a samu piece of mind da kike ikrarin za a samun." "Ni fa har yanzun ban fahimci manufar maganganun ka ba, karata ta kawo ko me?" "No, na dai yi zaton sanin halin Zuwaira da kika yi zai hana biye mata shiriritar ta." Ta danyi murmushi "Idan ranka ya baci afwaan ba za a kara ba. Kamar yadda na fahimci halinta tun ranar dana fara ganinta, na lakanci tana cikin mutane extrovert, wadanda masu sanin halayen Dan Adam suka ce yawancinsu akwai su da shishshigi, karancin basira, wasu su hada da karya da kwadayi, son shigewa gaba kan al'amurra ko wanda bai shafesu ba, su Kan nunawa jama'a sun san komi irin yadda take nuna min, ni Kuma idan naga zata kureni sai in nuna mata ba hakan bane, nan muke samun tangarda. .. Yace Fahimtar banbancin halayenku ita mai yawan surutu ke Kuma introvert nasan ba wani dadin zama za kuji da juna ba." Rahima tace "Ni kuwa sai Ina ganin har ta fara canzawa, cikin dabi'unta marasu kyau na lura sun ragu sosai. Ka dai ci gaba da yi mana addu'a wata rana sai labari l." Ya nisa yace "Gaskiyar Kuma nima na lura da hakan but na kasa accepting cewan zata canza, Allah yasa ta dore." Rahima tace "In Sha Allahu, duk ranar da Allah ya ganar da ita influence din kawayenta ba alkhairi bane zata natsu." 19/09/2020, 22:40 - Anty saliha: ...ˆRAHIMA..doc by jami 48 Dakta yai shiru yana kallon matarsa yana yaba halinta cikin zuciyarsa. Hakika yaga canji wajen Zuwaira, tun yana mamaki har ya daina yaci gaba da sa ido yana lura da dabbin dabi'un data bullo dasu, misali gabatar da sallar asubah ba tareda makara ba shine babban canjin da yai masa dadi a ransa,ta rage yawo kusan rabon da tace zata bukin kawa ko aminiya ya manta, business din ma yayi sanyi ba kamar da ba, yaranta suna samun kulawarta sakamakon ganin irin kaunar da Rahima ke yi musu da yi musu tarbiyyar kwarai, shi kansa yasa mata dokar hana kaisu ko'ina da sunan a barsu can, sai dai a kaisu su gaida kakanninsu da yanuwa direba ya dawo dasu. A gaskiya problems din da yake fuskanta da ita sunyi sauki sosai thanks to beloved Rahima, matsalar data rage yanzun shine yadda Zuwaira ta shafawa idonta toka taki amincewa zuciyarta matsayin Rahima na da can da wanda Allah ya kawota a yanzun, sai dai inda yake jin sanyi Rahima ta daure kowanne cin Kashi da Zuwaira ke mata, inda take Burgesa ma duk iya masifar Uwargidanta ba dai kaji bakinta ba, sai dai na Zuwaira wace takan Kara masa gishiri tace anyi alhalin ba ayin ba. Ta dan bugi hannun kujerar da yake Kai tace "Lafiya kayi shiru haka cikin zurfin tunani?" Ya juyo ya dau glass dinsa ya manna a fuskarsa ya sakar mata lallsusar murmushinsa yace "Just thinking of how lucky iam to have you in my life." Tayi dariyarta mai fitar da kyawawan jerin hakoran ta cikin shagwaba ta "Ya Haseeb kenan, godiya nike sosai." A can cikin dakinta Zuwairan Dakta ta zauna tana cizon yatsarta cikin damuwa domin kissar data shiryawa Rahima kamar kullum bai yi wani tasiri ba. Gaskiya yarinyar akwai dan Karen wayo, duk wani plan data shirya don taga downfall dinta sai dai ya wargaje ko ta wargajesa cikin ruwan sanyi. Gaskiya da sake lale, ba zata zauna ace Rahima ta kwace mata miji ba. To me rage, me yai saura? Matar da babu irin kissa da kisisinar da bata kware a Kai ba, matar data iya hilace miji ta hanyoyi daban-daban? Sai dai ita kanta ta amince Rahima mace ce Mai matukar ladabi da biyayya halayen da kowanne namiji ke so wurin matarsa, to ko wadannan halaye basu isa su mallaka mata mijinta ba? Ga yadda taji labarinta tun aurenta na farko Rahima bata yiwa mijinta musu, duk abinda yace fari ne zata tas kuwa koda kuwa baki ne za tace yafi nono fari. Bayan haka ko taso ko taki Rahima macece mai hakuri mai son zaman lafiya da kowa bata son tashin hankali sam amma bata daukar raini, to ita yanzun ya zata yi? Tas ta gama amfani da magunguna da Husaina ta kawo mata bata ga wani canji ba, Husaina bata da mutunci ga wata gurguwar shawara da take bata wai ta rabu da Haseeb, hhmmm da ne zuciyarta ta rinka gigin yayo mata wannan mummunar tunanin, but ta rabu dashi ta auri wa? Ina zata sami kamarsa? Ita kuma don sakarci ta rinka daukar shawara... Zuwaira ta muskuta a gado taci gaba da tunani, to yanzun data gane kuskuren biyewa Husaina wane mataki ya dace ta dauka don mallake zuciyar mijinta irin Rahimar? Gidan malamai? Ta girgiza kai, no ba ya cikin dabi'a ko tsarinta, tayi saurin kawar da wannan, bata yarda da yawon gidajen bokaye Rahima ta shigewa Haseeb zuciya tayi daram ba, to meye sirrin? Inganta tsabtar jiki da tufafi da muhalli ko kuwa iya sarrafa dadad'an nau'ikan abinci? Kai ah ah wadannan kadai basu isa su mallaka mata zuciyar gwarzon namiji irin mijinta ba. To ko kuwa kamun kai da rike mutuncinta ne silar suka zama silar zama 'yar gaban goshin sa? Shin Ina zata gano sirrin don itama ta kwatanta taga ko zata ci riba tayi nasara mijinta ya rinka kaffa-kaffa da rawar jiki da matar da a da yake nuna ita din dole ce tasa ya aureta? Kafin ta samo amsarta ya dace tasan ita macece , tasan martaba, kima da darajar da Allah yai Mata, to idan ta zubar da mutuncin nata tuntuni fa, yanzun ne take son tattaroshi ta kwaso ta zama equal da Rahima fa duk da hausawa sunce mutunci madsra ba a barinsa a kwashe duka? Nan take hawayen nadama suka fara gangaro mata, tabbas mijinta yai hakurin zama da ita, da wani ne da tuni ya koreta amma ya daure ya riketa duk da yasan illolin dake tattare da masu irin halinta, oh ni Zuwaira Allah ka shiryar dani hanya madaidaiciya ka hana min ci gaba da aikata sabonka,ka yafe min dimbin zunuban dana jibgawa kaina. Babu wani abinyi yi a gareta illa ta roki mijinta gafara kana taci gaba da istigfari, tsayuwar dare da azumin nafila ko Ubangiji zai ji kanta ya yaye mata matsolinta, ciki harda rokon Allah ya mallaka mata zuciyar mijinta, to bangaren Rahima fa? Ya zan dole ta ajiye duk wani kishi da kyashi da hassadarta su zauna lafiya ko ta Kara samun haske daga gareta wadanda zasu gyara mata al'amurranta. An dade da fara Kiran sallar magrib kafin ta dawo hayyacinta tayi hanzarin dauro alwala ta gabatar da sallar kana taci gaba da istigfari har aka Kira isha'i, ta mike ta gabatar ta sallame ta yi adduoinnta ta shafa. Kafin maigidan ya dawo daga masallaci ta shiga wanka ta fito ta canza ado ta fito da kayan abinci, tana harhadawa ya shigo falon tareda su Khalifa harda Abdul, suka zauna suka ci abinci suka kare, bayan sun wanke baki da hannu ta kallesu tace "Kun ga ku tafi sashen Aunty Rahima ku ce Ina gaisheta " Yara suka dubeta galala Kuma basu tashi ba to basu taba ji tace hakan ba,Saida ta maimaita suka mike cikin farin ciki, Khalifa ya kama hannun Abdul yace "Mama mu kwana a can?" Ta gyada Kai"Manufata kenan, oya, ku wuce ku bamu wuri " A guje suka fita sunata murna, shi kuwa yana zaune tamkar baiji diramar da suke yi ba duk da kasancewar yaji dadin furucinta ba zai nuna ba domin gudun ko halin neman maganar ce nata ya taso ko da wata manufar ta aikata hakan. Ta bude baki zata yi masa magana kenan sallamar Husaina y katseta, kafin ayi mata iznin shiga ta shige, masifar kamshin turarenta mai shegen hawa kai ya da doki hancin Daktan, yai saurin mikewa, ita Kuma ta rusuna cike da ladabi na kissa ta gaishe tana wani kashe murya sai kace karuwa, ya amsa a dakale ya nufi sashen sa. 20/09/2020, 12:08 - Anty saliha: ...ˆRAHIMA...doc by jami 49 Husaina ta kalli tace "Ni dai da sa'a nike, duk lokacin dana taho sai in tadda Oga na gida." Takaicin furucinta yasa Zuwaira shan mur, a zahiri kuma ta gaji da irin dirar mikiyar da aminiyar nata ke mata, bata taba zuwa gidanta sai ranar girkinta ta kuma tabbatar da zata sami Daktan a gida me take nufi? Kalli irin shigar data yi ma, har tana wani rausaya murya kasa -kasa don zata gaisheshi.... Husaina ta mike kafafunta ta kalli 'yantsun hannunta da faruttan da suka ci adon jan farce ta yaba da kanta tukunna sannan ta tabo Zuwaira "Meye matsalar naga kinyi shiru fuska a daure" Zuwaira ta kalleta a shagube "Wace irin matsala bayan kin shigo kin ganni muna zaune lakadan muna hira da mijina! Ta kura mata ido na dakika guda "Zuwaira kenan ni banga hakan ba yanayin murtuke fuskar da yayi, da kyar fa ya amsa gaisuwata, shine kike ban mamakin rabuwa dashi ki huta tunda ba kanin tsohonki ba ne." Kalamanta sun yiwa Zuwaira daci amma ta daure tace "Ba zan rabu da mijina ba Husaina tunda Ina son abina." Tayi wata 'yar shewa irin tasu ta 'yan duniya tace "Aiki ya ci sai ki kawo kudin biyan Malam." Zuwaira ta tabe baki "Ina ce sai an ga fa'idar abu ake biya?" "To a cewarki komi normal sai ki biyani." Zuwaira ta gyara zama ta kalleta daidai ta mika hannu ta dauki cup din da Daktan yasha lemo bai shanye ba shigowarta yasa ya aje cup din ya fita, ta Kai bakinta kenan Zuwaira ta kabe cup ya fadi ya fashe. A fusace ta zabura "Kan uba! Wane irin iskancine kike ji ne yau?" Zuwaira ma ta zaburo ta mike a fusace "Ha ki nan babbar 'yar iska da kike neman raina min hankali, ki rasa cup din da zaki sha lemo sai wanda mijina yasha a ciki?" "Ke din ce babbar 'yar iska har yaushe kika san darajar mijin da kike kuri dashi, yanzun me Kika san mutuncinsa?" Maimakon amsa mari Zuwaira ta shararawa Husaina..tace ki sake kirana 'yar iska kika yadda zanyi dake... Husaina ta rike kuncinta ta saki ta dunkula hannu ta sakarwa Zuwaira a ciki, ba sai dambe ya kacame ba, nan Mai aikinta ta saka ihu ta ruga sashen Rahima ta fado mata tana kuka. Rahima da Uwale suka rugo a guje, inda ta shiga tsakiyar aminan sa idanunsu ya rufe saboda masifa ba su ga zuwanta ba, wani cup din Husaina ta raruma ta wurgi Zuwaira dashi ta kauce bai sameta ba sai Rahima ya yanketa daidai saman girar ta. Jinin da suka ga yana zuba yasa suka daina masifar, Husaina ta suri Jakarta ta barta gidan a guje, Zuwaira da Uwale suka yo Kan Rahima suna mata sannu, nan take dai aka dauko first Aid kit aka wanke ciwon aka tsaida jinin kana aka rufe da plaster. Jikin Zuwaira yai sanyi sosai ta shiga cikin damuwar abinda zai faru da zaran maigidan ya dawo. Rahima ta lura tace "Don Allah ki kwantar da hankalinki tsautsayi ne Wanda ba a sa masa rana." Ta kalleta cikin jin nauyi sabida irin surutan da Husaina ta rinka barbadawa da gayya kuma tasan Rahimar da yaran gidan ma sunji (masu musu aiki) tace "Don Allah Rahima kiyi hakuri ki yafe min." Rahima ta kalleta cike da tausayi "Wallahi ban rikeki da komi ba Aunty Allah ya yafe Mana m baki daya ya tsare gaba." Suka dan zauna na 'yan mintoci kafin ta mike tace "Zamu koma can sabida ba kowa sai yara, mu kwana lafiya." Zuwaira ta amsa "Nagode a sanyaye." Ya dawo rai a bace dalilin yaje gidan Hajiyarsa ya shaida mata lalle zai rabu da Zuwaira muddin ba zata daina hulda da kawaye irinsu Husaina ba, ya taraa Hajiyar bata jin dadi dole ya kyale duk bai ce komi ba but yai deciding washegari zai kaita asibiti don ta samu proper care, ya dawo gida a fusace. Ya shige bedroom dinsa bai ga Zuwairan ba, ya gyada kai ai yasan ba zata dumfareshi ba yanzun tunda bata da gaskiya. Zuciyarsa ta rinka kuna, ya shiga yai wanka ya fito abin na cinsa a rai kiranta yayi ta waya. Kafin ta iso ya Kai ya komo cikin bedroom dinsa ita kuma tana can cikin fargabar masifar da zai mata, ashe Zuwaira ana tsoron manya, ko can wargi wuri yassamu. Ta sallama ta shiga tayi kamar ba zata zauna ba ta canza shawara ta dofane a gefen bedroom chair, yai kai ya dawo yai mata tsaye a gaba ba tareda yace uffan ba, ta rinka satar kallonsa da wutsiyar idon. ... Haseeb ya dan baya ya juya mata baya ya tambayeta "Zuwaira Ina son baki zabi wanda in kin riga kinyi an yi an gama, ba yi hakuri balle na tuba. Shin kina son zama dani ko ah ah?? Cikinta ya bada kulululu kamar mai jin zawo, cikin makyarkyatar murya tace "Me ya kawo wannan maganar Dakta?" Cikin muryar data tsani yai mata magana yace "Amsa zaki bani ko nima tambayata kike? Ta Kara kidimewa "Ah ah wace ni, yi hakuri, wallahi Ina sonka Dakta, ban taba son kowa ba sai ke, ka yafe min. .. Ba wannan amsar nake son ji ba." Ta gyara zama "Ina son zama da Kai har muddin rayuwa." Ya numfasa ya zauna yace "Ba na jin zaki sami wannan daman ta bangarena as long as za kici gaba da mu'amala da kawayen banza to zan sauwake miki aur..... Bata bari ya karisa ba ta mike zumbur tasa hannu ta rufe bakinsa tana kuka "Don darajar iyayenka karka furta, don kaunarka da Annabin rahama ka yafe min... Ta durkushe a gabansa ta dafa gwiwoyinsa tana rasgar kuka tana masa bayanin yadda suka yi da Husaina bayan fitarsa .. Jin an ambaci Rahima ya mike da sauri "What! Iskancin naku ya wuce kuyi a waje har cikin gidana har ku nemi kassara min mata ta?" "Ka saurareni don Allah laifine na riga na aikata, nayi kuskure but nayi nadamar dukkan abubuwan da na aikata tuni, inata istigfari dare da Rana, na gane illar kawancena da su Husaina na kuma janye daga gareta data lura ne ta kara shige min amma wallahi bada yawuna tazo gidana ba." Ya numfasa "Ba dole tazo gidanki ba tunda tanada manufarta Wanda a da banyi niyyar fada miki ba sai kin gane da kanki but tunda ta fiki wayau da iya siyasa ko in ce duniyan cin zauna Ina zuwa." Ta koma gefen gado ta zauna tana sharar hawaye, ya wuce Kai tsaye ya bude wardrobe dinsa ya bude wani safe da key ya ciro wata katuwar envelop ya mika mata yace "Duba contents din nan kafin inje in dubo Rahima in dawo. Ta karba gabanta na faduwa, ta rinka zaro pictures dinsu ne da Husaina wasu da abokan huldar kasuwancin nasu tana jinjina Kai, don ita ta manta ma anyi wadannan hotunan don bata basu mahimmanci ba. Da alamun kowa yai barci a sashen Rahima sai ita kadai dake zaune a falonta rike da dan karamin littafin adduar Nan *Al-Ma'asurat* tana karantawa. Ya isa gareta bayan ta amsa sallamarsa, cikin kyakkyawar kulawa yace "My dear Iam so sorry." Ta sakar masa murmushi Mai kwantar da hankali "Haba karka damu isn't all that serious." Hannunsa yasa ya taba jikinta, wuya da goshinta, ya rike tsintsiyar hannunta ya duba pulse, saida ya tabbatar temperature da vital sign normal ya saki ajiyar zuciya yace " Kiyi hakuri su Zuwaira sun saka ki cikin shiriritar su." Tace "Dakta duk misulmin kwarai yasan kaddarori da jarabawar rayuwa, fatan mu Allah yasa mu ci jarabawar." Yace "All the same sai na sa an daure wannan matar." Ta bude baki ta sauka kasa gwiwa biyu tace"Haba Dakta kana son ayita zuzuta zancen kenan, don Allah ka bar magnar a rabu da ita kawai in don ni" Yasa hannayensa ya dagota "Kin san ba laifinta gareni kenan ba?" "Kamar Yaya?" "Could you believe matar nan messages ta rinka turo min harda letters wai don Allah in aureta?" Rahima ta zaro ido "What? Kiji min maras mutunci taci amanar Aunty Zuwaira take nufi?" Ya gyada Kai "Why not tunda ita Auntyn taki bata san ciwon kanta ba?" Ta jinjina "Taf mutum sai Allah, Allah ya tsaremu da sharrin mugun mutum." "Ameen ya Azeez, gobe in Sha Allah zan Kai Hajiya asibiti mu dan binciketa tana bukatar kulawa ta musamman.". Tace "Yakamata gaskiya, Allsh ya bata lafiya yasa ba wani serious problem bane." Ya mike kana yace "Insha Allah ba matsala." Yai mata sallama ya koma wajen Zuwaira ikon Allah. 21/09/2020, 15:53 - Anty saliha: ....RAHIMA...doc by jami 50 Zuwaira ta zauna turus tana karanta takardun da wai wace ta dauka da suna aminiyar ta aikowa mijinta, ta girgiza kai cikin dimuwar ganin irin kalaman soyayya da bata zaton Husaina zata iya bayyanawa wani ba balle mijinta. Hhmmmm abin tambaya ma a nan tun yaushe Husaina ta fara karakainan turowa mijinta sakonni, tabbas wannan dalilin na daya daga cikin reasons din Haseeb na dagewa cewan ta rabu da Husaina, ita kuma saunar bata gane komi ba sai kara cusa kanta take gareta tana badadi da sirrin mijinta a duniya. Yanzun ta fara regrtting watsi da nasihohin da mijinta da iyayenta ke mata tana watsu dasu. Kaicona ni Zuwaira! Ga batun da Iyayenta keyi nan cewan idan basu isa su fada mata taji ba duniya zata yi mata hankali cikin ruwan sanyi gashi ta gani. Oh oh ya Haseeb yaji da ya fara ganin sakon wannan maras mutuncin? Hmmmm ita tasan halin mijinta ko a mafarki ba zai ji sha'awar Husaina ba, rikon addininsa da kamallarsa zasu sa Allah ya tsare fadawa sharrinta don idan ance ta kai sunansa gidan malamanta ba zata musa ba, za tayi abinda yafi hakan shu'umar banza. To ni Zuwaira mene na gani laifin Husaina, ai sai bango ya tsage kadangare ke samun wurin shiga. Me na rasa? Duk da Ubangiji yai mini muwafaqa ya azurtani da samun nagartaccen miji maimakon in gode masa ta hanyar karfafa imanina da tsarkakke zuciyata, bin dokokin Ubangina da sauke hakkokin mijina, faranta ran iyayena da kokarin zama uwa ta gari ga 'ya'yana sai nayi kunnun uwar shegu na fandare na butulcewa Mahaliccina baiwar da yai min.. Ta matso wasu zafafan hawaye yayinda take tambayar kanta shin na ma sauke hakkin iyayen nawa ma kuwa bayan su din sun sauke dukkan hakkokina gwargwado? Mahaifina yai min zabin uwa ta gari, da aka haifeni ya rada min suna Kan tsarin islama, ya kokarin ganin mun samu ilmin addini dana zamani daidai yadda zasu taimaka mana gyara zamantakewar mu na duniya da gyara lahirarmu, iyayena sun bani ingantacciyar tarbiyya kana su kayi min zabin miji nagari dana isa aure to amma ni wane sakamako na basu a rayuwata ta duniya? Shin nayi kokarin sauke hakkinsu mai girma a kaina kuwa, bayan ance Annabin Rahama ya la'anci duk Wanda ya wulakanta iyayensa, an horemu da yi musu d'a a, mu yiwa Manzon Tsira, mu kyautata musu domin wajibi ne a garemu matukar basu kauce hanyar islama ba, hatta da magana ance Kar muyi musu kalamai masu muni, sabida girman iyaye a garemu ne har aka wajabta girmama 'yanuwa da abokanansu ko kawaye kamar yadda zamu girmama su iyayen namu. Ni Zuwaira 'na shiga uku' sunan wani littafi na 'Gidan iko' . Duk inda aka tabo ni inada rauni da nakasu. Can tunaninta ya koma kan abokiyar zamanta Rahima da taki amincewa da kaddarar take wulakanta ta a idon kowa alhalin ba laifinta bane ko Haseeb bai aureta zai auri wace duk Allah ya rubuto masa. Ya jima a tsaye yana kallonta tana share hawayen da suka gaza tsayawa, tausayinta ya kamashi, ya isa inda take ya rungumota yana fadin "Ya isa haka nan Zuwaira komi ya wuce tunda kin gane kuskurenki. Ta kallesa cike da damuwa "Anya Ubangiji zai yafe min laifukana kuwa?" Ya rufe bakinta "Kasancewarsa gafurun rahimeen, Yana amsar tubarmu ko da zunubanmu sun Kai girman Uhud ne, hakika Unangijinmu mai afwa ne, yana kankare mana dukkan zunubanmu idan mun gane munyi, munyi nadama mun rokesa gafara da niyyar ba zamu sake komawa ga daukan zunubin ba. Ba shakka ya soki da rahama tunda yai gaggawar fahimtar dake har kika kaskantar da Kai Kika nemi ya yafe miki." Daman ba wai Dr Haseeb bai kaunar Uwargidansa Zuwaira bane, halinta ne ya tsana yake kyama Kuma, da Allah ya nufe ta da shiriya alhamdulillah ya rungumi abarsa. Yau kwanan Hjy Katume uku a Haseeb Medical Centre, a dalilin rashin lafiyar data taso mata mai suna *NEURASTHENIA* Wanda idan cutar ta kama kwakwalwar mutum zai rinka jinsa ko yaushe bai da isassar lafiya, kasala da rashin kuzari su addabesa, ba wata cuta ce mai tsananun gaske ba, nan da nan likitocin kwakwalwa ke ganota suka taimaka da magunguna da bada shawarar samun isashshen hutu ga maras lafiyar don shawo kan cutar. Tunda ya gano cutar dake damun Hajiyarsa kenan ta matsa ya daukota da kansa ya kawota asibitin gashi har jikinta yayi kyau ta samu sauki sosai, likitoci da sauran ma'aikatan asibitin sai ina ka saka ake da ita, kulawa ta musamman ake bata, to wani ma yai rawa ballantana dan makadi? Mahaifiyar Chief Medical Director ce fa da kanta. Tunda aka kawota Rahima ce ke zaman jinya tunda ba tada diya mace, da kyar dai Hajiyar ta amince da dawainiyar ganin alamun 'yar gidan nata na dauke da juna biyu. Kwananta na hudu kenan yau ta Kara samun sauki Amma likitan yaki sallamarta yadda ta bukata don haka Uwargida Zuwaira ma ta taho tace Lalle ita zata amshi Rahima wajen jinyar domin ta huta, jinya fa ba karamin al'amarine ba, so da yawa Mai jinyar maras lafiya kanyi ciwo na musamman saboda yanayin kulawar ko zirga-zirga da sauransu. Rahima ta dage ita zata karike don ladan take kwadayi. Suna cikin gardama sai ga Hayatu da nashi ayarin sun shigo cikin dakin da Hajiyar take, wurin ya kacame... Sai ga Ya Haseeb ya danno kai, wuri yai tsit, fuska a murtuke ya kalli Hayatu "Daman kana cikinsu kana kallonsu suka dami mutane da hayaniya?" Hayatu yai turus yace "Sarkin yawa fa ya fi sarkin karfi Ya Haseeb, duba ganni ka gani mata hudu ni kadai?" Yayi murmushi "To lauya, hayaniyar me ake?" Zuwaira tace "Wai nace Rahima ta koma gida haka nan ta huta ni zanci gaba da zama taki, ita Kuma Haulatu tace itama zaman za tayi." Ya kalli Mahaifiyarsu cikin kauna yace "Me kika ce?" Tasha mur ta mayar "Me zance kuwa, in da ka barni cikin dakina ai da kowa ya huta, yanzun sai kasan nayi " Ya sake yin murmushi yace "Shikenan na yarda da shawarar Zuwaira, kowa ta koma gida a barta ra zauna shikenan ko?" Duk suka yi tsit har Rahiman kuwa da yai tunanin ta furta wani abu bata kala ba, to wa ya isa ya daga hukuncin da babban Yaya ya zartas?" 21/09/2020, 22:59 - Anty saliha: ...ˆRAHIMA..doc by jami 51 Da kansa ya dauki Rahima suka koma gida, ta cewa Uwale bata jin cin komi a daren don haka suka yi sallama ta wuce dakinta, ta tube ta shiga wanka inda ta dade cikin ruwan dumi tana shakar lemon scent na bath salt data zuba, ta rufe idanunta tana hamma.... Haseeb ya gama nasa wankan ya kimtso ya shigo domin mika godiyar dawainiyar da take da mahaifiyarsa, ya zauna shiru bata fito daga toilet ba, ya dauki wayarsa ya scrolling ma'idanar wakewaken da yai saving, ya danna daya daga cikin wakar da yake so mai taken *What have I to do to make you love me,what have I to do to make it right?* Wace mawaka da suka lakabawa kansu suna *Blue* suka raira. Ya gyara kwanciyarsa ya l lumshe idanu yana tuhumar me yasa idan yana sauraren wakar nan ya kanji tamkar domin shi da Rahima aka rerata? Me yasa zuciyarsa taki amincewa da Rahima na so da kaunarsa yadda take ikrari,baya son yana doubting but Rahimar ce wani lokaci sai ya kasa gane kanta, sai ta saki jiki Sai Kuma ta janye sai ya rinka bi yana rarrashi, ko kuwa har yanzun bai fahimci ita din mai murdadden hali bane kamar sa? Ta kanyi taka tsan-tsan da gujewa duk abinda tasan zai jefata a damuwa. Ya sake duban agogo, ta dade fiye da kima cikin bathroom... Ya kasa daurewa ya mike yai knocking daya biyu har uku shiru ba amsa, habawa a gigice ya bude kofar ya afka cikin toilet din a tsorace... Ya saki kyakkyawar ajiyar zuciya yayinda ya ganta zaune cikin bathtub tana barci. Ya matsa ya zauna bakin bath din tare da saka hannunsa cikin ruwan wankan da har ya fara hucewa, don kar ya firgitata ya matsa daf da kunninta ya rinka Kiran "My dear....a hankali. Kamar a mafarki ta farka ta jita tsundum cikin ruwa, ta girgiza kai tana kokarin gano halinda take ciki Ya mika mata dauke da towel ta amsa ta mike tsaye ta daura yasa hannu ya daukota cak bai direta ba sai kan gado, sanyi ya fara kadata ta shiga rawar dari, yai saurin dauko riga mai kauri ya saka mata kana ya lullubeta da lallausar blanket ya koma ya zauna yana kallonta cikin takaici, sun jima ba wanda yai magana har saida ta ji ta daina jin sanyin, dumi ya ratsata ko'ina ta yaye blanket tayi mika ta dago ta kallesa tace "Thanks for rescueing me ban san lokacin da barci ya daukeni ba." "Na fahimta." Ya mayar mata a takaice. Jin irin amsarsa yasa ta yunkura ta zauna tace "Me ke faruwa naga you're worried?" Yace "Ke ya dace a yiwa wannan tambayar Ina bukatar sanin meke faruwa?". Ta amsa "Kamar me?" "Ina son sanin dalilin da yasa kike yawan barci yanzun duk inda kika zauna al'amarin ya kai Kuma har a bathtub, why?" Tace "Nima haka na tsinci kaina ciki." Ya dago cikin mamaki "Kina nufin rashin lafiyace ta sameki ban da labari?" "Kalau Nike, may be dai yawan tashin da nike cikin dare bana samun isashshen barci ne." Yace "Uhhmmm, do me a favor, Miko min hannunki." Tayi nawar mika masa don tasan da abinda yake son ganowa ya tabbatar... Ya riko hannun da kansa ya juya tafin hannunta ya kura ido ya tsaya shiru kamar mai nazari.. zuwa can ya saki ya saki ajiyar zuciya kana cikin muryar da bai taba amfani da ita wajen magana da ita ba yace "Yaushe Kika shirya fada min kina dauke da cikina Rahima?" Da ace ba kusa da ita yake ba da wuya taji abinda ya Fadi, da tajin Kuma yanayin muryar tasa duk ilahirin gashin jikinta mikewa saboda taushinta, ta kasa bashi amsa saboda kalamansa sun ratsata sosai, ua akayi ya gane tana dauke da juna biyu? Kaji wani wauta, to idan shirmenta rashin laulayi da dafewar cikinta zai hana kowa ya fahimci halinda take ciki shi ba likita bane zai iya ganewa cikin kowanne yanayi? Wace amsa zata bashi yanzun? Bata da wani kwakkwaran dalilin rashin sanar dashi illa jin nauyin a ce wai ita ke dauke da cikin Ya Haseeb, kunji wata sabuwa! Meye na jin kunya tunda an riga an zama daya anyi auren nan me ya rage illa fatar samun zuriyya dayyiba?" Shirunta ya kara tunzura shi ya mike zai bar dakin ga tunaninsa zargin da yake yi ne ya tabbata tabbas bata damu dashi ba, Rahima bata wani sn shi, because idan ba hakan ba ne why zata samu ciki almost 3months taki fada masa me take nufi? Ta lura da niyyarsa tayi saurin durowa daga gado ya juyo a fusace, nan da nan ta durkusa a gabansa "Nasan nayi laifi kayi min afwaa kayi hakuri. Ya nisa "Hhhhh inda take kamashi kenan, da zaran tayi ba daidai ransa ya baci zata gaggauta bashi hakuri sai dai wannan karon yayi fushi sosai ya kalleta rai bace "Da hakurin ta mutu nawa kika bayar? Ki zauna kiyi tunanin abinda kika yi min dinnan ya dace, idan ban San halinda kike ciki ba wa ya kamata ya sani? But tunda kina ganin hakan ne alkhairi a gareki is okay ki neme ni lokacin da kika shirya." Yana gama magana ya fice abinsa ya barta a durkushe. Ita kanta tasan ta tsokano zuciyar maza ba fus kenan. Tun daga ranar bai sake waiwayarta da batun na ita Kuma ta rasa yadda zata bullo masa, rayuwar tasu ta canza salo suka koma kamar yanayin zamansu da farkon auren. Satin Hjy Kaltume biyu cif a asibiti ta matsa ya sallameta, ya dauketa da kansa suka maishe ta gida shi da Zuwaira. Hajiyar sam bata San da wata matsala tsakanin Daktan da amaryarsa ba, babu ma wanda ya lura su kadai suke abinsu. Yau Rahima ta tashi cikin matsanancin zazzabi hade da mura, Shafa'atu ta shigo gaisheta suna hira Zuwaira ta damu ta shiga Ina ka saka da kanwar nata don tunda suka shirya haka suke kaffa-kaffa da kulawa da juna musamman idan rashin lafiya ya shigo. Kasancewar Rahimar ce da aiki Zuwaira ta shigo sashenta ta tambayeta abinda zata dafawa maigidan tunda ita tana kwance. Tace Aunty akwai time table na nau'ikan abincin da muke dafawa kowacce rana Uwale ta nuna miki ko ki dafa duk abinda kika ga ya kamata, nagode." Zuwaira tayi dariya "Godiya Kuma tsakaninmu kanwata, in dai lalura ce yau gareka ne gobe ga danuwanka balle ance ko baka iya alkhairi ba ka yiwa mai maka, ni so nawa kika shigo Kika taimaka mini? Fatanmu dai Allah yasa murar alkhairi ce." Sallamar su Maryam yasa Rahima ta dafe kai tace "Aunty ga 'yan baka nan don Allah karki maimaita batun nan a gabanta." "Yaushe Kuma ai na riga naji, Hjy Zuwaira Allah ya amsa harda nan bangaren don naga sai wani sisi kike yara sun dade da zama samari." Zuwaira tayi dariya "Marhabin sannunku da zuwa, Aunty Maryam karki ga laifinmu a nan tuhumi Dakta, may be tsufa ne ta fara aikinta." Maryam da kawarta Ummul khair suka shiga ciki Zuwaira ta bisu aka gaisa kana tace "Komin tsufansa idan ba zaku tabuka ba sai mu sake darzo masa amarya.". Rahima tayi murmushi "Yo ta taho mana wa ke tsoronta?" Ummulkhair tace "Ai tsoron ba naku bane nata ne don duk wace tace zata shigo cikinku gaskiya sunanta sorry.' Maryam tace "Tabbas zamanku na burgeni, Allah ya Kara hada kanku." Zuwaira ta amsa "Ameen Bari in shiga kicin in dawo." Ummulkhair ta rike baki "Oh ina ma ace gidanmu ya dawo irin naku? Rahima tace "Wai har yanzun babu canji a yanayin zamanku?" Ta girgiza kai "Ai Rahima yanzun ne ma gidan ke Shirin zama sansanin fada sabida ga goron amaryarmu ta hudu na kawo muku." Rahima tace "Ikon Allah! Duk kwasar karar mahaukaciyar da akeyi a gidansa bai isa ba sai ya karo wata masifar?" Shafa'atu tace "Namiji ne fa,? Ai sun fi son su tara ayita bala'i da masifa a kansu." Maryam ta gyada Kai "Wannan idan Allah bai sa kun fahimci rashin alfanun rashin zaman lafiyar ba kenan. Muddin kuka yi hakuri da juna sai ku sami salama da kwanciyar hankali.". Ummukhair ta gyara "Dace da irin wadannan kishiyoyin da zasu fahumci zaman lafiyar yafi zama Dan sarki, su fahimci arziki bai samuwa saida hakuri Abu ne mai wuyan gaske a zamanin nan da muke ciki. Idan ba a samu mai shurin shigowa ra fishsheki ta tsigeki cikin yaranki ba za a samu Mai cewa ki shigo din ki gane kurenki tunda kin auri mijinta, sai kace kowanne namiji an lika masa lambar zama da mace guda ne a goshinsa, ku dai kunyi dace da kishiyoyin." Daidai Zuwaira ta leko tace " Hmmmm all the credit goes to Rahima, tambayeta ta baki sirrin." Tana juyawa Ummul khair ta kalleta "Da gaske?" Rahima ta danyi murmushi "Fada kawai take yi, yes ba shakka mun dan fuskanci problem tsakaninmu amma hakuri, kau da Kai, dogaro da kai wajen samun sana'ar da zata hana maka bata lokacinka kan al'amurran kishi, kyautatawa juna, girmama juna, tarbiyyar yaranmu tafarkin gaskiya, sanin hakkokin junanmu da yadda zamu sauke hakkin, danne zuciya daga saurin fushi, toshe kunnuwanmu daga kunji-kunji, rashin ganin kyashi da hassadar junanmu, tsayawa a matsayin da Allah ya ajemu, kyautata ibadarmu wajen bautar Ubangijinmu da mika dukkan al'amurranmu garesa suka shafe komi, suka kawar mana da dukkan fitunu dake tasowa ya mamaye cikin gida, sai kyautatawa shi kansa uban tafiyar Wanda sirri ne don kowacce da nata salon." Ummulkhair ta jinjina tace "A gaisheku da kokari, ko a nan kinga hannu guda ba zai dauki daki ba, Ni kadai ba zan ita gyaran al'amurran gidanmu muddin ba mataimaki." Rahima tace "Wajibi wata ciki tafi hakurin da kau da Kai saboda Allah bai halicci zuciyarmu iri daya ba, haka zurfin tunani da hangen nesa ba zai zo daya ba, abunda wata zata dauka a shekara wata ko na minti gudan ba zata iya dauka ba, to ana son idan an hadaku ita mai zafi ce ke sai ki yayyafawa kanki ruwan sanyi, tayi masifarta ta gaji baki tanka ba balle ku zama daya, ba Kuma za kiyi shirun don tsoro bane, no zaki nuna mata ke tarbiyyarki ta daban ce, sai ta gaji ta bari yau da gobe don kinsan akwai ciwo mutum ya takaleka baka kulashi ba." Ta gyara zama "Kin dai San mu uku ne, Ni ce karama, dukkanmu muna da Yara, na Uwargida sune mata manya sun girma sun isa aure, amma saboda mugun tarbiyyar da uwarsu tayi musu gaisuwa ta fatar baki bai hadani dasu dai dai kuji suna wake-wake da habaici har da zage-zage wata ran wai dani suke, in hanya ta hadamu su nemi bangajeni suce idan na isa in taka su karya banza.. "Tafdijan! Inji Shafa'atu me ya hana ki lallasata ki barta kwance ba kiga wa ya tsaya musu?" "Uwarsu mana tunda ita ke turosu suyi rashin mutunci, ai na taba daukar mataki na dake su da suka kaini makura sai uwarsu tazo taci dammara tace da ita zanyi itace kishiyata ba su ba, suka taso za suyi min taron dangi suka ga ba zasu ci riba ba don ba zan dau rainin da rashin kunyar da suke yiwa ta biyun mu ba sai suka canza salon rashin mutunci,idan nayi abinci babu mai ci, yarana cikin duka da kyara kullum, babu mai daukar musu, ko ciwo suke yi babu mai lekowa yace musu sannu daga su har uwar, ita wancan ce da suke yiwa cin Kashi ta kan Dan leko. Ga sata ga keta, komi na ajiye a sace, su bata na batawa su zubar da wasu, kullum Ni kenan boyon tarkace, ko wanke tufafina dana Yara nayi wajibi gareni in girke kujera in zauna jiran su bushe in kwashe karsu sa reza su kekketa min. Da suka ga ban nuna damuwa ba sai suka zuba min gishiri ko suka zunduma min ruwa yafi karfin sanwata,,sai su aza tukunya su dora wani su ci su koshi, ko su fita su sayo wani suci su koshi." Maryam tace ",To shi maigidan yana Ina ake badakala haka cikin gidansa?. Rahima tace ga abin damuwa nan gurbata tarbiyyar diya mata, ita wace irin uwace da zata saka 'ya'yanta mata a harkar kishi? Me take koyar dasu kenan, Shi Kuma uban ya Kyaleta tana la'anta tarbiyyar yaransa?" Tace "Ya Zama mijin tace ai. Ba ya iya kwabon yayansa Sam, nida nike kokarin kwabawa sunce na cika tsanani ne, nace a tafi haka. Kwanaki yaran nan suka shirya makurcin da Saida ya sakeni, ban San hawa da sauka ya shigo Yanata masifar wai na hana yayanshi abinci Wai bai auro matar da zata hanasu abinci ba, don ma na samu suna cin girkin nawa da ban iya ba? Har da cewa zai ita rabuwa da kowacce mace kan yayansa. Ban San dalilin masifarsa ba, ashe Wai sunce masa bana dafa u Isashshen abinci ranar girkina alhalin bai mana iyaka da store ba.Ba bincike ya shiga tsiya, Ni kuma zuciya ta kawo min wuya ba bata lokaci na fara hada komatsaina nace na gaji gidan zan bari. Wai sai ita da yaran suka yo tsinke suka yi min tsaye a kofar daki suka ci gaba da rashin mutuncinsu wai ai daman sun gargadeni in bisu a sannu ko su shirya min tuggun da zan bar gidan dole, harda cewa igiyar auren kowacce matar gidan hannun uwarsu take sai sun so a zauna. To alhaki kwikwiyo a zatonsu Uban nasu yai nisan kiwo Ashe ya dawo ya shigo gidan basu sani ba yana tsaye yana jinsu, can suka ganshi da iccen faskare suka watse, yace ya saki uwar tasu saki guda, Ni Kuma yaita bani hakuri. Za kuyi zaton muna zaman lafiya da ta biyun, to kusan gara uwargidan ta fito da maitar ta a fili nasan bata kaunata, wannan sari ka noke ce macijiyar kaikayi Saida na jima a gidan na lakanceta, munafuka ce ta gaske, ita 'yar a buga nan da can ne,ta kware wajen iya kissa, ta zama bakin kalangu duk inda ta lura yafi zaki can zata buga. Lokacin da uwargidanmu ta fita nayi biris da ita tunda na lakaci halinta,sai ta ja yaran uwargidan a jiki, ta nuna musu Ni nasa a saki uwarsu da asiri. Wata rana kadangare ya shiga dakinta ta rinka kwarma ihu har saida maigidan ya fito ya shiga dakinta ya shiga aka koresa ya fita. Bayan kwana biyu sai kawai naji gulmace-gulmace na tashi wai na tura mata asiri da kadangaruwa din itama in koreta, wasu sun kama wasu suka ce sharri ne, abin ya dameni da farko daga baya nace Allah ya isar min ni da ban taba tsugunawa gaban malami da sunan neman taimakon asiri ba." Rahima tace "Ai sai ki barta da Allah ya saka miki." "Ai tuni nayi na Kuma rokesa ya tona asirin masheranta, Kar Kuma ya hore min ko sisin da zanje in cuci danuwa musulmi. Na rokesa da ya dawo da uwargidansa, yanzun da ya taho da batun auren ta hudu nace watakila idan ta taho na samu sassaucin tsangwamar da suke min. Kuma ga sakayya nan na fara gani wace zai auro diya aminiyar ita munafukan ce ce duk yawon gidan malamai tare suke zuwa, sun san sirrinta kaf. Mai 'ya'ya mata Kuma dake bugun kirji da takamar suke korar mata kishiya yarinyar da za a kawo ta dama su ta shanye a rashin ta ido, bata ganin Kan kowa da gashi kunga me zance na koma gefe Ina kallon yadda kowacce cikinta ya duri ruwa " Rahima tace "Idan ta taho ki kama girmanki karki sake ta rainaki, kiyi hakuri ki ci gaba da zama dasu da zuciya ki kama mijinki ki rike Kam,wace ta gaji da haukar ta warke kiyi huldar arziki da ita, wace taking ki shareta kici gaba da hidimominki, wace ta nuna bata kaunarki ki gujeta daga Nan har birnin sin din makiyi abin gudu ne." Shafa'atu tace "Ko Ni na dauki shawarwari nan insha Allahu." "Kema kishiyar gareki?" Maryam ke son sani.. Ta girgiza Kai ",Ba gara kishiyar da kuka hada miji daya kunsan duk shu ya ajiyeku ba a bisa tawa kishiyar sauri ce (Kishin bal-bal) "Mu dai Allah ya yaye Mana m wannan jarabar, tsakaninmu da matan kannin Dakta ladabi da biyayya muma mun rike girman mu." Maryam tace "Sa'a kuka ci Allah bai hadaku da masu shegen kyashi da hassada ba " "Kamar dai yadda matar wan mijina take. Gida daya muka zauna lokacin ina amarya,tun kafin in haihu Nike m dawainiya da yaranta har mijina na jin haushin yadda nike mata, yini guda Ina tsaye tsakar gida kamar wata tabarya, inyi hidimar girkinmu inyi hidimar shara wanke-wanke da lalurar yaranta duk a tunanin tunda nice karama, mijina ma shine karamin hidimomin sun hau kaina,ita kuwa ta kwanta ta shari barcinta. A nan na samu admission na zuwa school of nursing, karatu ba zai barni ci gaba da hidimar gida yadda na saba ba, na roketa tayi girkin rana in rinka na dare,matar nan fir taking yarda, tun a nan na gane bakin cikinta a tare dani.Ta amsa da kyar, ba ayi nisa ba ta fara korafin ta gaji da yi min wahala Ina can Ina gantali, wasa wasa muka raba girkin, sai raba mazajenmu cin abinci kwano daya, Sabiu yai bacin ransa ya hakura ga ba uwa ba uba duk sun rasu balle su tsawatar sai kanninsu Mata, yau ta bullo da wannan gobe wancan har dai na fahimci tsantsan kishina ke damunta dalili da Allah yaiwa mijina nasibi fuye da nata duk da haka yana kwatanta musu alkhairi don Yana son danuwansa amma mata ta shiga tsakiyarsu har ta kai ko ga maciji ba suyi tsakaninsu, a haka mijina ya sayi gida muka tashi yace ya yafe masa nasa rabin gadon ya hada da nashi, yanzun haka ba wanu shiri ake sosai ba saboda kawai Allah ya horewa wancan wannan bai Kai samun wancan ba, amma mace ko miji daya muka hada Ina naga lokacin fitina, kishin da ba na neman kudi ba ai ya zama shiririta. Rahima tace" Watau mu Mata problems din mu yawa ne dasu, haka kawai mace ta daukowa kanta rigimar da zata dameta ta rasa nayi, rayuwar duniya? Kan mazan yanzun ma da basu da tabbas Allah dai ganar damu yai Mana jagoranci. Zuwaira ta kare abincinta mai rai da lafiya ta zubo suka hadu suka ci banda Rahima da ta kasa cin komi tana kwance, sannan suka tafi bayan sunyi sallar la'asar. 22/09/2020, 18:19 - Anty saliha: ...RAHIMA..doc by jami 52 Bayan tafiyar bakinta ta kwanta ta dafa kanta ta karanto suratul fatiha *7 hade da ayoyin shifaa, nan da nan ta sami saukin ciwon kai da ya dameta, ta juya ta dauki remote ta canza channel din dish tana kallon labarai, nan barc ya dauketa.. Ya shigo ya ganta a haka bai tasheta ba, ya karbi remote din dake hannunta ya rage sautin tv kadan ya fita zuwa sashen Zuwaira. Ta fada mishi Rahima bata jin dadi, ya gyada Kai ya wuce dubo yara da sukayi barci, ya tofa musu addua ya dawo yai ma Zuwaira saida safe ya koma sashensa, yaci abinci kana yayi wanka ya kimtsa kana ya sake komawa sashenta. Still bata farka ba, ya zauna shiru yana nazarinta kafin ya mike ya nufi bedroom dinsa ya kwanta. Can cikin dare ta farka ta ganta bisa settee, a takaice Ya Haseeb bai dawo ba kenan, da ya shigo ba zai barta ta ci gaba da kwanciyar haka ba, can ta shaki kamshin turarensa ta bude ido sosai, this isn't her imagination lalle ya shigo ya fita abinsa tunda har yanzun fushi yake da ita. Ita ma ta kai kul saboda bata ga dalilin da zai sa ya dau batun da zafi ba bayan ta riga ta bashi hakuri ta nemi afwar laifinta. Yes tasan tayi kuskure domin komi kunyarsa da take ji ba zai hanata mishi albishir din rabon da Allah ya basu ba, Wanda idan ba Ubangiji ba wa ya isa yai wannan ikon? Ya tsaga rabon haihuwa tsakaninta da wa da kani? Fushinta na wofi ne maras tushe tunda ta riga ta amshi Haseeb a matsayin mijin da Allah yai mata zabi, ta amince wani hanin ga Allah baiwa ce meye problem dinta kuma tunda ta dade da tsunduma cikin kogin soyayya mai zurfi da fadi, ta kurbi ruwan kogin da ya kunshi dandanon zuma, gishiri da madaci, tasan dandanon zakin zuman soyayya, ta shaidi gardinta ta hadiye tsaf har da neman kari, wajen dandanon ruwan gishirin ma ta hadiye rabi ta watsar da sauran, ya rage sauran ruwan madacin data guntsa cikin baki yana kokarin shigewa cikin makoshi tana kokarin fiddo shi don ko alama wadannan ruwan ba ruwan sha ne a gareta in dai domin soyayyarta da Haseeb ne. Tayi ajiyar zuciya, so in har tana so ta amayo wadannan ruwan madaci da suka riga suka gauraye bakinta ya zama dole ta warware problem din dake tsakaninta da mijinta. Ta tashi ta nufi bedroom dinsa tayi knocking ta tura kofar a hankali. Kwance yake ringingine ya dora dukkan hannyensa ya dafe goshinsa, dim light din dake dakin bai hana ta ganin yanayin dake yake ciki ba, ta matsa ta zauna gefen da yake kwance, sanyin air condition da kamshin turaren *Emotion* da qira'ar sheikh Abdurrahman Sudais suka da yake saurare cikin suratul Rahman suka sanya mara wani irin natsuwa cikin ranta. Bai nuna alamun yaga shigowarta ba ma balle ta tanka, hhmmm tasan halin gogan nata, miskili kafi mahaukaci ban haushi but ko shi ana janyo ra'ayinsa da rarashi da dabara, idan haka dole ita ta ajiye nara miskillancin a gefe... Ta Kira Ya Haseeb can kasa so very softly.... Cikin muryar data sakar mata kasala yace "Lafiya ba kiyi barci ba har yanzun?" Ta Kara sassauta murya "Abinda ya hanaka barci shi ya hana min.". Ba tareda ya motsa ba yace "In har akwai problem dake damuna kin sani, so nagode kije ki kwanta." Tsawon minti biyar ta rasa yadda zata bullo ya saurareta abu ya faskara saboda bai yi niyya ba.. Ta mike tsam, a zatonsa ficewa zata yi... Zuciya ta kule shi ya rumtse ido, tabbas Rahima kan dole take zaune dashi... Ta matsa daf dashi ta duka ta riko hannunsa na dama ta dora bisa cikinta tace "Da ni da abinda ke ciki muna matukar bukatar kulawarka, idan ka juya mana baya yanzun zamu zama abin tausayi, kaine bargon dake lullubemu da so da kaunarka, yanzun ji nike tamkar wace aka sabule fatar jikina na zama exposed to sanyi, rana, iska da kowace irin cuta domin rashin kyakyawan kariyarka. Please do forgive me, Ya Haseeb baka san irin nauyinka da nike ji ba, kwarjini da muhibbanka na cika min ido har yasa komin rashin kunyata ba zan iya tunkararka da wani zancen Kai tsaye ba, Allah yai maka wannan baiwar, still Iam so sorry I didn't mean to hurt you." Kalamanta suka rinka ratsa shi suna shigarsa ya rinka jin wani ni'imtaccen sanyi cikin zuciyarsa da kokon ransa. Farin ciki ya taso ya shafe radadin dake kewaye da ruhinsa. Cikin hanzari ya bude idanunsa ya ganta tsugunne a gabansa, ya yunkuro ya tashi jiki na kyarma ya rungumota, suka sauke wani gwauron numfashi tare da sumbatar juna.. Ya sassauta rikonta ya lakace mata hanci yace "I have only one weakness my dear...and that weakness is you please don't take advantage of it to hurt me." Rahima ta Kara makale mijinta tace "You're my love, my life and my everything Ya Haseeb." Duk da cewan sun taba zuwa Maiduguri wannan karon tafiyar ta musamman ce domin sunan diyar aminiyarta Hjy Fatima suka tafi, sai dai kash Yayan nata yai mata na 'yan duniya,suna isa garin ya shafawa idonsa toka yaki yarda ta sauka gidan aminiyarta dai *Lake Chad Hotel* inda yai musu booking *V.I P Suit* Bayan suna da kwana da biyu suka shiga ciiin birnin na El-Kanemi. Tun zuwanta na farko Rahima ta yaba da birnin sosai musamman karamcin da 'yanuwan Hjy Fatima da mijinta Alh Ahmad Sheriff suka nuna Mata, basu manta da alkhairin Dr Haseeb da matarsa suka yo musu a Kanon Dabo ba. Daman ai shege kadai ke manta alkhairi. Kwanansu uku suka sallemesu da dimbin alkhairi, kyautar turarukan wuta da humra da lapayoyi saida ta kasa godiya. Daga can Bauchin Yakubu suka yiwa tsinke wai zai kaita ta gani abokansa da suka yi makaranta tare suka Kuma dade basu ga juna ba. Suna shiga garin, Rahima taji wani irin natsuwa ta musamman na shigarta, hakika Allah ya albarkaci jihar da wani irin kwanciyar hankali mai shigar baki irin yadda taji a ranta. Da ganin yadda jama'ar garin ke Kai kawo cikin sukuni bisa titi kasan jihar na daya daga cikin jihohin Arewa da Allah ya karesu daga hargitsi da tashin hankali. Kai tsaye gidan abokinsa dake cikin gidajen jamiar Abubakar Tafawa Balewa suka wuce inda suka sami kyakkyawar tarbo daga iyalin shahin malamin. Nan aka barta da muhawara da zuciyarta kan cewan tsakanin mutanen Bornu da Bauchi su wa suka fi karrama bako? Gaba dayansu suka fita gari din ba ido abincinsa, cikin University suka fara shiga, suka nufi fadar Mai martaba Sarkin Bauchi Allah yaja zamaninsa, daga can sai Yankari Reserved, Zaranda Hotel nan ma zasu gaisa da abokinsa, matarsa da Rahima suka wuce kasuwar Wunti domin sayayyar tsaraba Tsarin garin ya burgeta, ta rinka kwatanta wajen yawon bude na Kyarimi park dake Maiduguri da Yankari Game Reserved, duka jihohi biyun sun bata sha'awa, wajen alkhairinsu kuwa tsakaninta da jama'ar garuruwan sai adduar da fatan Allah yai musu sakayya, ta Kuma gode da kauna. 22/09/2020, 22:36 - Anty saliha: ..RAHIMA..doc by jami 53 Kwanci tashi cikin Rahima ya isa haihuwa, Ubangiji ya kawo nakuda da haihuwar cikin sauki saboda tsananta adduoi da suke tayi, ta haihu a gida tareda taimakon kawarta nurse Shafa'atu da Auntyn ta Zuwaira, ta haifo diyarta mace sak kamanin Dakta. Murna da farin cikin 'yanuwa da abokan arziki bai faduwa, Uban kuwa dawowa gida kawai yayi ya tadda mai jego da diyarta, yayi kamar zai lashe su, gashi Allah ya jarabce shi da son diya mata. Ba tantama Hajiyarsa aka yiwa namesake "Ummulkurthum. Ana sauran kwanaki kadan su cika arba'in aka wayi gari babu Alh. Muhammad mahaifin Zuwaira. Wannan babban rashi ya girgiza Haseeb fiye da kowa, Zuwaira taci kuka har ta gode Allah, ta rame ta fige tayi baki duk ta lalace, mijinta da 'yaruwar zamanta suka rinka bata magans tareda nasihohi har ta dangana taci gaba da yiwa Allah godiya da ya nufeta da shiriya ta rokesa gafara ya yafe mata kullum yana sanya mata albarka kafin Allah ya amshi rayuwarsa. Gaba dayansu suka nufi aikin Hajj da shekara ta zagayo, inda Rahima ta sauke farali, Haseeb da Zuwaira kuwa sun taba zuwa. Tana yaye Muhibba ta nemi iznin komawa B.U.K yin masters, ya amince saboda sanin muhimmancin ilmi bai tauye ta ba taci gaba da karatu. Tana cikin shekara ta biyu a makarantar ta sake haihuwar mai sunan Ummanta Habibatu suna kiranta Ummi. An haifeta ba jimawa Zuwaira ta samu nata rabon itama ta haifi Ummul Salama. Allah mai jin rokon bayinsa kenan, Haseeb ya roka an amsa, ya bashi 'yan mata uku reras sai fatar Allah ya raya masa ya shiryasu hanya madaidaiciya. Tunda Zuwaira ta daina fita fita zuwa Dubai da Saudiyya yawon saro kaya suka sake hada gwiwa da suna ba Hayatu yana dauko musu kayayyakin da ake bukata tunda shima ya zama business man, sosai suke samun nasibi baya ga business dinsu da Maryam Kuma, sun Kara da saro designers perfumes, shoes and bags latest designs. Rahima ta biyawa Umma da Baffa kujerar Hajj, ranar Umma Saida ta zuba ruwa a kasa tasha domin murna tare da godiyar Allah da ya rayasu ya shirya musu zuriyyar ya daukaka su har an fara dawainiyya dasu da wasu ma duk ana cin gajiyarsu. Ka'idane duk shekara Haseeb na fitar da zakka ya rabawa marasu galihu, ya kuma biyawa wadanda Allah ya tsaga rabonsu zuwa sauke farali ko Umrah, wannan karon kuri'ar kan Lauratu goggon Rahima, Malaminsa Mal. Nuhu da amintaccen maigadinsa Mal Hassan ta fada.. Rahima tace itama zata biyawa Uwale da fatar Allah ya kai ladar kabarin mahaifiyarta da Rabi'u Duk karshen wata suke haduwa family ana sauke qur'ani a gidan Daktan, in an kare ayi adduoi ga dukkan mamata da masu rayuwar, iyaye, 'ya'ya, 'yanuwa da abokan arziki, jiharsu da kasarsu baki daya. Duk ranar jumma'a za a dafa abinci a rinka rabawa mabukata sadaka duk don neman yardar Ubangiji da neman karin yalwarsa cikin dukkan al'amurran ratuwarsu. Aikin Dr Haseeb sai dada bunkasa yake, sunansa na dada yaduwa yayinda yaci gaba da bude rassuna jiha-jiha Yana samo kwararrun likitoci Yana zubawa Gwamnatin tarayya ta yaba da kwazonea kwarai suka bashi mukamin *Minister for health* Yace bai so hidimomi sunyi masa yawa... Mata da 'yanuwa suka yi masa ca! Bai amince ba saida Hajiyarsa tasa baki tace "Ya Allah zai maka daukaka ka butulce? Hidimomi ba Allah ke taimakonka tafiyar da komi ba ko da karfinka kake?" Ya amsa da zuciya guda ya fara aiki. Kamar ba za a sake haihuwa gidan ministan ba domin Saida Ummi ta shekara uku aka samar mata kani, wannan karon sai ga kyakkyawar yaro, ga tsawo ga kiba, babansa zahiri.. Ranar suna Saida kowa yai kwalla da yaji sunansa *Rabiu* Nauyi kam ya karu kan Daktan, ga na iyalinsa, ga na Mahaifiyarsa, 'yanuwa dana yanuwan Zuwaira ga na jama'an Annabi da suke cin arzikinsa banda na aikinsa, ya zama bai da lokacin kansa. A ka zo batun komawa Abuja Zuwaira tace sai dai Rahima ta tafi domin ta sakankance ita dince ce *star* din Haseeb, ta kuma hakura da haka duk da cewa ba nuna banbanci yake tsakaninsu a zahiri ba, Rahimar taki yarda da shawarar Aunyn ta domin tsakaninta da ita girmamawa ce. Da kansa takobin dagan ya raba gardama cewan kowacce zata rinka zuwa wata uku ta dawo dayan ta tafi Kuma, wace lokacin hutu ya shigo cikin turn dinta ta tafi da yara. Zuwaira ta sake samun 'yar bebinta 'yar caraf kyakkyawa, da ganinta tace wannan ai Rahima ce,kamar yana jiran ta furta, ministan ya rada mata suna *Rahima* suna kiranta Amira. Zuwaira na murna ita kuwa wace akayi dominta ta korafin me yasa ba a fara sanya sunan Zuwaira ba? Ya kalleta yace "Banyi gwaninta ba kenan?" Ta amsa "Wallahi kayi sosai na kuma ji dadi nagode amma kayi min alkawarin idan muddin na haifi mace Zuwaira ce." Yace "Allah ya kawo cikin, shin ko har an samu?" To Allah yayi an haihun amma namiji aka samu sai yaya kenan? Ya rada masa suna Habibullah. Shekaru sun mika kwarai, tuni Dr Abdul Haseeb Junaid ya ajiye aikin gwamnati bayan shekaru takkwas yana bautawa kasarsa a matsayin ministan lafiya. 'Ya'yansu maza sun kare univertsity. Junaid (Khalifa) Engineer ne, Mohammad(Abba) Architect, Abdul Haseeb karami ya bi sahun babansa ya zama likitan kwakwalwa, yana kasar Bulgeria karo ilmi. 'Yan matan Kuma Muhibba ta dage saita zama irin Dr Kausar ta cikin littafin Anti Saliha Zumuncin Zamani, ita din Gynaecologist ce, Ummul Salama Lawyer ce don ita Bartister Tahir ne gwaninta(Son Zuciya) Ummi Habiba sha'awar Boutique din Sufab ya tunzuro ta da yadda ita kanta Surayuar ke tafiyar da business dinta da son taimakon iyayenta yasa ta karanta Business Administration yayinda Amira Rahima ke son zama cikakkiyar malamar makatanta mai zaman kanta irin na Sa'adatun Sagir haka dan autan gidan Daktan yace shi malamin lissafi zai zama, so Habibullah mathematician ne. Wata rana Daktan ta tara manyan 'ya'yansa lokacin Abdul karami ya kare karatunsa yace lokaci yayi da kowannansu zai fitar da abokiyar rayuwarsa. Ba bata lokaci Junaid ya nuna Walida diyar Maryam yake so wace ke zuwa hutu wajen Innarta Rahima, Muhammad yace Nabila diyar Uncle Hayatu. Wadannan 'yan Mata duk karatu suke a B.U.K. ne, Walida na karanta Mass Communications tunda a rayuwarta Laila Tahir Mutallib ce role model dinta, Nabils na karanta Economics. Idan ta bi daga-daga na kurya kan Sha Kashi, Abdul Haseeb junior yayi shiru bai ce komi ba, to shima miskilin ne irin uwarsa da wan uban, to Barewa tayi gudu ne danta yai rarrafe? Baban nasa yaxe ya rubuto sunan wace yake so tunda ba zai furta ba, ya rubuta ya ajiye, yana fita ya dauki takardar ya warware, abinda ya gani yai matukar faranta ransa, ba domin namiji yake ba da yai guda Amma yayi abinda yafi dacewa yayi a irin yanayin, ya daga hannuwansa sama yace "Tsarki ya tabbata gareka ya Allah Ubangijin Al'Arshi mai girma!!! Ya sake duban takardar da Abdul ya rubuta *Daddy Rahima Amira ce mata ta Insha Allahu* Ya juya takardar yana mamakin ko ya aka yi yaran suka yi tunanin hada auren zumunci gaba dayansu oho? 23/09/2020, 12:31 - Anty saliha: ...RAHIMA...doc by jami 54 Iyaye, 'yanuwa da kakanni kama da abokan arziki da sauran jama'ar da suka ji labarin hada wadannan igiyoyin aure sai sha'awa da murna suke. Kasa-kasa ba inda Daktan bai aika da katin gayyata ba, duk wasu masu hulda da asibitocinsa, abokai da tawagar shugaban kasa da kusoshin gwamnatocin jihohin Arewa sun halarci wannan gayarumin dauren aurarraki. Da yake al'amarun tuwona Mai na ne shi kansa Daktan ya rasa inda zai fi maida hankali a sha'anin, to kusan shine uban angwaye da amaren baki daya, haka ya wakilta kanninsa da abokan arziki aka taru aka yi komi cikin tsari gwanin sha'awa. A wajen bukin ne su Ummul Salama suka hadu da masoyansu ita ta hadu da abokin Khalifa, Muhibba dan abokin babanta balarabe nan na Riyadh ke sonta, har sun amincewa juna, sai adduar Allah ya nunawa iyaye lokacin nasu bukin. Bayan an gama shagalin da wata guda, kura ta lafa, Zuwaira ce da Rahima ke zaune a main parlour suna hira, sai kallon Rahimar take cike da sha'awa tana yaba yadda take tafiyar da al'amurran rayuwarta ta yau da kullum, me zata ce da wannan baiwar Allah? Gaskiya sai godiya da adduar Allah ya saka mata da khairan domin a dalilinta ita kanta da 'ya'yanta sun samu nagartacciyar rayuwa, ta sami kan maigidanta yanzun girmamata yake sabanin da can inda aka fito..... Karar waya ta dawo da ita daga duniyar tunani, tayi firgigit daidai Rahima ta dauka ta sallama, can taji ta rafka salati ta kalli Zuwaira, ita Kuma a firgice tace "Me ya faru wa Kuma muka rasa?" Rahima tace "Allah yaiwa Husaina rasuwa sanadiyyar accident.....Zuwaira tayi kasake tsoron Allah ya Kara kamata, duniyar kenan mai halin dan mangwaro, sai ta bari ka saki jiki kana tsotso kana jin zakinta ta subuce maka. Ita yaushe rabonta da ita tun ranar da ta taho gidanta shekarun baya suka rabu baran-baran amma tana da labarin sheke ayar da take abinta har Allah ya amshi ran ta. Ta nisa oh Allsh na gode maka da ka taro Ni ka dawo dani Kan hanya madaidaiciya, tun lokacin tuba bai kure mata ba. Basu Kara firguta da al'amarin Ubangiji ba Saida suka ji labarin ya baza gari cewa kasa taking amsar gawar Husaina, duk inda aka tona ko a ga maciji ko kunamu har jamaa suka gaji da watangaririya da gawarta, bata samu hutun da gawar mutum ke matukar bukata ba sai dare da malamai suka taru suka rinka adduar neman gafara da rahamar Ubangiji. Ya Allah ka shiryemu, ka shirya gaba da bayanmu dama da hauni, kasa mu fi karfin zuciyarmu kar ka kawata mana kyalkyalin duniya, abinda ya faru da Husaina ya zama izna/ishara ga yawancin matan zamani da suka maida aure abin wulakantawa, Allah ya yafe mana dimbin zunubanmu. Wata rana Rahima na kishingide bisa doguwar kujera cikin shiryayyu falon sabon gidan da suka koma, maigida ya Kira wayarya cewan yana son ganinta. Ta mike da hanzari ta gyara rigar da ta saka ta wata bugaggiyar shadda coffee and orange colour, anyi mata dinkin boubou da aka gewaye da cord lace gwanin sha'awa, kayan da launin kayan sun amshi jikinta sosai, ta fito dagwas-dagwas take takawa zuwa falonsa, ta sallama ya amsa ta shiga ta zauna. Tunda ta bullo ya kura mata ido har ta iso ta zauna kusa dashi bai dai na kallonta ba, hakika kwalliyar ta burge wansa aka yita dominsa ko da bai furta ba ta fahimci cikin kwarar idanunsa,ta matsa kusa kamshin man shafarwata (avon) *soft musk* suka daki hancinsa, ya rumtse ido ya bude, tayi kasa da nata idanun saboda kunya tace"Gani, Daktan yana bukatar wani abu ne?" Ya amsa "Uhhmm uhhmm. Kuma yaci gaba da kallonta dai. Nan take ta urunce ta fara kaduwa, zuciyarta ta fara harbawa tasa hannu ta danne saitin wajen, cikin makyarkyatar murya tace "Dakta your gaze is so intense, it makes me nervous, don Allah me kake so?" Kafin ya bata amsarsa ya rungumota cikin sarkakkiyar murya yace "What I want in my life is your love forever, can you give me that much?" Ta kwantar da kanta a kirjinsa tace *Na dade da mika maka zuciyata cikin so da kaunarka ba don komi ba sai domin ka sanya min nishadi cikin rayuwata tunda ka amince na zama daya bangaren jikinka, ka fahimci bukata ta, ka zama babban aminina, Ya Haseeb na sadaukar da kaina da soyayyata gareka da fatar zamu kasance a haka har abada." Dakta Haseeb yai murmushinsa mai Kara sakata cikin shaukin kaunarsa yace "Na gode sosai my dear. Nayi murna da farin cikin jin kalamanki, Ina Kara godewa Allah SWT da Kara salati ga Manzon Tsira wanda ya luras damu sai abu hudu sun hadu sannan mutum ke da azikin rayuwar duniya. Na farko mace Saliha ta gari, na biyu makwabci nagartacce, na uku abin hawa lafiyayye sai ma hudu gida mai fadi. Kinga duk Ubangiji sarkin sarauta ya hore min dukkan wadannan, fatana yanzun Allah tasa mu gama da sauran tsoffinmu lafiya, ya bamu ikon ci gaba da sauke hakkokinsu dana iyalina, sannan yai mana kyakkyawar cikawa idan lokacinmu yayi. Rahima ta amsa "Ameen ya Zuljalali wal ikram, Dakta." Wadannan dattjai biyu sunci gaba da tafiyar da rayuwarsu cikin so da kaunar juna duk da sun fara manyanta an kai ga fara ajiye jikoki, kullum soyayyarsu Kara tofo take tamkar ana mata ban ruwa daman ance *so* bai tsufa sai dai masoya su tsufa. A ko yaushe Rahima ta Kan zauna ta rinka kwatanta Haseeb da taurarin littafin Anti Saliha. A miskillancin sa za su zo daya da Faruk, a tsabar kwarjininsa sai dai ta hadashi da Abdul Nasir, wajen sadaukar da Kai wajen aikinsa shi da Tahir suna mata kama, to wajen son zumunci da kaunar 'yanuwansa fa dole ta hada shi da Sagir. A fagen matan kuwa ta rasa wacce zata kwatanta kanta da it's saboda tun daga Surayyar, Kausar, Laila da Sa'adatun kowaccensu sarauniyya ce Kuma tauraruwar dake haska zuciyar masoyinta don haka data hada ta tace ta tankade ta rairaye bata samu abun zubarwa ba daga mazan har matan domin kowanne naji da abokin rayuwarsa tamkar yadda suke ji da rayukansu. Sai dai duk a je a komo abubuwan da take ganin sune jigon rayuwar wadannan ma'aurata in ka debe tsantsar so da kaunar juna sune aminci, hakuri, yarda, mutunci, kyautatawa da barin wa Wanda ya hadasu dukkan al'amurransu, baya ga sanya shi a gaba da bayansu tare da yin kyawawan adduoi da kaurara godiyarsu gareshi gwani sarkin Sarakuna. Har yanzun a iya tunaninta ta rasa shin idan ta kwatanta rayuwar aurenta da nasu, ita dun wace lamba za a bata? Da yake bai dace ta baiwa kanta amsa ba gudun son kai, ta hakura ta barwa jama'a suyi mata alkalancin. *SUBHANALLAH WALHAMDULILLAH WA LA ILAHA ILLALAH WAL LAHU AKBAR WA LAHAULA WALA QUWWATA ILLA BILLAHIL ALIYIL AZEEM.*